Zuwa can anjima tafara tashi daga jikin khalifa yayinda ta kwace hannunta daga hannun sameer idonta arufe
Salati tafara tana kiran sunan ALLAH kanta ne taji yana jujjuya mata da sauri tariqe kan hannun bibbiyu
Memorynta ne yafara dawowa ahnkl tafara tuno rayuwarta na baya da kashe mata iyaye da baba dauda yayi da gudunsu ajeji ita da yaya khalifa da rayuwar da sukayi ajejin har izuwa rabuwarsuDA rayuwarta tare dasu sameer na mantawa da komai datayi har izuwa yau dataji sunan khalifa da 4eyes's din da sukayi
Da sauri ta bude ido tana waige waige tagansa kusa da ita kuka mai tsuma zuciya ta saki gamida daga hannayenta biyu wanda suke rawa kamar mazari tana shafan fuskarsa. Domin ta tabbatar shidin ne ko kuma gizo ne
Shima hawaye yakeyi
Cikin muryan kuka tana shafa fuskarsa tace ya..yay...yaya...kha...khali.....khalif....khalifa...
Daga mata kai yayi alamun eh my safreena nine ya riqo hannunta
DA sauri ta rungume sa tana kuka tana mgn dan Allah yaya khalifa karka sake tafiya kabarni zuciyata bazata ɗauka ba
Hannu biyu yasa shima ya rungumeta yana hawayen farin cikin sake ganin safreena arayuwarsa
Haqiqa adduar bawa bata fadi ƙasa banza saidai jinkiri gashi Allah ya amsa du'a'insa yasake hadasa da safreenaDuk gabaki daya sun Zama abin kallo
Jama'ar dake wajan kansu ya ɗaure sun kasa fahimtar komai
Amma banda mutum uku
Ahmad
Nabeel
SaeedMami ce tace waini balaraba meke faruwa ne kam kun samu aduhu fa kuyi mana bayani mana yanda zamu fahimta kufitar damu a ruɗani
Nabeel ya bude baki zai magana bai ankara ba sameer ya fizgi safreena daga jikin khalifa ya rufesa da duka kamar Allah ya aikosa
Kokarin shiga tsakani akayi amma ina sameer idonsa ya rufe da kishi. ganin tabbas fa zai iya rasa najma idan baiyi da gske ba Duka kawai yake kaiwa ta ko ina wa khalifa
Safreena tashiga tsakaninsu tana hana sameer wanda idonsa ke rufe bisa tsautsayi ya kai mata duka tasaki ƙara zata fadi ihsan da madina suka tarota
Ahmad nabeel saeed kokarin riqe sameer sukeyi amma yana zillewa
Sameer baiyi auni ba yaji sauƙan maruka hudu a fuskarsa da sauri yadafe kuncinsa sbd marin ya shigesa nan da nan ya samu natsuwarsa sakamakon tozali da idon mahaifinsa da yayi ranshi abace
Ganin fadan nasu bana ƙare bane yasa mami ta kira dad tace mishi kazo gidan biki ya zama gidan fada ga sameer na dambe shine ran dad yabaci suka taho dukkansu shida dadyn nabeel da dadyn saeed
Dad yana huci cikin muryan tsawa yace sameer kalan tarbiyyan dana baka kenn ? Irin ilmin dana baka kenn? Ina hnklnka yake ? Ina natsuwar taka take ? Wannan shine abinda zaka sakamin dashi kenn?
Dadyn saeed ne ya dafasa yace alh ya isa haka yanxu dai ba asi yakamata muji dalilin wannan fadan
Caraf madina tace dadyna wlh duk ya khalifa ne yajawo domin da baizo ba da yanzu muna can muna gudanar da shagalinmu cikin kwanciyar hankali
Kwace yakeso yayiwa yaya sameer najma wai yake kira da safreena
Nabeel yace madina ki rufawa mutane baki bakisan komai ba
Cikin tsiwa tace au yaya nabeel kaima bayansa kake bi kenn lallai kam ansamu waje sosae
To kai din waye khalifa ?Tsawa nabeel yamata yace banace ki rufe bakinki ba
Lallai khalifa kasamu waje dama kam ance duk wanda yasamu waje saiyayi shanyarsa kuma wlh.....
Hannu safreena ta dagawa madina gamida cewa
Ya isheki haka madina
Shin kinsan waye YAYA KHALIFA kinsan wacece ni
![](https://img.wattpad.com/cover/240250469-288-k538873.jpg)
YOU ARE READING
GUDU A JEJI
Short StoryGUDU A JEJI, LABARI NE MAI CIKE DA TAUSAYI, CIN AMANA, HASSADA, KYASHI DA SON ZUCIYA, KARKU BARI A BAKU LABARI, KU HANZARTA KARANTAWA DAN KU JI ME LABARIN GUDU A JEJI YA KUNSA, KU DAGA JI KUNSAN AKWAI CAKWAKIYA, KU DANNA MIN VOTE KU YI FOLLOWING DIN...
31-32
Start from the beginning