Zaunawa ta koma tayi tace yanzu kam ma  ba kauye ba jeji ma nake dry khalifa ya hau mata SBD yanda ta karashe mgnr ne yabasa dry
Kallonsa safreena takeyi tace nidai idan kana dry kyau kake karawa yaya khalifa

Kallonta yayi batare da yayi magana ba itama tashi tayi tashiga bukkan nan ta hau karkadewa ganye ta yanko ta hau share bukkan shi kuma khalifa yana aikin gasa kifi

************
Ba karamin tashin hankali black snake yashiga ba sakamakon rashin dawowar mutanensa SBD Wanda yake jidasu ya tura

Waya yadaga ya kira dauda yace wai bangane ba na tura mutane na amma  basu ba labarinsu ko lafiya ?

Dauda cikin tunxuran zuciya yace nima ai shurun naji

Black snake yace wlh idan wani Abu yasami yarana saina kasheka dauda kai da Dan iskan yaron nan
Yana gama fadin haka ya kashe wayar

Dauda shawara ya yanke shida kansa zaije jejin nan domin ya koyawa khalifa hankali lallai khalifa yayi wasa dashi baisan hatsabibancin sa bane amma yanzu zai gane yaja da Wanda suka fisa ma balle shi yaro karamin alhaki

********

Cin kifin nan sukayi sosae suka koshi suka kora da ruwa
Duk da ba gishiri balle ayi tunanin maggi ko oil burinsu kawai su koshi

Har dare bayan sun idar da sallah isha suna zaune awajan bukka ga wuta naci Wanda khalifa ya kunna musu da kirare

Shuru sukayi kafin safreena ta katse Shurun da cewa yaya khalifa kataba soyayya ?

Tambayarta ta yajita daga sama Dan haka yace meyasa kika min wannan tmbyar ?

Sosa keya tayi tana jujjuya idanuwanta Wanda suka kara mata kyau tace kawai tmbyarce tazomin kabani amsa

Yace eh na taba lkcn ina....bai karasa ba yaji safreena ta buga wata uban tsaki Wanda hakan ba karamin mamaki yabawa khalifa ba yace safreena lpy kuwa wannan tsaki haka?

Cikin fushi tace to ni ina ruwana

Yace ina ruwanki dame  safreena?

Tace da tmbyarka danayi ko ka taba soyayya ta karashe mgnr tana murguda masa baki murmushi yayi yace to ai baki tsaya kin karasa jin lbrn ba kika katseni itafa yarinyan ma tayi aurenta babanta ne yace bazai aureta ba shine yabayar da ita ma wani dan Dan' uwansa

Dry tayi tace lallai fa ya kyauta kam dama zatayi karanbanin auren mijin da banata ba

Tashi tayi tashige bukkan khalifa ya bita da kallo yakasa fahimtar mgnr ta

Can ta leko taga ya kwanta awaje tace yaya khalifa kashigo mana tashi yayi yana mata kallon amma bakida hankali

Yace inadin zan shigo safreena?

Hankalinta kwance batare da tunanin komai ba tace ciki mana

Murmushi yayi yace lallai safreena har yanzu akwai yarinta na yawo asaman kanki

Mu kwanta adaki daya ke bakisan duk inda mace da namiji suka hadu waje daya su biyu cikon na ukunsu shaidan ne
Yakamata muguji sharrin shaidan da sharrin zuciya

Ke amana CE agareni inaso na sauke wannan amanar kullum adduata Allah ya fitar damu cikin wannan jejin sannan na maka dauda a kotu ayi masa hukunci daidai da abinda ya aikata

Tunda khalifa yafara mgna ta natsu tana sauraronsa yana dasa aya tace haka amma kuma ai Allah yaga zuciyarmu bamu da wata mummunar nufi

Murmushi ya kumayi yace har yanzu dai baki ganewa safreena ita zuciya batada qashi sai tsoka
Kitashi ki shiga ki kwanta

Kin tashi tayi tace nikam bazan iya bacci na barka anan kai daya ba saidai mu kwana anan

Khalifa bai kara mata magana ba tashi tayi tashiga ta dauko maganin da maharbin nan yabata tazo ta zauna kusa dashi hannunsa ta kama ta hau barbada masa maganin sai binta da ido yakeyi tana gamawa yayi murmushi yace ngd
Hade rai tayi ta tashi ta ajiye maganin tadawo

Dry yayi yace to shi kuma wannan fushin na miyene da yazo yanzu kefa kincika rigima

Nan ma bata kulasa ba shima kyaleta yayi ya cigaba da hidimarsa

Da

Washe gari dauda

Ya shirya helicopter da wasu majiya karfi da garada zasuje jeji

Sai mun hadu a next page

Comments

And

Share

By momyn ahlan✍🏻✍🏻

GUDU A JEJIWhere stories live. Discover now