chapter 1: MAFARI

65 1 0
                                        

*MADUBI...🪞 *
"The persona effect: A story of hidden identities and betrayal"
*©Salma Ahmad Isah🦋*

*SADAUKARWA*
Wannan littafin sadaukarwa ne zuwa ga Rabi'atu Abubakar (Pinky) A small token of appreciation filled with love from your Lilly, thanks for your support and prayers
~Gaisuwa~
Gaisuwa ta musamman zuwa ga Khadeeja Abubakar Alkali (Khadeeja Candy) a.k.a Oum Namra, Zainab A Baba (Abokiyar Hira), Fatima Ahmad Isah, Amina I. Ibrahim (Nanameera), Jamila Umar (Janafty). Allah ya bar tare.

^°^SHIMFIƊA^°^
Koren maciji ne a ƙarƙashin koriyar ciyawa. Hauwasa suka ce mugu ɗan masara, ana goyonka kana gemu. An ce da ɗan gari akan ci gari! Shin kun yarda da hakan? Idan ka kalli fuskarka a saman ruwan kogin dake gudana, za ka ji tamkar kana kallon MADUBI ne, domin shi MUDUBI kan bayyanar da zahirin abin da ido ka iya gani... Tunanin nazarin suffarka a saman ruwan zai sa ka ɗauka cewa kai ne da kanka a kan ruwan. Kuma hakan ba shi ke nuna cewa babu wasu abubuwa ɓoyayyu a ƙasan ruwan ba. MADUBI na nuna mana zahirin abin da muka yarda da shi ne, zuciya ita ce ma'ajin sirrin kowani bawa. A nan aka samu tangarɗa! Domin kuwa a duniya babu MADUBIn da zai iya haska zuciyar wani bawa. Da ace za a samu, da sharrika da dama ba su wanzu ba, da ace za a samu, da kullika da yawa sun warware, domin MADUBI ba ya ƙarya, ɗan Adam kaɗai ke yaudarar kansa idan ya so. Ta wani wurin abu guda ɗaya ne ya haɗa su, wato kaddarar mahaifi! A wani ɓangaren kuma abubuwa da dama sun bambantasu, duk da maƙasudin kasancewarsu a halin da suke ciki abu ɗaya ne, hakan ba shike nuna cewa idan suka tsaya suka kalli juna a MADUBI ta ko wani gefe kammaninsu za su zamto ɗaya ba. Rikicin cikin gida, wani babban gida da ya ɓoye tarin sirrika masu ban tsoro, waɗan da idan aka bayyanasu ga mai karatu dole ya jijjiga. Murmushin mutanen dake kewayensa shi ne makaminsu. Mahaifinsu ya tarwatsa rayuwarsu da hannayensa, son zuciya da son kai su ne ke kai mutum ga halaka. Ƙawar dake duniya ita ke ruɗar mutane da dama, sukan yarda da abin da idanuwansu ke gani, ba tare da sanin cewa komai da suke gani gaibu ba ne, duk abin da ka samu, wata rana dole ya ƙare. Abu ɗaya ne da ba zai taɓa sauyawa ba, cewa MADUBI ba ya ƙarya...

Page | 1
•°{MAFARI}°•
Haihuwa ita ce silar zuwan ko wani bawa duniya, mutuwa ita ce ƙarshen duk wani abu mai rai... Dalilin mafarin labarin ko wani bawa tana da banbanci da ta saura. Shin! Kun taɓa tambayar kanku ta ina? Yaushe? Tayaya? A wani lokaci labarinku ya fara? Garesu wannan ce amsa, ranar da ƙaddarar naiman magani ta kai kakkaninsu ga yanke hukuncin da sai sun yi nadama a nan gaba...

*Ƙauyen Tulo-Tulo, Yusfari Local government, Yobe state.
*Shekara ta 1989...*

Tun daga saman tilin saharar dake ƙarshen shiga ƙauyen na tulo-tulo, za ka hangi tarin dandazon jama'a a kofar wani babban gida ginin kasa. Kallo daya za ka yi wa tarin jama'ar ka musu kudin goro ka basu sunan masu naiman magani. Ba wai majinyata ne kadai a wurin ba, har da 'yan uwan majinyatan da kowanne a cikinsu ya zo da fatan samun maganin cutar dake damun majinyatansu.

Malam Usman da matarsa Iya Saude, na daya daga cikin tarin mutanen da suka yi wani dogon layi a kofar gidan, wanda idan ka gan shi ba ka ce zai kare nan da gobe ba. Kamar dai sauran jama'ar dake wurin, idanuwansu bude suke kan mutanen da suke fitowa daga gidan ƙasar bayan an sallamesu. Fuska ɗauke da murmushin nasara, domin ko abin da aka zo naima an dace.
Hakan shi ke karawa zukatansu fatan cewa lallai su ma zasu dace, kamar yanda yake ne a kan ko wani majinyaci, duk wurin maganin da zai je gani yake kamar a nan warakar take. Babbar 'yarsu cikin 'ya'yansu mata biyu da Allah ya azurtasu da su dake rike a hannun Iya Saude ce ta yi luuu zata fadi, lamarin da ya ja hankalinta zuwa kan 'yar tasu mai suna Zainab, wadda akewa laƙabi da Jebu. Da sauri ta tarota tare da gyara mata zaman hijabin dake jikinta, kasancewar su ne a layi.
"Me ya faru?"
Malam Usman ya tambaya ganin yanda Iya ke ta kokawa da Jebu.
"Ina ga abin ne ya motsa"
Ta fadi cikin halin damuwa. Malam Usman ya mika hannu ya tallafa mata suka gyara mata tsayuwa suna ta jera mata sannu, duk kuwa da sun san cewa ba a cikin hayyacinta take ba. Yau a ƙalla an kwashe sama da shekara uku ke nan tana kwance tana jinya, irin jinyar dake fitar da mutun a hayyacinsa, ba ta san wanda ke kanta ba, ba ta iya magana, sai dai a kwantar sai dai a tayar.
Magani kuwa babu kalar wanda ba su gwada ba, kuma har kawo yau ba su zauna ba, a na haka suka samu labarin Bogaji Sarkin Mayu. Wanda yake zaune a ƙauyen Tulo-Tulo. Irin labarin da suka samu a kansa na cewar idan an je gare shi ana dacewa yasa ba su yi sanya ba wurin yin takakkiya tun daga garin Kanon Dabo zuwa ƙauyen na Tulo-tulo, zuciyoyinsu cike da fatan dacewa a wannan wuri.
"Na gaba ya shiga!"
Garjejen gardin dake bakin kofar shiga gidan ya faɗi yana duban Malam Usman, wanda ya saki baki yana kallon matar da ta fito tana takawa kan kafafunta ras, sabanin lokacin da ta shiga tana jan kafartata. Cikin hanzari ya tallafawa Iya suka shiga da 'yar tasu, a babban soron dake farkon kofar shiga suka iske wani farin tsoho, zaune kan tabarma, gefe, da dama da hauninsa dika tarkace ne na kayan magunguna. Daga jikin bangwayen dakin kuma ko ina an sakale fatu na dabbobi iri-iri. A dan karamin muhallin da aka bari a gabansa suka zube su ukun, Iya na ta kokarin gyara tsayuwar kan Jebu da ke a langare.
"Alagafarta Malam barka da rana, wannan ita ce diyar tamu da muka kawo, wadda ta gamu da wani ciwo da ba mu san kansa ba tsawon shekaru biyu!"
Malam Bogaji ya ɗaga kai ya kalli Jebu dake jikin Iya, sannan ya miƙa hannu ya dauki tawada ya fara rubutu bisa allon dake gabansa.
"Nawa ne lissafin taurarin haihuwarta?"
Malam Bogaji ya tambaya hankalinsa bisa kan allon da yake riƙe da shi. Malam Usman ya kalli Iya da ita kanta rudani ya cikata, domin wannan abu ne da ba su sani ba, jin sun yi shiru yasa ya dube su.
"Ba-ba mu sani ba Alagafarta!"
"A wace shekara kuma a wani wata, sannan wata rana aka haifeta!"
Wannan kam cikin hanzari Malam ya zayyana masa, shi kuma ya yi amfani da su wurin lissafa taurarin haihuwar tata da yake bukata, sannan ya ci gaba da rubutu bisa allonsa. Hannunsa dake rike da alkalami ya janye daga kan allon, sannan ya kai kan bakinsa yana nazarin abin da yake rubuce kan allon, yayin da Malam da Iya suka zuba masa ido suna jiran jin abin da zai fito daga bakinsa.
Bayan shudewar wasu sakkani Malam Bogaji ya bude idanuwansa a kan allon, saboda shi kadai ya san abin da ya gani, kansa ya daga ya kalli Jebu, sannan ya sake kallon allon, irin kallon da yay wa Jebu yasa Malam da Iya suka dubi juna, domin abu daya ne ya zo cikin tunaninsu cewar ya gano wani babban lamari dangane da jinyar Jebun.
Gyaran murya ya yi sannan ya gyara zama ya dubesu da kyau yana aje allon hannunsa.
"Zainab sunanta ko?"
Da sauri suka gyada kai, cike da mamakin yanda aka yi sunanta na yanka ya bayyana gare shi ba tare da sun furta masa ba.
"Mayu ne suka kamata. Ku godewa Allah, domin yau saura kwana uku a cinye kurwarta..."
"La haula wala ƙuwwata illa billah! Yanzu Malam ina mafita?"
"Akwai mafita, sannan zan iya mata magani, amma akwai sharadi!"
Malam ya gyara zama, cikin sauri yace.
"Ko nawa ne zan biya domin ka mata magani Malam, zan biya ko nawa ne!"
A karo na farko, Malam Bogaji yay murmushi yana girgiza kansa.
"Bana bukatar ko da ƙwandala daga gareku!"
Batun ya kara saka Malam da Iya cikin mamaki, hakan yasa suka dubi juna, kafin suka sake kallon Malam.
"Me... Kake buƙata mu yi Malam?"
"Ina da mata huɗu, 'ya'yana goma sha uku, gaba ɗaya cikin 'ya'yana goma sha uku biyu ne kacal maza, dika sauran mata ne, babban dana shi ne Auwalu, wanda ya kasance direban babbar mota, abin da nake so a nan shi ne ku bawa ɗana aurenta, ta haka ne kaɗai za ku iya biyana ladan maganin da zan mata!"
A lokacin hukuncin wanzuwar kaddararsu ya sauka a doron duniya, wanda yake rubuce cikin lamhil Mahfouz, wanda aka kirkire shi tun kafin a samar da su. Halin da maganar Malam Bogaji ta cilla Iya da Malam Usman, da kuma tunanin wahalar da suka sha ta naiman magani na tsawon shekaru biyu, yasa nan take suka yanke shawara ba tare da sun yi duba ko la'akari da abin da ka iya zuwa ya dawo ba... A lokacin ba abin da suke tunani face lafiyar 'yarsu, ba su bukaci amincewarta ba, domin sun san halinta, sun kuma san yanda take musu biyayya ba za ta taɓa bujirewa ko wanne umarni nasu ba, musamman idan ta ji cewa dalilin naima mata magani yasa suka yanke wannan hukunci.
Nadamarsu ɗaya ce a wannan lokacin, da suka tuna da matashin saurayi Muhammad Sani, wanda maganar aure ta shiga tsakaninsa da Jebu, domin ba dan wannan jinyar da ta kwantar da ita ba, da tuni an daɗe da yin aurensu, sai dai da suka duba suka gani, sai suka gane cewa wata kila Allah ya ƙadarta hakan ne saboda Jebu ba rabon Muhammad Sani ba ce. Dan haka suke kyautata zaton shi kansa Muhammad Sani zai fahimci inda suka dosa a matsayinsu na iyaye.
Abin da suke hange ke nan a nasu bangaren, ba tare da sanin abin da Malam Bogaji yake hasashe ya sha banban da nasu ba Ya yi duba game da taurarin yarinyar, yaga cewa yarinya ce da za ta kai arziki ga duk wanda za ta raɓa, hakan tasa ya yanke shawarar aurawa dansa ita domin ya zamana su za su amfana da wannan arziki.
A halin yanzu Auwalu yana da mata daya da yaransu biyu, kuma ya san halin mafisa irin ta matar Auwalun, wanda ba za ta bar shi ya zauna da wata mace ba bayan ita, sannan shi kansa Auwalun ba zai taba lamunta da batun auren ba. Amma ya tari aradu da ka, domin da zarar ya nuna masa dalilinsa na yin wannan abu tabbas Auwalun zai yi farin ciki da hakan.
A nan aka kulla wannan aure mai cike da tarin rikici, wanda zai haifar da tarin birkitattun lamuran da kai ba zai iya ganesu ba. Wani irin aure na ban mamaki, wanda zai yi albarka, albarkarsa tai yi girma ta samar da inuwar da ko makiyi zai so ya raɓa.

MADUBIStories to obsess over. Discover now