SANADIN SHI 11-20

Start from the beginning
                                    

Ko wane da course din da yake karanta dan ba faculty dinmu daya ba, Teemarh tana humanities sai ni ina polic science sai kuma Meenat tana low shiyasa tafiyarmu take da banbanci kowa da lokacin da yake tafiya.

Tunda na taso samari sukayi man ca!kowa ka gani yazo gidanmu sai yace ni yake so da yake daman nafi duka yan gidanmu kyau bani kama da kowa sai dai kamar jini amman komai nawa daban yake akan rasa wa na biyo a cikin dangin Baba da Mama nidai gani nan kama ta daban da ta kawo..ni kuma tunda Allah yasa na taso bani kula kowa duk wanda zaice yana sona to yayi aikin banza har da wofi ma dan kayi ka gama ka kama gabanta ba lokacinka zanyi ba.

Yau tunda na tashi na fara shirin zuwa school dan muna da lecture 8,shiyasa tunda na tashi asuba ban koma bacci ba dan nasan halin Wasila da shigen nacin bala'i dan da na kuskure na ja mana makara ta dunga mita kenan har sai na bani da mitarta... shiryawa nayi cikin wata atamfa purple dinkin riga da siket ni na dinka kayana da kaina dan gidanmu ba wanda bai iya dinki ba sai dai idan baka sa kanka koya ba,size bag dina na dauka na fito parlo na tadda Mama tana hada ma Baba break zama nayi Ina cewa.."Mama Ina kwana." Kallona tayi fuskarta dauke da murmushi tace.."lafiya lau Kulu,fatan dai babu wata matsala dai ko.?"

Girgiza kai nayi na tashi na hada tea na dauki bread Ina cewa.."babu sai dai kudin hannuna sun kusa karewa fa." Murmushi tayi tana cewa."Kulu ba dai kashe kudi ba,ai Babanki bai Kai da fita ba idan ya fito sai ki gaya mashi,amman duka duka yaushe Babanku ya baki duba biyar har kin kusa ganin bayanta?kuma bayan na hanaku yawan kashe kudi kamar ba gobe."

Turo baki gaba nayi Ina cewa.."amman Mama ai nayi kokari yau fa sati da bani 5k din da kike magana,kinga dai kudin naped kanshi ya karu ga kuma handout banda abinci ai Ina ma yin maleji sosai gaskiya nidai." Har zatayi magana Baba ya fito yana cewa."sai kuta yin addua Allah ya kara budi,ya bude hanyar samu sai ai ta baku yanzun bayan kudin babu wata matsalar ko.?" Dariya nayi Ina kurbe shayi nace.."Allah ya barmana kai Babanmu,Babanmu maganin kukanmu." Dakuwa yayi man yana murmushi yace.

"Ai Allah baya barin wani dan wani yaji dadi,nidai fatana Allah yayi maku albarka ya kuma kareku da kariyarsa ya bani hanyar da zan baku halak malak."
Dan marairaice fuska nayi Ina cewa.."Allah dai ya kara maka tsawon rai Baba,banda wata matsala bayan ta kudin." Da Amin ya ansa yana cigaba da yin break dinshi na rigashi tashi,dakatar da ni yayi yana cewa.."tsaya na dauko maki kudin ko Jiddo." Murmushi nayi kawai Ina ce ma Mama."yau mai zaku girka mana da rana.?"harararta tayi tana cewa.."abunda kika nemo kika bamu mijina." Dirdira kafafu nayi Ina cewa.."wayyo Allah Mama daga tambaya." Itama yin yanda nayi maganar tayi tana cewa.."wayyo Kulu daga baki ansa." A tare mukayi dariya Ina rungumai bayanta nace.."inasonki Mama sosai,Allah yasa ki gama da duniya lafiya." Lakutar man hanci tayi tana cewa.."Nima inasonku Kullu,Allah yayi maku albarka keda yan'uwanki baki daya,ya kareku da karewarshi."

Fitowa Baba yayi yana cewa.."to masoya kun fara ko?yanzun zaku fara nunaman banbanci." Rufe baki nayi Ina cewa.."ai bamu Isa ba Baba kaima ai kasan kaine mai babbar fada a birnin Zuciyar Hauwa'u Kullu Jidda Abdullah jibir."murmushi kawai yayi yana girgiza kai ya mikoman kudi yace.."gasu nan sai a jallallauta kinji Kakata Kinga dai Baban nan naki ba kudi ne dashi ba." Ansa nayi Ina lissafawa naira dubu goma ne murmushi nayi nace.."nagode Babana Allah ya Kara bude ya Kara tsawon rai,Ina kaunarka Babana." Murmushi yayi yana cewa."ki kula kinji Kakata ,Allah yayi maku albarka." Da Amin na ansa na fito waje Ina duba time dan nasan halin Wasila ila tana kofar gida tana jira sai cika take tana batsewa.

Koda na fito cikin sa'a ban tadda Wasila ba tsaya sai na sauke ajiyar zuciya Ina mai nufar gidansu da yake unguwarmu d'aya,duk da ba jikin gidanmu gidansu yake ba amman tafiya kadan zakayi ka iso gidansu daga gidanmu.

Kafin na ida Isa gidansu Wasila ta fito tana kama baki tana cewa.."A'a yau kuwa za'ayi ruwa har da kankara Hauwa kice da kanki?." Murmushi nayi Ina cewa.."ya  son ran  yanmatan zuciyarki?ai nayi fushi nima ba zaki kara jirana ba sai dai ni na dunga jiranki daga yau dan na gaji da gorin da ake man kusan kullun." Dariya tayi tana kallona sai kuma tace..."tabbb mu gani kasa ke din? da dai baki dan banzan bacci dai,amman na baki kwana biyu kadai kafin angulu ta koma gidanta na tsamiya."daure fuska nayi Ina cewa.."wato haka ma kika ce ko.?" murmushi tayi tana yin gaba tace."eh ke din ai halinki na sani shiyasa." Bin bayanta nayi Ina cewa.."ni din dai ko.?"Daga man kai tayi tana cewa.."eh." Shikenan ni kuwa in shaa Allah sai na baki mamaki yanmata." Dariya kawai tayi muka cigaba da tafiya har muka iso bakin titi,muna isowa Yaya Auwal ya tsaya gabanmu da mota yana zuge glass din motarshi yace.."Jidda sai Ina da safenan sarauniyar mata.?" Dan karamin tsaki nayi Ina dan yin murmushi nace."Ina kwana." Da yake Ina dan jin nauyinshin abokin Yaya Muhammad ne tare sukayi karatu sai dai shi Yaya Muhammad yana ingila can yake karatun likita ya samu scholarship,amman duk tare suka taso a cikin unguwa.

DA'IMAN ABADAN (Sanadin shi)Where stories live. Discover now