YAN UBANCI

114 3 0
                                        


        🅿️9️⃣⏩1️⃣0️⃣

  Hindatu ta shiga makaranta  kuma alhamdulillah  tana k'ok'ari sosai, dan duk da makarantar  k'auye ce amma hakan bai sa malaman makarantar suna yin ojoro ba. Dan haka sai ya zamana  Hindatun  ta k'ara sanya abun a rai kullum tana karatu  sannan  da yamma ta tafi makarantar allo  ta kofar gidan su. Ikilima  ma kwa na arabi ba boko  sai  shegen yawan tsiya da fad'ace -fad'ace a gari gashi idan ma Ummarta ta d'ora mata talla sai dai ta kawo kud'in ba dai -dai ba amma hakan bai sa Ummarta ta tsawatar mata ba sai ma ta d'akko sabon salo na koyawa yarinyar  kaiwa tallan gurin maza a cewarta sun fi siya  dan wani lokacin  ma har su kan yi juye ko su ba da kud'in  fiye  da na kayan ,hakan yasa  yarinyar  ta ke kai wa  talla shago da duk in da ta san maza suna zama ganin tana samun kud'i fiye da na kayanta yasa take kai musu dan ba wai haka kurum suke k'ara mata kud'in ba suna yin  wasan banza ne da ita dan tsabar mulmulata da maza ke yi yasa ta fara k'irgen dangi ita kwa uwar ba ruwanta in dai zata ta kawo mata kud'i to babu ruwanta da me zai faru wanda hakan bata san kuskure bane babba  amma ita ko a jikinta  Ummi Ishalle  ce ke k'ok'arin  ganar da ita amma ta mata rashin mutunci, shi kwa Malam da yake a shanye sai kallo da ido.Haka rayuwa ta cigaba da kasancewa  har Hindatu ta kammala karatun ta na primary school  ta shiga junior, bayan ta kammala Junior School sai kawai ta maida hankali kan karatun arabi dan dama iya Junior School  ne yanzu haka ta  kusa ta yi  saukar Alqur, ani  mai girma. Ikilima ma kwa sai dai gyaran Allah a lamuranta dan yanzu ta zama bata da wasu abokan huld'a sai maza ta je su mammatseta su bata kud'i  ta  yi harkar  gabanta, dan ma dai Ummi Ishalle  tana mata nasiha idan ta ga Ummarta ba  ta  nan duk da ba wani saurarenta take yi ba dan ko tana mata fad'a waya take dannawa dan yanzu wayoyinta har biyu da samarinta su ka siya mata dan haka ba ta ko bi ta kan Ummi Ishalle ba ta tashi ta shiga d'aki abin ta.

"Allah kyauta ya shirya mana zuri, a baki d'aya "cewar Ummi Ishalle itama ta nufi d'akin malam za ta gyara.

  Washe gari da safe Hindatu na sharar tsakar gida dan gaba d'aya  ita ke share ko ina ta wanke kwanuka, tana cikin sharar Ikilima ta fito daga d'aki da wata riga mai k'aramin hannu sai zani da ke daure a jikinta tsayawa ta yi tana k'arewa gidan kallo tana wani yatsina.

"Kai ni daman ba a gidan nan aka haifeni ba wlh me za,ayi da talauci gida duk yab'en kasa ga wasu dabbobi su yi ta damunka da kuka su hanaka barci mai dad'i,hmmm gaskiya ni ba  na son talaici" Ikilima  ta fad'a tana wani kama tsantsa.Ummi Ishalle  ce da ke baiwa dabobi ruwa ta juya ta kalleta ta jijjiga kai cikin takaicin hali irin na Ikilima duk da ta san ba laifinta bane laifinta laifin mahaifiyarta ne dan gaskiya akwai k'arancin tarbiya a tattare da Ikilima.
Hindatu kwa da ke shara ko d'ago kai ba  ta yi ba bare ta kalli Ikilima shararta kawai ta ke a nutse, dan ita har ga Allah tausayin y'ar uwarta ta ta ke yi  dan gaba d'aya rayuwarta babu wani hali mai kyau sai dai addu, a kawai Allah shiryeta.

"Ke zo ki kwalfa min ruwa ki kai min bayi zan yi wanka"Ikilima ta ce rai b'ace dan ganin jelar gashin Hindatu  da ya fito tana k'asan d'ankwalinta gashi har tsakar bayanta amma ita nata ko parking bai yi sai dai  ta je a mata k'arin gashi.

"Babu ruwa  a gidan yanzu za,a kawo sai dai ki jira idan an kawo komai zuba ki kai sai ki yi wankan "Hindatun ta fad'a tana  had'e rai itama.

"Ke ni  ki ke fad'awa haka da me zan ji, da rashin ruwan ko da maganar ki in banda ma talauci ace ruwan wanka ma sai ka jira an kawo yanzu da a birni aka haifeni ruwan wanka ma sai dai in kunna famfo in d'auka, wlh duk laifin Umma ne da ta yi aure a k'auye"ta fad'a a zafafe.

"Ke Hinde ki ke ko Hindu wato har wuyanki ya yi  k'warin da za ki fad'a mata wannan maganar bayan kin san gaba ta ke da ke ko dan ba tarbiya gareki ba, ba, asan  girman na gaba ba amma ba laifinki ba ne laifin  gyatumarki  ne da ba ta koya  miki bin na gaba ba"Umma Kande da ta fito daga d'aki ta fad'a tana  kamo Ikilima  ta  rungume ta da  hannu d'aya.

"Ki yi hak'uri  Umma walllahi ba haka bane, kawai dai  na ga kullum ni ta ke sanyawa in kai mata ruwan wanka amma  iya biyayya ai  ina mata "Hindatu  ta fad'a a sanyaye dan ba halinta bane raina babba duk kuwa da tana jin ciwon abinda su ke yiwa  Umminta  amma sai Ummin  ta ke tausarta dan bata tarbiyar da ta  dace.

"Kande wai dan Allah me yasa ku bakwa son zaman lafiya ko kad'an, kullum ace da tashin hankali ake karyawa a gidan nan duk da ba kulaku mu ke yi ba amma sai kun tarko abin da zai zama b'acin rai, yanzu menene laifinta  dan ta ce in an kawo ruwan ta zuba da kanta duk kuwa da  ita ke zuba mata ruwan kullum  ko da kuwa makaranta  za ta  tafi sai ta  zuba mata amma ba ta tab'a gode mata ba, amma yau ki ke cewa ban bata tarbiya ba,shin har kin kasa gane Hindatu  tana da tarbiya ko ba ta, ko kuma kin kasa gane ke ce baki baiwa Ikilima  tarbiya  ba" Ummi Ishalle ta ce tana kallonta  dan abin da ta fad'a  ya sosa mata rai kawaici da kauda kanta ya sa Kande tana ganin kamar tsoronta take, wanda ba haka bane kawai dai ba ta son tashin hankali sannan  kuma duk abin da  za su yi shi y'ay'ansu za su je su aiwatar a gidajensu wanda ita kuma bata fatan haka.

"Lallai Ishalle  ni ki ke fad'awa son ranki to wallahi kin d'akko ruwan dafa  kan ki, kuma Hindatu ce marar tarbiya  ba Ikilima  ma ba kuma wallahi har gobe a matsayin mak'iya ku ke a wurinmu dan  Y'AN UBANCI tsakanin Hindatu da Ikilima  yanzu aka soma ko ma in ce ba,a soma ba"Kande ta ce tana girgiza jiki.

"In dai Y'AN UBANCI kar ku daina ai  ba kan  mu ba aka soma  ba za, a gama ba kuma a kan  mu, tunda Allah  ya had'asu UBA d'aya  to har  gaban abada ubansu  d'aya  ne"Ummi Ishalle  ta ce tana baiwa Hindatu umarnin shiga  d'aki itama ta mara mata baya, dama Malam yana wurin almajirai.

"Haba  Umma wai ma me yasa ki ka auri wannan Baban namu, baki  auri mutum saurayi ba kuma ki sa shi ya miki alkawarin ba zai miki  kishiya ba kin ga d'aya yanzu barin ni da Y'AN UBA, amma ga talauci ga zaman k'auye .

"Yi hak'uri y'ar  lelena akwai dalilin da  ya sanya na auri babanki, sabo da tarin kadarorin  da ya tara kuma mu  kad'ai  za mu ci ba tare da wadannan y'an bak'inciki  ba, kin ga idan mu ka mallaki kadarorin sai mu je  binni mu sayi tanfatsetsan gida" kande ta ce tana  washe baki kamar dai abin ya  faru ma.

"Yauwa  Ummana ashe akwai abin da  ki  ka shirya  mana "Ikilima ta fad'a tana  k'ank'ame Kande.

"Haka ne sha kuruminki komawa binni kamar an yi an gama kuma ko ba mu koma binni ba a binni za ki yi aure, dan sai dai  wasu su ga ana zuwa binni amma su da binni sai  a labari "

"Yauwa shi ya sa nake sonki, ki bud'e k'aramar jakata ki irgi dubu biyu "

"Yauwa y'ar albarka  Allah k'aro miki masoya amma a binni "Umma Kande ta ce tana wata dariya.

*Bayan  wani lokaci*

Rashin zama lafiya  da ya ke gudana  a gidan Malam Buba ya sa Nana ta nemi izinin mijinta ya zo ta  d'auki  Hindatu  ta tafi da ita Maigatari domin cigaba da zama a can dan dama tana da burin haka dan ta san zaman gidansu sai a slow, kuma ta samu miji mutumin kir ki ya amince mata, dan har lokacin Allah bai ba ta  haihuwa ba.Sosai Ikilima  da Ummarta su ka yi bak'inciki  dan kuwa bak'inciki sa son Hindatun ta bar gidan dan sun fi so ta zauna su cigaba da nuna mata Y'AN UBANCI, haka dai su ka hak'ura da wani k'udurin  na da ban. Tun da ta koma Maigatari  aka sanyata a islamiya amma ba ta allo ba, sannan  an sanyata a boko a in da ta fara zuwa makarantar jeka ka dawo ta cigaba daga  S. S 1 nan ta cigaba da karatun ta hankali kwance  ba tare da damuwa ba.

YAN UBANCIWhere stories live. Discover now