LABARINSU 3

31 0 0
                                    

*LABARINSU*
*© SALMA AHMAD ISAH*
*TAURARI WRITERS*
*03*
~~~
_-*If it doesn't set your soul feel free, then it isn't love...*-_
***
*No.234, Efab Estate, Gwarinfa, Abuja*
*07:30am*
“An ya kuwa kina ganin abun nan zai iyu ?, jiya fa ba kiga irin faɗan da muka yi da shi ba, wai ka wai dan na mata faɗa, sai ciwonta ya tashi, ko a ɗakina ma bai kwana ba.....”
Muryar Hajjara ta faɗi ta cikin wayar da take da ƙawarta Fati. Tsaye take a jikin wardrobe, yayin da hannunta na dama ke riƙe da murfin wardrobe ɗin, na hagun kuma riƙe da wayar da take.
“Wai baki yarda da ni ba ne ?, na faɗa miki shifa wannan aikinsa ba irin na sauran ba ne, aikinsa ma ya fi yankan wuƙa kaifi, ke hatta da alburushima baya faɗawa aikinsa saurin ci ba, ke de kawai ki yi abinda na ce miki, za ki kira ki bani labari....”
Hajjara ta yi dariya tana rufe wardrobe ɗin, sannan ta juyo tana kallon Fahima da ke wasa a kan gado.
“In dai har kuwa maganin nan ya yi aiki, ni nasan abinda zan baki”
Tana iya jiyo muryar Fatin cikin dariya.
“Za ki kira ki bani labari....”
Daga haka suka tattauna a kan shirin da suke, kafin ta sauƙe wayar, ta ƙarasa jikin side drawer ta buɗe, ta ɗauko maganin da Fatin ta aiko mata. Ta yi murmushi a fili, sannan ta furta.
“Yau zan ga ƙarshen ƙauna!....”.
MISHAL POV.
Tsaye take a kitchen ɗin gidansu tana dafa noodles, sanye take da baƙar skirt ɗinta ta uniform, sai farar long sleeve oxford shirt ɗin da take sakawa a ƙasan suit ɗin uniform ɗin, sai dai babu suit ɗin. Kanta parker cikin ponytail, jelar na reto a gadon bayanta.
Sallamar Hajjara ce ta sa ta juyo ta kalli bakin ƙofa, a zuciyarta kawai ta amsa sallamar, sannan ta ɗauke kanta ta ci gaba da aikinta.
Hajjara ta yi murmushi, ta ƙaraso cikin kitchen ɗin, ta yi birki a gefen Mishal. Sai da gaban Mishal ya faɗi, sannan ta ɗago da kanta ta juya ta kalleta.
Dan ta fita tsayi, da ma girman jikin ne da ita kawai, ba ta cika tsayi ba. Murmushin da ta ga kwance a fuskar Hajjaran ne ya ƙara tsoro tata, duk da ita ba gwanar tsoron ba ce.
Kuma kafin ta yi wani tunanin, Hajjara ta kai hannayenta ta kamo na Mishal dake riƙe da spoon. Da sauri Mishal ɗin ta janye hannayenta tana zaro ido.
Dole ma da wani abun da wannan matar ta shirya, ta daɗe da sanin cewa ba santa take ba, dan ba iyaka jiya ne ta taɓa tada mata da ciwonta ba.
Tana yawan ja mata matsololi da dama, bata santa!, haka take yawan faɗa mata, to me zai sa yanzu tazo tana mata murmushi.
Dakewa ta yi, dan bata san ta ga rauninta, bata san ta gane cewa ta ji tsoronta.
Hannunta ta kai ta kashe gas ɗin, sannan ta ɗauke ƙaramar tukunyar da ta ɗora noodles ɗin, ta juyeta a cikin lunchbox ɗinta ta fice ta bar mata kitchen ɗin, in yaso duk masifar da take ji da ita ta ƙare a kanta, ta ci kanta ta sha baƙin ruwa.
A parlo ta iske Mama Ladi na bawa Daala abinci. Ta yi murmushi tana aje lunchbox ɗinta a kan coffee table. Sannan ta zaga ya zuwa kan sofa, ta ɗauki suit ɗinta a inda ta ajeta, ta saka a jikinta.
“Mama ni zan wuce, ga Baba Ali nan ya zo”
Ta faɗa yayin da take gyara zaman hairband ɗin dake kanta, bayan ta ji horn ɗin motar Baba Alin.
“To a dawo lafiya, banda rashin ji”
Ta yi murmushi tana ɗaukar jakarta, tare da saɓata a bayanta. A dai-dai lokacin Abubakar da Hammad suka sauƙo a tare.
Tana kallonsu har suka ƙaraso cikin falon, ciki-ciki ta gaisheda Abubakar, dan ba wani sosai suke shiri da ita ba, saboda faɗan da yake mata.
“Yaya, gap ɗin nan ya haɗe, yaushe za mu je kasa a cire min braces ɗin nan?”
Abubakar ya miƙe tsaye, kuma ba tare da ya kalleta ba yace.
“Sai mun dawo daga meduguri....”
“Wallahi da gaske nake Aky, ta haɗe fa, idan baka yarda ba zaka iya gan!.....”
“Ya isheni haka! Ke dole ne duk abinda kike so sai an miki ?!, To ba zan kai ki a cire braces ɗin ba!”
Cikin tsawa da ƙaraji yake maganar, ya ma manta waye gabansa, dan haka kawai yake ganin baƙinta yau, maganarta ma baya san ji.
Mama Ladi ta miƙe tsaye mamaki na cinyeta, tasan ba yau ya saba mata faɗa ba, amma kuma ba ya mata cikin masifa haka, kuma ba ya mata faɗa sai ta yi laifi, amma ita a cikin wannan maganar da ta yi bata ga abun lafi ba.
Ba ƙaramar tsorata Mishal ta yi ba, ta ji ƙofofin numfashinta na neman ɗaukewa, amma duk da haka ta daure ta shiga baza idanunta a falon. Tsaye a bakin kitchen ta ga Hajjara na wani irin murmushi me kama da na mugunta.
Dama ita tasan za'a rina, shi yasa sam bata yarda da matar wan nata ba, dan ko abincinta bata ci, ita da kanta take girka abincinta.
“Ka yi haƙuri Aky!...”
Da ƙyar ta furta hakan, muryarta a shaƙe, dan bata san numfashinta ya ɗauke.
“Baki da magana da ta wuce hakan ai, ke kullum cikin aikata laifi, yau kina wannan gobe kina wancan, ni kenan kullum cikin sintiri a hanyar makarantar ku!, Kin girma amma baki san kin girma ba, saboda Allah yanzu yarinya kamar ke ace bata san ciwon kanta ba?, to bari ki ji na faɗa miki idan har baki kama kanki ba, wallahi sai na saɓa miki!”
Har yanzu cikin ƙaraji yake maganar, yayin da Mishal ta runtse idonta tana kawar da kanta gefe, duk da isashiyyar iskar dake falon ita sam bata iya jinta a huhunta, sam bata jin wata iska na kai mata inda ya dace.
“Haba Abbakar? Ya haka dan Allah?”
Mama ta faɗi cikin tausasawa.
Abubakar na maida numfashi kamar wanda ya yi gasar tsere ya kalleta. Kafin a fusace ya fice daga falon.
Hajjara ta ji kamar ta zuba ruwa a ƙasa ta sha, duk ƙaunar duniya sai a ce Mishal, komai Mishal komai Mishal, hatta da makarantar da take ta fi ta Hammad tsada, kuma har mota ya siya mata tare da ɗaukar mata driver, bayan ita nata ɗan a school bus yake tafiya. Koma dai miye yau ranta ya yi fari tunda har ya mata faɗa. Ta kaɗe gefen rigarta ta yi sama, dan taje ta bawa Fati labari.
“Zauna Mishal...”
Mama ta faɗi tana zaunar da ita, tare da sauƙewa jakar bayanta, ta ciro littafi a ciki ta shiga mata fiffita. Kafin ta samu ta dawo hayyacinta.
“Kin sha maganinki ?”
Kai ta gyaɗa mata tana miƙewa, ba tare da tace mata komai ba, ta ɗauki jakarta haɗi da lunchbox ɗinta ta fita.
Mama ta bi bayanta da kallo, zuciyarta cike da tausayin yarinyar.
“Allah ka kawo mata sauyin rayuwa!....”
Wata ƙila ta faɗa a bakin 'yan amin, wata ƙila Allah ya zaɓeta ne dan ta zamo silar yin addu'ar wani abu dake shirin faruwa kwanaki masu zuwa.
Addu'ar tata, ita ce ta zama silar faruwar wata ƙaddara da Allah ya hukunta faruwarta a 'yan kwanaki masu zuwa. Wata iriyar ƙaddara da zata tarwatsa komai, sannan ta zama silar shiryuwar wasu lamura.
*Brickhall School, Kaura district, Abuja*
*09:40am*
RABI'A POV.
“Gashi, driverna na bawa saƙo ya siyo min, kuma ya ce ya nema amma bai samo irin wannan ɗayan ba, sai ɗan kwali ya samo...”
Cewar Mishal, yayin da take miƙa mata lalle ɗan kwali.
Rabi'a ta sa hannu ta karɓa. Tsaye  suke a bayan ajujuwan makarantar, a ƙofar store, inda ake aje kayan share-share na makarantar.
Rab'a ta juya ta kalli dama da hagun inda suke tsaye.
“A ina zamu yi kenan ?”
“Ga kujeru a can, muje mu zauna”
Kuma da ga haka, suka ƙarasa inda kujerun suke, suka zauna, sannan Rabi ta shiga haɗa lallen. Yayin da Mishal ke dudduba jakarta, a ciki ta ɗauko biscuits, ta buɗe ta shiga ci. Cike da mamaki Rabi'a ta kalleta.
“Bakya azumi ne ?”
Mishal ta yi murmushi, har karafunan braces ɗin da aka sa mata suna bayyana.
“Wahala ce ba zan iya ba, ga zuwa makaranta ga azumi, inaaa!”
Rabi'a ta yi dariya, a kamaninta idan ka ganta sai ka ce tana da wasu shekaru masu yawa,amma da zarar ka yi magana da ita ko na minti uku ne za ka fahimci yarintarta ƙarara.
“Shekarunki nawa ?”
Mishal ta dakata da taunar biscuits ɗin dake bakinta, ta ɗan ɗaga olive green colour eyes ɗinta, tana san ta tuna shekarun nata. Kafin ta sauƙe su a kan Rabi'a dake ɗaure ledar lallen da ta gama haɗawa.
“I’m 17, next year zan cika 18....”
Rabi ta ɗage girarta cikin murmushi tana kallon lallen da ta gama ɗurewa.
“Ki ce babbar yarinya ce...”
Mishal ta yi dariya, wani abu da ba kasafai ta cika yinsa ba.
“Ke fa shekarun ki nawa ?”
“Ki ƙara biyu a kan naki”
“Sha tara ?”
Rabi'a ta gyaɗa mata kai. Ganin ta gama haɗa lallen yasa Mishal maida sauran biscuits ɗinta cikin jaka, tana karkaɗe hannunta, tare da taune sauran wanda ke bakinta.
Ta miƙawa Rabi'a hannunta na dama, sannan Rabi'a ta fara zana mata lallen.
“Wow!, Amma fa ta yi kyau”
Mishal ta faɗi a karo na barkatai, sanda aka gama zanen lallen, ta ɗaga hannayenta sama yafi sau a ƙirga, sai kallon lallen take tana sakewa. Ba za ta ce when last rabonta da ba.
“Nawa ne kuɗin lallen ?”
Sai ta ga Rabi'a ta haɗe rai.
“Shekaru nawa na baki ?”
“Biyu”
Ta masa tana mamakin abinda ya haɗa tambayar da ta mata da kuma wannan batun.
”Kinga kenan ni yayarki ce, kuma ina matsayin yayarki ai bazan karɓi kuɗin lallenki ba...”
“Yanzu mun zama 'yan uwa kenan ?”
Rabi'a ta gyaɗa mata kai tana murmushi.
“Adawiyya ?”
Zuciyar Rabi'a ta dunguwar a lokaci guda, Adawiyya?!, kaf duniyar nan mutane biyu ne ke kiranta da sunan, Ummanta, da kuma yayarta Baby!.
*Unguwar Madallah, Suleja, Niger state*
*05:30pm*
“Wai har sun muku hutun?”
Cewar Saratu, yayin da takewa Rabi ƙananun kalba.
“An musu dai”
Rabi ta bata amsa. Suna zaune ne a ƙofar ɗakinsu, bayan Rabi'an ta dawo daga wurin aikinta ne ta share gidan tas, duk da wahalar rana da kuma aikin da ta je ta yi, ga kuma azumin dake bakinta.
Amma haka ta share gudan tas, kuma bayan ta gama ta ɗora da wanke-wanke. A lokacin Saratun tace mata ta zo su fara kalbar, tun da ta riga ta tsefe.
“Ai har ke, tun da de ba za ki je makarantar ba har sai an koma”
Rabi dai bata sake cewa komai ba, dan tun da ta ambaci kalmar 'makaranta', tunaninta ya tafi ɗazu, ta shiga tuna abinda ya faru tsakaninta da sabuwar ƙanwarta a ɗazun.
“Jibi za mu tafi garinmu, a can za mu yi bikin sallah”
Muryar Mishal ɗin ta katseta a ɗazun. Sai kawai ta yi murmushi.
“Ina ne garin ku ?”
“Maiduguri”
Mishal ta bata amsa tana firfita lallen hannunta da iskar bakinta. Rabi'a ta gyaɗa kanta. Tana ƙara tabbatarwa da kanta hasashen da take a kan Mishal ɗin, na kasancewarta shuwa arab.
“Shikenan, na san zuwa yanzu an koma break, bari naje na share inda aka ɓata, ki kula da kanki, Allah ya dawo da ku lafiya, sannan ki gaida Mamanki idan kin koma gida”
Ta faɗi tana ƙoƙarin tashi, amma maganar Mishal ɗin ta gaba ita ce ta hanata tashin.
“Mamata bata raye, kuma tun a sanda zata haifeni ta rasu, ban san babana ba ma, lokacin da cikina ya rasu, tare da yayana kawai na taso.....”
Rabi'a ba za ta iya cewa ga abinda take tunanin ba a lokacin, tasan dai kawai ta tsirawa ƙaramar yarinyar ido ne, tana nazarin ya akayi ta rayu tsawon shekarunta babu iyaye. Ita da ta rasa iyaka mahaifiya ma kawai rayuwarta ta hargitse bare ita da ta rasa duka biyun.
Kuma bama wannan ba, ba ma ta sansu ba, bata taɓa ganin ko ɗaya daga cikinsu ba.
“Ke Rabi? Tashi ki zo ki soya mana doyar nan!”
Muryar Habiba ta dawo da ita zahiri, a hankali dubanta ya kai kan Habiban dake tsaye a kansu.
“Umma ki bari mana na ƙarasa mata, saura guda biyu fa....”
“Ban yi niyya ba, yanzu nake so ta tashi ta min aiki na....”
Ba tare da Rabi'a tace komai ba, ta shiga ƙoƙarin jan doguwar kalbar dake riƙe a hannun Saratu dan ta miƙe, amma sai Saratun ta mayar da ita ta zaunar.
“Gaskiya Umma ba kya kautawa, Wallahi wannan ba adalci ba ne, yarinyar nan ta je ta yini tana aikin bautar da ba ita take cin kuɗinta ba, dan ke take kawowa, sannan ta dawo ta yi aikin gidan nan, kuma yanzu ta samu ana ɗan mata kalbar da za ta yi adon salla sai ki ce baza'a mata ba ?!”
Habiba ta ɗan sunkuyo tana miƙowa Saratu bayanta.
“Da ke ni mama Saratu, na ce inji didim!, sai na tabbatar da ranki ya ɓaci....”
Ta miƙe tana ci gaba da faɗin.
“Na taɓo uw*r ki Rabi ko?, To baki isa ba, dole sai ta tashi ta soya doyar nan!....”
Kafin Saratu ta sake cewa wani abu, Rabi ta yi wuf ta miƙe tsaye, tana ƙoƙarin ɗaure kanta da ɗankwali. Gashin kanta da tsayinsa ya ragu a yanzu ya kwanta luf a gadin bayanta, har yana reto.
“Gaskiya Umma na gaji!, Wallahi na gaji da abinda kikewa yarinyar nan a cikin gidan, ita ma fa 'ya ce, kuma ko baabaarta bata raye hakan ba ya nufin a cusguna mata. Umma kema uwar 'ya'ya mata ce, wata rana gidan wani za muje. Na tabbatar da idan uwar miji ko 'yan uwansa suka mana haka ba za ki ji daɗi ba. To ita ma kamar haka ne, tana da dangi bayan mu. Dan tsabar san zuciya irin naki yau shekarar yarinyar nan biyar a gidan nan, amma kin hanata ta je ta ga dangin mahaifiyarta, dan kar ta je ta faɗi irin azabar da ake bata a cikin gidan nan su hanata dawowa ki rasa baiwa. Wallahi Umma wannan ba adalci ba ne, ke ba kya tunanin wata ƙila wannan abun da kike shi ne ya zama sannadiyyar tagayyarar mu?, Ita 'yar taki ta fari, bata jin daɗin aurenta, sannan ni, shekaruna 27, amma na rasa mijin aure, ko sau ɗaya saurayi bai taɓa zuwa ƙofar gidanan yace yana sallama da ni ba, ga kuma Mama, wadda ta lalace da bin maza!.....”
“Ya ishe ni haka Saratu, ki rufa min baki ko na make ki a wurin!”
Saratu ta share guntuwar ƙwallar da ta zubo mata ta buɗe labulen ɗakinsu ta shige ciki.
Rabi'a da ke kiciniyar hura wuta ma ta share tata ƙwallar, saboda tunawa da ta yi da dangin Ummanta, ta tuna yanda suke matuƙarsanta da 'yar uwarta, sai kuma tunanin Anti Saratun, Allah ya sani kuma ita ma ta sani, ba ƙaramin cutuwa baiwar Allahn nan take  da zaman gidan.
Kuma ta san cewa Anti Saratun na matuƙar san aure, dan tasha kamata tana kuka, kan abun da ke damun rayuwarta, sai dai ta zauna ta bata baki har ta samu ta yi shiru.
*DSS Headquarter, Maitama Evenue, Abuja*
*10:30am*
KULIYA POV.
“Aliyu Zaid Bichi!”
Cewar shubansa, yayin da yake tsaye a gaban shugaban, ya ƙame cike da girmamawa.
Wani murmushi kwance a fuskar ogan. Kuma cikin abinda bai wuce sakan biyu ba, wannan murmushin ya sauya zuwa ɓacin rai ma bayyani.
“Kai wai me yasa ba zaka taɓa sauyawa ba?, yanzu saboda shashancin da ka yi, ɗaya daha cikin criminal ɗin ya mutu, kai kwata-kwata baka iya controlling fishinka ne ?!”
Kuliya ya ƙara ƙamewa yana kallon wani wurin da ban, dan da ma yasan hakan sai ta faru, ba ma yasan ya kalli fuskar ogan, dan idan har ya kalleta, zai iya hasaso kansa yana marin shugaban nasa, kuma wata ƙika ma hasashen ya zama gaskiya.
Dan baya san a ɗaga masa murya, daga an ɗaga masa murya yake kai hannu, shi kansa yasan cewa zuciyarsa a kusa da take, abu kaɗan ne ke tunzura shi. Ya ɗaga kafaɗarasa yana ci gaba da kallon wani hoto dake aje a bayan ogan nasa.
“A haka kake san zama kamar Lion ɗin ?...... Shi Lion ɗin da kake san zama sam ba haka yake ba, cikin basira da taka tsan-tsan yake gudanar da aikinsa, ba shi da saurin fusata kamar kai, ba shi da saurin kai hannu kamar kai!....”
Lion?!, wani suna guda ɗaya da yake ƙwarara masa gwiwa a kan aikinsa, wani sunan da ko jinsa ya yi sai ya ji jinin jikinsa na tafasa. Kuma ba shi kaɗai ne sunan Lion ke bawa ƙwarin gwiwa ba.
Kusan duka ma'aikatan DSS sun san sunan Lion, dan abu ne mayuwaci, ka je training ɗin DSS ba tare da an  baka maka tarihi da kuma sunan Lion ba.
Duk wani jarumi da mai hazaƙa a hukumar burinsa kawai ya zama kamar Lion. Sai dai kuma duk da wannan nasara da kuma jarumta irin ta Lion ɗin, in ka ɗauke manyan hukumar tasu, babu wanda yasan kammanin fuskarsa, sunan nasa kawai ake ji, sai kuma ƙwazon da yake a aikin nasa, sunan nasa ma ba na ainahin kowa ya sani ba. Code name ɗinsa kawai suka sani.
Amma duk da haka yana burge kowa, dan duk wanda zai gwada wata jarumta da kuma san nuna role model ɗinsa sunan Lion za ka ji ya kira.
“Sam shi Lion ɗin ba haka yake ba....”
Muryar Ogan nasa me amsa sunan Chidera Kingsly ta katse masa hanzari.
“Lion yana da basiri, he is so intelligent, amd smart, ya san aikinsa, baya komai cikin fushi, cikin nustuwa da tunani yake gudanar da aikinsa.....”
Kuliya ya sauƙe kansa ya ɗora manyan idanuwansa a kan fuskar shugaban nasa. Kuma har zuwa lokacin bai ce komai ba, dan tun bayan gaida shi da ya yi a sanda ya shigo office ɗin, bai ƙara cewa komai ba.
Kuma shima Chideran yasan cewa ba lalle ya sake cewa komai ɗin ba, dan kowa yasan miskilancin bawan Allahn nan.
“Na san cewa yanzu haka ka rayawa ranka cewar; ka dalle min fuskata da mari!”
Wani abu me kama da murmushi ya faru a cikin zuciyar Kuliya, dan ya canka dai-dai, hasasowa kansa yake yayin da yake kashe sauraye a kan fuskar chideran, dan ba sauro ɗaya ba.
*
“Ehemm!”
Muryar Kuliya ta yi gyaran murya, alamun ya bawa wanda yake buga ƙofar izinin shiga, dan wannan ɗabi'arsa ce. Kusan duk wanda yake headquarter ɗin yasan da hakan.
Shi a ganinsa magana ma wani kayan gabar ne, amma idan masifarsa ta tashi yafi ub*n kowa iya ɗaga murya.
Zaune yake a office ɗinsa, yayin da yake daddana system. Kamar kullum; sanye yake da baƙaƙen kaya, wata baƙar suit ce a jikinsa. Hatta da long sleeve oxford shirt ɗin dake ƙasan suit ɗin baƙa ce.
Ƙofar office ɗin ta iyo ciki, alamun dai wanda yake bayan ƙofar yana shirin shigowa. Suffar Abubakar ta bayyana a bayan ƙofar.
Kallo ɗaya Kuliya ya masa ya ɗauke kai, tare da ci gaba da danna laptop ɗin gabansa.
“Barka da safiya..... ni na gaida ka, tun da kai ba za ka iya ba gaisheni ba”
Abubakar ɗin ya faɗi yana ƙarasowa cikin office ɗin. har ya zauna a kujerar dake tsallaken teburin Kuliyan bai masa magana ba.
“Me yasa yau ka makara ?”
Muryar Kuliyan ta tambaya bayan wani lokaci, ba tare da ya kalli Abubakar ɗin ba. muryar tasa kamar da ga sama. Sannan amonta ya fito kamar kullum, cikin ɗaci da alamun ɓacin rai.
Dan shi kullum ba'a rasa abinda yake ɓata masa rai. Abubakar ya yi murmushi, to shi ya zai yi ne?, tun da Allah ya haɗa shi zama da mutane biyu masu murɗaɗɗen hali, tsakanin Kuliya da ƙanwarsa Misha!, Ya rasa wannene ya fi wani murɗewar hali.
“Ƙanwarka ce, ta yi rashin jin da ta saba a makaranta, sai da na biya ta can, sannan na ƙaraso nan”
Kuliya ya ɗaga kafaɗarsa ta dama. Shi duka-duka sau ɗaya ya taɓa ganin ƙanwar Abubakar ɗin, ba ma sosai yake iya tuna lokacin ba, dan shekarun da ɗan dama.
“Dama autopsy results ɗin nan na zo karɓa, Kamis yace yana wurin ka”
Ba tare da Kuliyan ya kalle shi ba, ya ɗaga kafaɗarasa ta dama, sannan ya buɗe wata loka dake jikin teburin nasa, ya ɗauko file ɗin,ya miƙa masa. Abubakar ya karɓa  yana miƙewa tsaye.
“Na tafi...”
Ko kallonsa Kuliya bai yi ba, bare ya bashi amsa, kuma shi ma yasan ba lalle ya kalle shin ba. Yasan halin Kuliyan sarai. Har faɗi yake da bakinsa cewa; idan ba Abubakar ɗin ba babu me iya zama da shi a matsayin aboki.
Dan kaf duniyar nan Abubakar ɗin ne kaɗai abokinsa, ba shi da wani aboki da ya wuce shi, sai Sharon da suke ɗan jitiwa, ita ma kuma ba kullum ba.
*Badawa layout, Kano....*
RAJA POV.
“Raja dan Allah, dan Allah!.....”
Cewar wani mutumi a galaɓaice, yayin da yake durƙeshe a gaban Rajan. Kuma bai ko gama rufe bakinsa ba, Rajan ya ƙara tsinduma kansa cikin bahon dake aje a gabansa, wanda yake cike taf da ruwa.
Haka mutumin ya yi ta motsi da kansa a cikin ruwan, saboda azabar da yake ji. Zaune yuke a harabar gidansa. Yayin da Rhoda da su Zuzu ke tsaye a bayansa.
Waɗanan lumssassun idanun nasa na kallon mutumin da kansa ke fancal-fancal cikin ruwan sanyin. wannan innocent face ɗin nasa fayau!, banu wani abu da za ka iya tsinta a cikinta. Kai ba ka ce mamallakinta ne ke wannan aikin ba.
Ƙarar ringing tone ne ya karaɗe wurin. A hankali Rhoda ta duba screen ɗin wayar 'Oga Garuje', shine abun da ta ga an rubuta, dan haka da sauri ta ƙarasa kusa da Raja.
“Garuje ne ya ke kira”
Bai kalleta ba, sai ma bindigarsa ƙirar pistol da ya ɗora a kan fuskar mutumin da ya tsamo kansa daga cikin ruwan. Sannan wannan kamillar muryar tasa ta furta.
“Me yasa ka ci amanar mu?”
A nitse muryar tasa ta fito, cikin wannan sautin nata mai nuna tsantsar innocent ɗinsa.
“Dan Allah Raja....Dan Allah...”
Ji kake Tas!!. Ƙarar bindiga ya karaɗe harabar gidan. Me gadin gidan ya yi saurin faɗawa ɗakinsa. Duk da yasan cewa abun ba zai komo kansa ba. Amma wai me hausawa suka ce ne?, idan ka ga gemun ɗan uwanka ya kama da wuta, to ka shafawa naka ruwa.
Raja ya yi wani murmushi me kama da dariya, a sanda ya ga shigewar me gadin nasa. Kafin ya saki gawar mutumin nan da ya harba a ka. Jini har ya ɓata masa hannu.
Ba tare da nuna damuwa ko wani tashin hankali ba, ya sunkuya ya wanke hannunsa cikin ruwan bahon nan.
Kuma har zuwa lokacin wayar tasa na riging a karo na barkatai.
“Ina ji”
Nutsatsiyar muryarsa ta faɗi,bayan ya amsa wayar, cikin wannan kamala da kamewar tasa, kai ba ka ce shi ne ya kashe rai yanzu ba.
“Raja!, Oga ne da kansa ya yi waya, ya ce ya na buƙatar ka je ka same shi a Abuja....”
Raja zai iya rantsewa kan zuciyarsa sai da ta buga sau biyu a lokaci guda. Kenan tsawon shekarun da ya kwashe yana wannan aikin sun kusa ƙarewa?. Shekaru sama da uku ma rayuwarsa ya kwashe yana bautar da bai san ranar ƙarewarta ba. Sai a yau ne komai ya ke gaɓa. Komai ya ɗauko hanyar ƙarewa. Ya kawo inda ya ke matuƙar burin kaiwa.
Sai dai a yanayin fuskarsa ba za ka tsinci hakan ba, dan miƙewa tsaye kawai ya yi, sannan ya juya yana kallon su Rhoda.
Da waɗanan lumsassun idanuwan nasa, ƙwayar idon wadda ta kasan ce gray color tana kallon yanda su Zuzu ke magana ƙasa-ƙasa. Ya ɗaga kafaɗarsa ta dama, sannan ya ce.
“Yaushe kenan ?”
“Ko zuwa nan da sati ɗaya ne, dan da alama ka koma can da zama, ka ga kenan sai an nema muku gidan da zaku zauna, da dai sauran su...”
“Na fahimta!”
Kuma da ga haka ya tsinke wayar.
“Alandi, Zuzu, ku fita da gawar nan da ga gidan....”
“An gama Oga Raja!”
Suka faɗi suna yin wurin da gawar ke yashe.
Sannan shi kuma ya yi hanyar shiga cikin gidan, da hannu ya yiwa Rhoda alamu da ta biyo shi.
“Rhoda, mun kai ga gaci....”
Wannan salihar muryar ta faɗi a sanda suke zaune a falon gidan.
”Me ya faru?”
Rhoda ta tambaya.
“Alhaji Bala ne da kansa ya ce na je na same shi a Abuja”
Cike da mamaki, murna da kuma farin ciki take kallonsa.
“Kenan mun kusa zuwa ƙarshe?”
Ya ɗaga kafaɗarsa ta dama, sannan ya ce.
“Kusan zan iya cewa hakan”
“Kai amma fa na yi farin ciki...”
Ta faɗi da iyakar gaskiyarta, dan ta yi farin cikin, tana ganin kamar komai ya kusa ƙarewa, kamar an gama komai, kamar wannan wahalar da suka sha tsawon shekaru ta ƙare.
Kuma ba ita kaɗai ke wannan tunanin ba, shi ma kansa Rajan haka yake tunanin sun kammalla komai, komai ya zo gangara, gangarar da zata gangaro da ƙarshen wahalar da suka sha tsawon shekaru.....
Sai dai abinda bai sani ba shi ne; yanzu ne ma komai ya fara, a yanzu LABARIN zai soma, sai a yanzu ne babin ƙaddarar tasa zai buɗe.
Wani sabon babi fil!, wanda babu ɗigo ko ɗaya a ciki, sai na wanda ubangiji zai hukunta. Saboda wata ƙaddara da ke shirin faruwa 'yan kwanaki masu zuwa. Ƙaddarar da zata tarwatsa komai, ta kuma gyara wasu lamuran.
A dai-dai lokacin ƙofar falon ta buɗe, Jagwado ne ya shigo, dan da ma banda shi aka tafi yasar da gawar.
Lighter ce riƙe a hannunsa yana ƙyasta ta, yayin da sigari ke maƙale a bakin. A sa'ar da Raja ya ɗora idonsa a kan wutar, a lokacin ne kuma wannan tsoron ya shige shi, tsoron wuta da Allah ya saka masa tun bayan abinda ya faru da shi.
Baya san ganin wuta sam, domin wuta na ɗaya daga cikin abin da ta zama silar rabuwarsa da mutane uku da suka fi soyiwa a ransa. Da farko ta raba shi da mahaifiyarsa, sai kuma ta zo ta raba shi da ƙaninsa, ɗan uwansa abokin tagwaitakarsa. Sai ku ma Maman Rhoda, wata mace da ta taka rawa mai makuƙar muhimanci a cikin rayuwarsa.
Wani irin wahallallen nunfashi ya ja, ya samu kansa cikin irin yanayin da ya saba shiga a duk sanda zai ga wutar. Duk da yanda yake ta kokawa da tunaninsa kan kada ya koma baya, amma sai hakan ya ci tura. LABARINSA na baya ya soma kunno kai cikin nazarinsa.
_“Zaid, ku tafi, kada ku tsaya a nan.....idan kuka tsaya wutar za ya iya ƙona ku....ku tafi na ce!.....” _
Amon wannan sautin nata ya shiga maimaita kansa a cikin tunaninsa, falon ya shiga rikiɗewa yana komawa gidansu, gidan da suka rayu a ciki, gidan da suka ci gaba da kwana a cikinsa har bayan sanda wuta ta gama ɗaita shi, wannan gidan da suka gina yarintarsu shi da ƙaninsa a ciki.
Sannan hoton ya sauya a idonsa, ya na ganin yanda take watso musu kayansu ta window, yayin da ƙofar falon take a kulle, ta kasa fitowa bare ta buɗe ƙofar har ta samu damar tsira.
Sannan ya kallin kansa da ma ƙaninsa Aliyu dake ta kuka, ƙaninsa me tsantsar kama da shi, dan idan suka kalli juna sai ka ce kansu suke kallo a madubi.
Dan kammanin da suke ya ɓaci, tsayinsu ɗaya, farar fatarsu ɗaya, girman idonsu ɗaya, komai na hallitarsu ɗaya ne, in ka ɗauke ƙwayar idon Zaid da ta kasance ash, sai kuma totsiyar karen dake haƙorin Zaid ɗin. Amma hatta wata ɗabi'a ta ɗaga kafaɗa dukaninsu suna yi.
“Jagwado menene haka ?, Sarai ka sani cewar Raja ba ya san ganin wuta!”
Muryar Rhoda da ke wa Jagwado faɗa ta dawo da shi zahiri.
Bai ƙara ce musu komai ba, ya miƙe tsaye, tare da ɗaga kafaɗarsa ta dama, ya yi ɗakinsa, yana jin yanda Rhodan ta balbale Jagwado da faɗa, shi kuma sai aikin bata haƙuri yake.
_________________
_To fa.... Bana kuma nan muka leƙo?_
_Na ce ba, wai Rajan ne ko Zaid ne?_
_Dan ni na kasa ganewa, kamar Zaid da Aliyu mutum ɗayane, kamar kuma....._
_Ko da yake, ba sai na faɗa ba ai😂_
#Labarinsu
#SalmaAhmadIsah
#Taurariwriters*LABARINSU*
*© SALMA AHMAD ISAH*
*TAURARI WRITERS*
*03*
~~~
_-*If it doesn't set your soul feel free, then it isn't love...*-_
***
*No.234, Efab Estate, Gwarinfa, Abuja*
*07:30am*
“An ya kuwa kina ganin abun nan zai iyu ?, jiya fa ba kiga irin faɗan da muka yi da shi ba, wai ka wai dan na mata faɗa, sai ciwonta ya tashi, ko a ɗakina ma bai kwana ba.....”
Muryar Hajjara ta faɗi ta cikin wayar da take da ƙawarta Fati. Tsaye take a jikin wardrobe, yayin da hannunta na dama ke riƙe da murfin wardrobe ɗin, na hagun kuma riƙe da wayar da take.
“Wai baki yarda da ni ba ne ?, na faɗa miki shifa wannan aikinsa ba irin na sauran ba ne, aikinsa ma ya fi yankan wuƙa kaifi, ke hatta da alburushima baya faɗawa aikinsa saurin ci ba, ke de kawai ki yi abinda na ce miki, za ki kira ki bani labari....”
Hajjara ta yi dariya tana rufe wardrobe ɗin, sannan ta juyo tana kallon Fahima da ke wasa a kan gado.
“In dai har kuwa maganin nan ya yi aiki, ni nasan abinda zan baki”
Tana iya jiyo muryar Fatin cikin dariya.
“Za ki kira ki bani labari....”
Daga haka suka tattauna a kan shirin da suke, kafin ta sauƙe wayar, ta ƙarasa jikin side drawer ta buɗe, ta ɗauko maganin da Fatin ta aiko mata. Ta yi murmushi a fili, sannan ta furta.
“Yau zan ga ƙarshen ƙauna!....”.
MISHAL POV.
Tsaye take a kitchen ɗin gidansu tana dafa noodles, sanye take da baƙar skirt ɗinta ta uniform, sai farar long sleeve oxford shirt ɗin da take sakawa a ƙasan suit ɗin uniform ɗin, sai dai babu suit ɗin. Kanta parker cikin ponytail, jelar na reto a gadon bayanta.
Sallamar Hajjara ce ta sa ta juyo ta kalli bakin ƙofa, a zuciyarta kawai ta amsa sallamar, sannan ta ɗauke kanta ta ci gaba da aikinta.
Hajjara ta yi murmushi, ta ƙaraso cikin kitchen ɗin, ta yi birki a gefen Mishal. Sai da gaban Mishal ya faɗi, sannan ta ɗago da kanta ta juya ta kalleta.
Dan ta fita tsayi, da ma girman jikin ne da ita kawai, ba ta cika tsayi ba. Murmushin da ta ga kwance a fuskar Hajjaran ne ya ƙara tsoro tata, duk da ita ba gwanar tsoron ba ce.
Kuma kafin ta yi wani tunanin, Hajjara ta kai hannayenta ta kamo na Mishal dake riƙe da spoon. Da sauri Mishal ɗin ta janye hannayenta tana zaro ido.
Dole ma da wani abun da wannan matar ta shirya, ta daɗe da sanin cewa ba santa take ba, dan ba iyaka jiya ne ta taɓa tada mata da ciwonta ba.
Tana yawan ja mata matsololi da dama, bata santa!, haka take yawan faɗa mata, to me zai sa yanzu tazo tana mata murmushi.
Dakewa ta yi, dan bata san ta ga rauninta, bata san ta gane cewa ta ji tsoronta.
Hannunta ta kai ta kashe gas ɗin, sannan ta ɗauke ƙaramar tukunyar da ta ɗora noodles ɗin, ta juyeta a cikin lunchbox ɗinta ta fice ta bar mata kitchen ɗin, in yaso duk masifar da take ji da ita ta ƙare a kanta, ta ci kanta ta sha baƙin ruwa.
A parlo ta iske Mama Ladi na bawa Daala abinci. Ta yi murmushi tana aje lunchbox ɗinta a kan coffee table. Sannan ta zaga ya zuwa kan sofa, ta ɗauki suit ɗinta a inda ta ajeta, ta saka a jikinta.
“Mama ni zan wuce, ga Baba Ali nan ya zo”
Ta faɗa yayin da take gyara zaman hairband ɗin dake kanta, bayan ta ji horn ɗin motar Baba Alin.
“To a dawo lafiya, banda rashin ji”
Ta yi murmushi tana ɗaukar jakarta, tare da saɓata a bayanta. A dai-dai lokacin Abubakar da Hammad suka sauƙo a tare.
Tana kallonsu har suka ƙaraso cikin falon, ciki-ciki ta gaisheda Abubakar, dan ba wani sosai suke shiri da ita ba, saboda faɗan da yake mata.
“Yaya, gap ɗin nan ya haɗe, yaushe za mu je kasa a cire min braces ɗin nan?”
Abubakar ya miƙe tsaye, kuma ba tare da ya kalleta ba yace.
“Sai mun dawo daga meduguri....”
“Wallahi da gaske nake Aky, ta haɗe fa, idan baka yarda ba zaka iya gan!.....”
“Ya isheni haka! Ke dole ne duk abinda kike so sai an miki ?!, To ba zan kai ki a cire braces ɗin ba!”
Cikin tsawa da ƙaraji yake maganar, ya ma manta waye gabansa, dan haka kawai yake ganin baƙinta yau, maganarta ma baya san ji.
Mama Ladi ta miƙe tsaye mamaki na cinyeta, tasan ba yau ya saba mata faɗa ba, amma kuma ba ya mata cikin masifa haka, kuma ba ya mata faɗa sai ta yi laifi, amma ita a cikin wannan maganar da ta yi bata ga abun lafi ba.
Ba ƙaramar tsorata Mishal ta yi ba, ta ji ƙofofin numfashinta na neman ɗaukewa, amma duk da haka ta daure ta shiga baza idanunta a falon. Tsaye a bakin kitchen ta ga Hajjara na wani irin murmushi me kama da na mugunta.
Dama ita tasan za'a rina, shi yasa sam bata yarda da matar wan nata ba, dan ko abincinta bata ci, ita da kanta take girka abincinta.
“Ka yi haƙuri Aky!...”
Da ƙyar ta furta hakan, muryarta a shaƙe, dan bata san numfashinta ya ɗauke.
“Baki da magana da ta wuce hakan ai, ke kullum cikin aikata laifi, yau kina wannan gobe kina wancan, ni kenan kullum cikin sintiri a hanyar makarantar ku!, Kin girma amma baki san kin girma ba, saboda Allah yanzu yarinya kamar ke ace bata san ciwon kanta ba?, to bari ki ji na faɗa miki idan har baki kama kanki ba, wallahi sai na saɓa miki!”
Har yanzu cikin ƙaraji yake maganar, yayin da Mishal ta runtse idonta tana kawar da kanta gefe, duk da isashiyyar iskar dake falon ita sam bata iya jinta a huhunta, sam bata jin wata iska na kai mata inda ya dace.
“Haba Abbakar? Ya haka dan Allah?”
Mama ta faɗi cikin tausasawa.
Abubakar na maida numfashi kamar wanda ya yi gasar tsere ya kalleta. Kafin a fusace ya fice daga falon.
Hajjara ta ji kamar ta zuba ruwa a ƙasa ta sha, duk ƙaunar duniya sai a ce Mishal, komai Mishal komai Mishal, hatta da makarantar da take ta fi ta Hammad tsada, kuma har mota ya siya mata tare da ɗaukar mata driver, bayan ita nata ɗan a school bus yake tafiya. Koma dai miye yau ranta ya yi fari tunda har ya mata faɗa. Ta kaɗe gefen rigarta ta yi sama, dan taje ta bawa Fati labari.
“Zauna Mishal...”
Mama ta faɗi tana zaunar da ita, tare da sauƙewa jakar bayanta, ta ciro littafi a ciki ta shiga mata fiffita. Kafin ta samu ta dawo hayyacinta.
“Kin sha maganinki ?”
Kai ta gyaɗa mata tana miƙewa, ba tare da tace mata komai ba, ta ɗauki jakarta haɗi da lunchbox ɗinta ta fita.
Mama ta bi bayanta da kallo, zuciyarta cike da tausayin yarinyar.
“Allah ka kawo mata sauyin rayuwa!....”
Wata ƙila ta faɗa a bakin 'yan amin, wata ƙila Allah ya zaɓeta ne dan ta zamo silar yin addu'ar wani abu dake shirin faruwa kwanaki masu zuwa.
Addu'ar tata, ita ce ta zama silar faruwar wata ƙaddara da Allah ya hukunta faruwarta a 'yan kwanaki masu zuwa. Wata iriyar ƙaddara da zata tarwatsa komai, sannan ta zama silar shiryuwar wasu lamura.
*Brickhall School, Kaura district, Abuja*
*09:40am*
RABI'A POV.
“Gashi, driverna na bawa saƙo ya siyo min, kuma ya ce ya nema amma bai samo irin wannan ɗayan ba, sai ɗan kwali ya samo...”
Cewar Mishal, yayin da take miƙa mata lalle ɗan kwali.
Rabi'a ta sa hannu ta karɓa. Tsaye  suke a bayan ajujuwan makarantar, a ƙofar store, inda ake aje kayan share-share na makarantar.
Rab'a ta juya ta kalli dama da hagun inda suke tsaye.
“A ina zamu yi kenan ?”
“Ga kujeru a can, muje mu zauna”
Kuma da ga haka, suka ƙarasa inda kujerun suke, suka zauna, sannan Rabi ta shiga haɗa lallen. Yayin da Mishal ke dudduba jakarta, a ciki ta ɗauko biscuits, ta buɗe ta shiga ci. Cike da mamaki Rabi'a ta kalleta.
“Bakya azumi ne ?”
Mishal ta yi murmushi, har karafunan braces ɗin da aka sa mata suna bayyana.
“Wahala ce ba zan iya ba, ga zuwa makaranta ga azumi, inaaa!”
Rabi'a ta yi dariya, a kamaninta idan ka ganta sai ka ce tana da wasu shekaru masu yawa,amma da zarar ka yi magana da ita ko na minti uku ne za ka fahimci yarintarta ƙarara.
“Shekarunki nawa ?”
Mishal ta dakata da taunar biscuits ɗin dake bakinta, ta ɗan ɗaga olive green colour eyes ɗinta, tana san ta tuna shekarun nata. Kafin ta sauƙe su a kan Rabi'a dake ɗaure ledar lallen da ta gama haɗawa.
“I’m 17, next year zan cika 18....”
Rabi ta ɗage girarta cikin murmushi tana kallon lallen da ta gama ɗurewa.
“Ki ce babbar yarinya ce...”
Mishal ta yi dariya, wani abu da ba kasafai ta cika yinsa ba.
“Ke fa shekarun ki nawa ?”
“Ki ƙara biyu a kan naki”
“Sha tara ?”
Rabi'a ta gyaɗa mata kai. Ganin ta gama haɗa lallen yasa Mishal maida sauran biscuits ɗinta cikin jaka, tana karkaɗe hannunta, tare da taune sauran wanda ke bakinta.
Ta miƙawa Rabi'a hannunta na dama, sannan Rabi'a ta fara zana mata lallen.
“Wow!, Amma fa ta yi kyau”
Mishal ta faɗi a karo na barkatai, sanda aka gama zanen lallen, ta ɗaga hannayenta sama yafi sau a ƙirga, sai kallon lallen take tana sakewa. Ba za ta ce when last rabonta da ba.
“Nawa ne kuɗin lallen ?”
Sai ta ga Rabi'a ta haɗe rai.
“Shekaru nawa na baki ?”
“Biyu”
Ta masa tana mamakin abinda ya haɗa tambayar da ta mata da kuma wannan batun.
”Kinga kenan ni yayarki ce, kuma ina matsayin yayarki ai bazan karɓi kuɗin lallenki ba...”
“Yanzu mun zama 'yan uwa kenan ?”
Rabi'a ta gyaɗa mata kai tana murmushi.
“Adawiyya ?”
Zuciyar Rabi'a ta dunguwar a lokaci guda, Adawiyya?!, kaf duniyar nan mutane biyu ne ke kiranta da sunan, Ummanta, da kuma yayarta Baby!.
*Unguwar Madallah, Suleja, Niger state*
*05:30pm*
“Wai har sun muku hutun?”
Cewar Saratu, yayin da takewa Rabi ƙananun kalba.
“An musu dai”
Rabi ta bata amsa. Suna zaune ne a ƙofar ɗakinsu, bayan Rabi'an ta dawo daga wurin aikinta ne ta share gidan tas, duk da wahalar rana da kuma aikin da ta je ta yi, ga kuma azumin dake bakinta.
Amma haka ta share gudan tas, kuma bayan ta gama ta ɗora da wanke-wanke. A lokacin Saratun tace mata ta zo su fara kalbar, tun da ta riga ta tsefe.
“Ai har ke, tun da de ba za ki je makarantar ba har sai an koma”
Rabi dai bata sake cewa komai ba, dan tun da ta ambaci kalmar 'makaranta', tunaninta ya tafi ɗazu, ta shiga tuna abinda ya faru tsakaninta da sabuwar ƙanwarta a ɗazun.
“Jibi za mu tafi garinmu, a can za mu yi bikin sallah”
Muryar Mishal ɗin ta katseta a ɗazun. Sai kawai ta yi murmushi.
“Ina ne garin ku ?”
“Maiduguri”
Mishal ta bata amsa tana firfita lallen hannunta da iskar bakinta. Rabi'a ta gyaɗa kanta. Tana ƙara tabbatarwa da kanta hasashen da take a kan Mishal ɗin, na kasancewarta shuwa arab.
“Shikenan, na san zuwa yanzu an koma break, bari naje na share inda aka ɓata, ki kula da kanki, Allah ya dawo da ku lafiya, sannan ki gaida Mamanki idan kin koma gida”
Ta faɗi tana ƙoƙarin tashi, amma maganar Mishal ɗin ta gaba ita ce ta hanata tashin.
“Mamata bata raye, kuma tun a sanda zata haifeni ta rasu, ban san babana ba ma, lokacin da cikina ya rasu, tare da yayana kawai na taso.....”
Rabi'a ba za ta iya cewa ga abinda take tunanin ba a lokacin, tasan dai kawai ta tsirawa ƙaramar yarinyar ido ne, tana nazarin ya akayi ta rayu tsawon shekarunta babu iyaye. Ita da ta rasa iyaka mahaifiya ma kawai rayuwarta ta hargitse bare ita da ta rasa duka biyun.
Kuma bama wannan ba, ba ma ta sansu ba, bata taɓa ganin ko ɗaya daga cikinsu ba.
“Ke Rabi? Tashi ki zo ki soya mana doyar nan!”
Muryar Habiba ta dawo da ita zahiri, a hankali dubanta ya kai kan Habiban dake tsaye a kansu.
“Umma ki bari mana na ƙarasa mata, saura guda biyu fa....”
“Ban yi niyya ba, yanzu nake so ta tashi ta min aiki na....”
Ba tare da Rabi'a tace komai ba, ta shiga ƙoƙarin jan doguwar kalbar dake riƙe a hannun Saratu dan ta miƙe, amma sai Saratun ta mayar da ita ta zaunar.
“Gaskiya Umma ba kya kautawa, Wallahi wannan ba adalci ba ne, yarinyar nan ta je ta yini tana aikin bautar da ba ita take cin kuɗinta ba, dan ke take kawowa, sannan ta dawo ta yi aikin gidan nan, kuma yanzu ta samu ana ɗan mata kalbar da za ta yi adon salla sai ki ce baza'a mata ba ?!”
Habiba ta ɗan sunkuyo tana miƙowa Saratu bayanta.
“Da ke ni mama Saratu, na ce inji didim!, sai na tabbatar da ranki ya ɓaci....”
Ta miƙe tana ci gaba da faɗin.
“Na taɓo uw*r ki Rabi ko?, To baki isa ba, dole sai ta tashi ta soya doyar nan!....”
Kafin Saratu ta sake cewa wani abu, Rabi ta yi wuf ta miƙe tsaye, tana ƙoƙarin ɗaure kanta da ɗankwali. Gashin kanta da tsayinsa ya ragu a yanzu ya kwanta luf a gadin bayanta, har yana reto.
“Gaskiya Umma na gaji!, Wallahi na gaji da abinda kikewa yarinyar nan a cikin gidan, ita ma fa 'ya ce, kuma ko baabaarta bata raye hakan ba ya nufin a cusguna mata. Umma kema uwar 'ya'ya mata ce, wata rana gidan wani za muje. Na tabbatar da idan uwar miji ko 'yan uwansa suka mana haka ba za ki ji daɗi ba. To ita ma kamar haka ne, tana da dangi bayan mu. Dan tsabar san zuciya irin naki yau shekarar yarinyar nan biyar a gidan nan, amma kin hanata ta je ta ga dangin mahaifiyarta, dan kar ta je ta faɗi irin azabar da ake bata a cikin gidan nan su hanata dawowa ki rasa baiwa. Wallahi Umma wannan ba adalci ba ne, ke ba kya tunanin wata ƙila wannan abun da kike shi ne ya zama sannadiyyar tagayyarar mu?, Ita 'yar taki ta fari, bata jin daɗin aurenta, sannan ni, shekaruna 27, amma na rasa mijin aure, ko sau ɗaya saurayi bai taɓa zuwa ƙofar gidanan yace yana sallama da ni ba, ga kuma Mama, wadda ta lalace da bin maza!.....”
“Ya ishe ni haka Saratu, ki rufa min baki ko na make ki a wurin!”
Saratu ta share guntuwar ƙwallar da ta zubo mata ta buɗe labulen ɗakinsu ta shige ciki.
Rabi'a da ke kiciniyar hura wuta ma ta share tata ƙwallar, saboda tunawa da ta yi da dangin Ummanta, ta tuna yanda suke matuƙarsanta da 'yar uwarta, sai kuma tunanin Anti Saratun, Allah ya sani kuma ita ma ta sani, ba ƙaramin cutuwa baiwar Allahn nan take  da zaman gidan.
Kuma ta san cewa Anti Saratun na matuƙar san aure, dan tasha kamata tana kuka, kan abun da ke damun rayuwarta, sai dai ta zauna ta bata baki har ta samu ta yi shiru.
*DSS Headquarter, Maitama Evenue, Abuja*
*10:30am*
KULIYA POV.
“Aliyu Zaid Bichi!”
Cewar shubansa, yayin da yake tsaye a gaban shugaban, ya ƙame cike da girmamawa.
Wani murmushi kwance a fuskar ogan. Kuma cikin abinda bai wuce sakan biyu ba, wannan murmushin ya sauya zuwa ɓacin rai ma bayyani.
“Kai wai me yasa ba zaka taɓa sauyawa ba?, yanzu saboda shashancin da ka yi, ɗaya daha cikin criminal ɗin ya mutu, kai kwata-kwata baka iya controlling fishinka ne ?!”
Kuliya ya ƙara ƙamewa yana kallon wani wurin da ban, dan da ma yasan hakan sai ta faru, ba ma yasan ya kalli fuskar ogan, dan idan har ya kalleta, zai iya hasaso kansa yana marin shugaban nasa, kuma wata ƙika ma hasashen ya zama gaskiya.
Dan baya san a ɗaga masa murya, daga an ɗaga masa murya yake kai hannu, shi kansa yasan cewa zuciyarsa a kusa da take, abu kaɗan ne ke tunzura shi. Ya ɗaga kafaɗarasa yana ci gaba da kallon wani hoto dake aje a bayan ogan nasa.
“A haka kake san zama kamar Lion ɗin ?...... Shi Lion ɗin da kake san zama sam ba haka yake ba, cikin basira da taka tsan-tsan yake gudanar da aikinsa, ba shi da saurin fusata kamar kai, ba shi da saurin kai hannu kamar kai!....”
Lion?!, wani suna guda ɗaya da yake ƙwarara masa gwiwa a kan aikinsa, wani sunan da ko jinsa ya yi sai ya ji jinin jikinsa na tafasa. Kuma ba shi kaɗai ne sunan Lion ke bawa ƙwarin gwiwa ba.
Kusan duka ma'aikatan DSS sun san sunan Lion, dan abu ne mayuwaci, ka je training ɗin DSS ba tare da an  baka maka tarihi da kuma sunan Lion ba.
Duk wani jarumi da mai hazaƙa a hukumar burinsa kawai ya zama kamar Lion. Sai dai kuma duk da wannan nasara da kuma jarumta irin ta Lion ɗin, in ka ɗauke manyan hukumar tasu, babu wanda yasan kammanin fuskarsa, sunan nasa kawai ake ji, sai kuma ƙwazon da yake a aikin nasa, sunan nasa ma ba na ainahin kowa ya sani ba. Code name ɗinsa kawai suka sani.
Amma duk da haka yana burge kowa, dan duk wanda zai gwada wata jarumta da kuma san nuna role model ɗinsa sunan Lion za ka ji ya kira.
“Sam shi Lion ɗin ba haka yake ba....”
Muryar Ogan nasa me amsa sunan Chidera Kingsly ta katse masa hanzari.
“Lion yana da basiri, he is so intelligent, amd smart, ya san aikinsa, baya komai cikin fushi, cikin nustuwa da tunani yake gudanar da aikinsa.....”
Kuliya ya sauƙe kansa ya ɗora manyan idanuwansa a kan fuskar shugaban nasa. Kuma har zuwa lokacin bai ce komai ba, dan tun bayan gaida shi da ya yi a sanda ya shigo office ɗin, bai ƙara cewa komai ba.
Kuma shima Chideran yasan cewa ba lalle ya sake cewa komai ɗin ba, dan kowa yasan miskilancin bawan Allahn nan.
“Na san cewa yanzu haka ka rayawa ranka cewar; ka dalle min fuskata da mari!”
Wani abu me kama da murmushi ya faru a cikin zuciyar Kuliya, dan ya canka dai-dai, hasasowa kansa yake yayin da yake kashe sauraye a kan fuskar chideran, dan ba sauro ɗaya ba.
*
“Ehemm!”
Muryar Kuliya ta yi gyaran murya, alamun ya bawa wanda yake buga ƙofar izinin shiga, dan wannan ɗabi'arsa ce. Kusan duk wanda yake headquarter ɗin yasan da hakan.
Shi a ganinsa magana ma wani kayan gabar ne, amma idan masifarsa ta tashi yafi ub*n kowa iya ɗaga murya.
Zaune yake a office ɗinsa, yayin da yake daddana system. Kamar kullum; sanye yake da baƙaƙen kaya, wata baƙar suit ce a jikinsa. Hatta da long sleeve oxford shirt ɗin dake ƙasan suit ɗin baƙa ce.
Ƙofar office ɗin ta iyo ciki, alamun dai wanda yake bayan ƙofar yana shirin shigowa. Suffar Abubakar ta bayyana a bayan ƙofar.
Kallo ɗaya Kuliya ya masa ya ɗauke kai, tare da ci gaba da danna laptop ɗin gabansa.
“Barka da safiya..... ni na gaida ka, tun da kai ba za ka iya ba gaisheni ba”
Abubakar ɗin ya faɗi yana ƙarasowa cikin office ɗin. har ya zauna a kujerar dake tsallaken teburin Kuliyan bai masa magana ba.
“Me yasa yau ka makara ?”
Muryar Kuliyan ta tambaya bayan wani lokaci, ba tare da ya kalli Abubakar ɗin ba. muryar tasa kamar da ga sama. Sannan amonta ya fito kamar kullum, cikin ɗaci da alamun ɓacin rai.
Dan shi kullum ba'a rasa abinda yake ɓata masa rai. Abubakar ya yi murmushi, to shi ya zai yi ne?, tun da Allah ya haɗa shi zama da mutane biyu masu murɗaɗɗen hali, tsakanin Kuliya da ƙanwarsa Misha!, Ya rasa wannene ya fi wani murɗewar hali.
“Ƙanwarka ce, ta yi rashin jin da ta saba a makaranta, sai da na biya ta can, sannan na ƙaraso nan”
Kuliya ya ɗaga kafaɗarsa ta dama. Shi duka-duka sau ɗaya ya taɓa ganin ƙanwar Abubakar ɗin, ba ma sosai yake iya tuna lokacin ba, dan shekarun da ɗan dama.
“Dama autopsy results ɗin nan na zo karɓa, Kamis yace yana wurin ka”
Ba tare da Kuliyan ya kalle shi ba, ya ɗaga kafaɗarasa ta dama, sannan ya buɗe wata loka dake jikin teburin nasa, ya ɗauko file ɗin,ya miƙa masa. Abubakar ya karɓa  yana miƙewa tsaye.
“Na tafi...”
Ko kallonsa Kuliya bai yi ba, bare ya bashi amsa, kuma shi ma yasan ba lalle ya kalle shin ba. Yasan halin Kuliyan sarai. Har faɗi yake da bakinsa cewa; idan ba Abubakar ɗin ba babu me iya zama da shi a matsayin aboki.
Dan kaf duniyar nan Abubakar ɗin ne kaɗai abokinsa, ba shi da wani aboki da ya wuce shi, sai Sharon da suke ɗan jitiwa, ita ma kuma ba kullum ba.
*Badawa layout, Kano....*
RAJA POV.
“Raja dan Allah, dan Allah!.....”
Cewar wani mutumi a galaɓaice, yayin da yake durƙeshe a gaban Rajan. Kuma bai ko gama rufe bakinsa ba, Rajan ya ƙara tsinduma kansa cikin bahon dake aje a gabansa, wanda yake cike taf da ruwa.
Haka mutumin ya yi ta motsi da kansa a cikin ruwan, saboda azabar da yake ji. Zaune yuke a harabar gidansa. Yayin da Rhoda da su Zuzu ke tsaye a bayansa.
Waɗanan lumssassun idanun nasa na kallon mutumin da kansa ke fancal-fancal cikin ruwan sanyin. wannan innocent face ɗin nasa fayau!, banu wani abu da za ka iya tsinta a cikinta. Kai ba ka ce mamallakinta ne ke wannan aikin ba.
Ƙarar ringing tone ne ya karaɗe wurin. A hankali Rhoda ta duba screen ɗin wayar 'Oga Garuje', shine abun da ta ga an rubuta, dan haka da sauri ta ƙarasa kusa da Raja.
“Garuje ne ya ke kira”
Bai kalleta ba, sai ma bindigarsa ƙirar pistol da ya ɗora a kan fuskar mutumin da ya tsamo kansa daga cikin ruwan. Sannan wannan kamillar muryar tasa ta furta.
“Me yasa ka ci amanar mu?”
A nitse muryar tasa ta fito, cikin wannan sautin nata mai nuna tsantsar innocent ɗinsa.
“Dan Allah Raja....Dan Allah...”
Ji kake Tas!!. Ƙarar bindiga ya karaɗe harabar gidan. Me gadin gidan ya yi saurin faɗawa ɗakinsa. Duk da yasan cewa abun ba zai komo kansa ba. Amma wai me hausawa suka ce ne?, idan ka ga gemun ɗan uwanka ya kama da wuta, to ka shafawa naka ruwa.
Raja ya yi wani murmushi me kama da dariya, a sanda ya ga shigewar me gadin nasa. Kafin ya saki gawar mutumin nan da ya harba a ka. Jini har ya ɓata masa hannu.
Ba tare da nuna damuwa ko wani tashin hankali ba, ya sunkuya ya wanke hannunsa cikin ruwan bahon nan.
Kuma har zuwa lokacin wayar tasa na riging a karo na barkatai.
“Ina ji”
Nutsatsiyar muryarsa ta faɗi,bayan ya amsa wayar, cikin wannan kamala da kamewar tasa, kai ba ka ce shi ne ya kashe rai yanzu ba.
“Raja!, Oga ne da kansa ya yi waya, ya ce ya na buƙatar ka je ka same shi a Abuja....”
Raja zai iya rantsewa kan zuciyarsa sai da ta buga sau biyu a lokaci guda. Kenan tsawon shekarun da ya kwashe yana wannan aikin sun kusa ƙarewa?. Shekaru sama da uku ma rayuwarsa ya kwashe yana bautar da bai san ranar ƙarewarta ba. Sai a yau ne komai ya ke gaɓa. Komai ya ɗauko hanyar ƙarewa. Ya kawo inda ya ke matuƙar burin kaiwa.
Sai dai a yanayin fuskarsa ba za ka tsinci hakan ba, dan miƙewa tsaye kawai ya yi, sannan ya juya yana kallon su Rhoda.
Da waɗanan lumsassun idanuwan nasa, ƙwayar idon wadda ta kasan ce gray color tana kallon yanda su Zuzu ke magana ƙasa-ƙasa. Ya ɗaga kafaɗarsa ta dama, sannan ya ce.
“Yaushe kenan ?”
“Ko zuwa nan da sati ɗaya ne, dan da alama ka koma can da zama, ka ga kenan sai an nema muku gidan da zaku zauna, da dai sauran su...”
“Na fahimta!”
Kuma da ga haka ya tsinke wayar.
“Alandi, Zuzu, ku fita da gawar nan da ga gidan....”
“An gama Oga Raja!”
Suka faɗi suna yin wurin da gawar ke yashe.
Sannan shi kuma ya yi hanyar shiga cikin gidan, da hannu ya yiwa Rhoda alamu da ta biyo shi.
“Rhoda, mun kai ga gaci....”
Wannan salihar muryar ta faɗi a sanda suke zaune a falon gidan.
”Me ya faru?”
Rhoda ta tambaya.
“Alhaji Bala ne da kansa ya ce na je na same shi a Abuja”
Cike da mamaki, murna da kuma farin ciki take kallonsa.
“Kenan mun kusa zuwa ƙarshe?”
Ya ɗaga kafaɗarsa ta dama, sannan ya ce.
“Kusan zan iya cewa hakan”
“Kai amma fa na yi farin ciki...”
Ta faɗi da iyakar gaskiyarta, dan ta yi farin cikin, tana ganin kamar komai ya kusa ƙarewa, kamar an gama komai, kamar wannan wahalar da suka sha tsawon shekaru ta ƙare.
Kuma ba ita kaɗai ke wannan tunanin ba, shi ma kansa Rajan haka yake tunanin sun kammalla komai, komai ya zo gangara, gangarar da zata gangaro da ƙarshen wahalar da suka sha tsawon shekaru.....
Sai dai abinda bai sani ba shi ne; yanzu ne ma komai ya fara, a yanzu LABARIN zai soma, sai a yanzu ne babin ƙaddarar tasa zai buɗe.
Wani sabon babi fil!, wanda babu ɗigo ko ɗaya a ciki, sai na wanda ubangiji zai hukunta. Saboda wata ƙaddara da ke shirin faruwa 'yan kwanaki masu zuwa. Ƙaddarar da zata tarwatsa komai, ta kuma gyara wasu lamuran.
A dai-dai lokacin ƙofar falon ta buɗe, Jagwado ne ya shigo, dan da ma banda shi aka tafi yasar da gawar.
Lighter ce riƙe a hannunsa yana ƙyasta ta, yayin da sigari ke maƙale a bakin. A sa'ar da Raja ya ɗora idonsa a kan wutar, a lokacin ne kuma wannan tsoron ya shige shi, tsoron wuta da Allah ya saka masa tun bayan abinda ya faru da shi.
Baya san ganin wuta sam, domin wuta na ɗaya daga cikin abin da ta zama silar rabuwarsa da mutane uku da suka fi soyiwa a ransa. Da farko ta raba shi da mahaifiyarsa, sai kuma ta zo ta raba shi da ƙaninsa, ɗan uwansa abokin tagwaitakarsa. Sai ku ma Maman Rhoda, wata mace da ta taka rawa mai makuƙar muhimanci a cikin rayuwarsa.
Wani irin wahallallen nunfashi ya ja, ya samu kansa cikin irin yanayin da ya saba shiga a duk sanda zai ga wutar. Duk da yanda yake ta kokawa da tunaninsa kan kada ya koma baya, amma sai hakan ya ci tura. LABARINSA na baya ya soma kunno kai cikin nazarinsa.
_“Zaid, ku tafi, kada ku tsaya a nan.....idan kuka tsaya wutar za ya iya ƙona ku....ku tafi na ce!.....” _
Amon wannan sautin nata ya shiga maimaita kansa a cikin tunaninsa, falon ya shiga rikiɗewa yana komawa gidansu, gidan da suka rayu a ciki, gidan da suka ci gaba da kwana a cikinsa har bayan sanda wuta ta gama ɗaita shi, wannan gidan da suka gina yarintarsu shi da ƙaninsa a ciki.
Sannan hoton ya sauya a idonsa, ya na ganin yanda take watso musu kayansu ta window, yayin da ƙofar falon take a kulle, ta kasa fitowa bare ta buɗe ƙofar har ta samu damar tsira.
Sannan ya kallin kansa da ma ƙaninsa Aliyu dake ta kuka, ƙaninsa me tsantsar kama da shi, dan idan suka kalli juna sai ka ce kansu suke kallo a madubi.
Dan kammanin da suke ya ɓaci, tsayinsu ɗaya, farar fatarsu ɗaya, girman idonsu ɗaya, komai na hallitarsu ɗaya ne, in ka ɗauke ƙwayar idon Zaid da ta kasance ash, sai kuma totsiyar karen dake haƙorin Zaid ɗin. Amma hatta wata ɗabi'a ta ɗaga kafaɗa dukaninsu suna yi.
“Jagwado menene haka ?, Sarai ka sani cewar Raja ba ya san ganin wuta!”
Muryar Rhoda da ke wa Jagwado faɗa ta dawo da shi zahiri.
Bai ƙara ce musu komai ba, ya miƙe tsaye, tare da ɗaga kafaɗarsa ta dama, ya yi ɗakinsa, yana jin yanda Rhodan ta balbale Jagwado da faɗa, shi kuma sai aikin bata haƙuri yake.
_________________
_To fa.... Bana kuma nan muka leƙo?_
_Na ce ba, wai Rajan ne ko Zaid ne?_
_Dan ni na kasa ganewa, kamar Zaid da Aliyu mutum ɗayane, kamar kuma....._
_Ko da yake, ba sai na faɗa ba ai😂_
#Labarinsu
#SalmaAhmadIsah
#Taurariwriters

LABARINSUWhere stories live. Discover now