HANGEN DALA ba shiga birni ba

By huguma

79K 7K 676

TSUMAGIYAR KAN HANYACE,KAMA DAGA MATAN AURE ZUWA 'YAMMATA More

BABI NA DAYA
BABI NA UKU
BABI NA HUDU
BABI NA BIYAR
BABI NA SHIDA
BABI NA BAKWAI
Babi na tara
BABI NA GOMA
Babi na Sha Daya
BABI NA SHA BIYU
BABI NA SHA UKU
BABI NA SHA HUDU
BABI NA SHA BIYAR
Babi Na Sha Shida
BABI NA SHA BAKWAI
BABI NA SHA TAKWAS
BABI NA SHA TARA
BABI NA ASHIRIN
BABI NA ASHIRIN DA DAYA
BABI NA ASHIRIN DA BIYU

BABI NA BIYU

3.5K 358 6
By huguma

👁️‍🗨️👁️‍🗨️ *HANGEN DALA* 👁️‍🗨️👁️‍🗨️
    _Ba shiga birni ba_

©️®️ *Safiyya Abdullahi Musa Huguma*

*BABI NA BIYU*

       Bakwai da rabi na dare bayan sun gama sallar isha'i,tana tsakiyar yaran suna aikin gida da aka basu a islamiyya,yaranta ne guda hudu,amir,ahmad,hanifa da rabi'a,sai yaran mmn ummi guda biyu mubarak da usman,wanda da can baya sai da aka kai ruwa rana kan donme mmn ummin zata dinga yiwa yaran aikin makaranta?,ko cewa akayi itadin bata iyaba ko bata da karatun,saida suka kai ruwa rana ita da baban amir kafin ta sauko ta haqura.

      Tana daga gefe tana kallonsu,hannunta daya saman cikinta wanda yafara nauyi,kadan kadan tunaninta na tafiya kan zuwan hafsat shekaran jiya gidan,wanda hakan yasake sawa mmn ummin takumsa sauyawa,har ita kanta tasake sauya mata,dan hadin kan da rabarta da take tasake janyewa,wanda ita ko kadan bai mata dadi ba,tasani cewa dole sai sun wanzar da zaman lafiya a tsakaninsu sannan koma wacece xata shigo daga baya itama tayi koyi dasu.

       Sallamar baban amir ita ta katse mata tunaninta,suka hada idanu sanda yaran ke rige rigen isa gareshi su rungumeshi gami dayi masa sannu da zuwa,ya qaraso dakin yanaji da sannu da zuwan yaran,tayi qoqarin qaqaro murmushi saman fuskarta tana masa sannu da zuwa,amsa mata yayi yana nazartarta,yanajin tausayi tausayinta yana kamashi,haliman taci sunanta qwarai shi kansa yasan da hakan,komai Allah shike tsarawa dan adam shi,auren maryam na cikin qaddararsa,haka rufaida da yakejin sonta cikin jikinsa,hakanan yana jin cewa tayi dai dai dashi ta kuma dace da ra'ayinsa,banda hakan babu abinda halima mmn amir tarasa,wanda daa a baya baisan da hakan ba,kafin ya auri maryam ganin gazawar haliman yake,gani yake kaman nata iya komai ba,akwai abubuwa da yawa da bata iya masashi wanda yake hasashen samunsa gurin wata macen,ashe Allah ya tsara masa auren maryam ne don ya fidda qima da darajat haliman a idanunsa,sai bayan ya auri maryma ne ya tabbatar haliman ba kayan banza bace,wannan dalili yasa yake matuqar ganin qimarta da qoqarin kyutata mata,gefe guda kuma yanajin kunya da nauyin abubuwan daya ringa aikata mata lokacin da idanunsa suka rufe yana neman auren maryam,wanda yayi imanin cikin kawaici da yakana ta halima haryau wani abun bata gayawa maryam shidin ya mata ba lokacin neman aurenta,sai gashi ayanxu yana samun sassauci da sauqi daga wajen haliman fiye da maryam,wadda ta bazawa idanunta kwalli,takuma shafawa fuskarta toka ta fitittike kamar basu taba wani abu soyayya ba kan auren da zai qara
"Sannu da zuww" haliman ta katse masa tunaninsa,ajiyar zuciya yasaki a boye
"Yauwa halima,kece da sannu,ya nauyin jikin?" Ya qarasa fada yana bude ledar daya shigo da tsarabar da yayiwa yaran nashi yasoma raba musu,murmushi kawai tasaki
"Alhmdlh" ta fada kawai a  taqaice,sai daya gama rabawa yaran duka tana zaune tana kallonsu sannan yacewa amir
"Jeka kiramin antynku,banji motsinta ba" aje kayan hannunsa yaron yayi yafita kiran kamar yadda ya umarceshi.

      Minti biyu amir din yadawo
"Abba,tace ba zata iya tasowa ba batajin dadi"
"Kace magana zanyi dasu,tazo injini" dakatar dasu mmn amir tayi
"A'ah,tunda bazata iya tasowa ba ka taddata can mana,yaukam batajin dadi sosai don tun daxun data gama aikima tana daki kwance" jim bban amir yayi,don yana tantamar hakan,don lokacin dayashigo tsakar gidan yana ganin sanda tashige dakinta abunta,ba tare data kula da sallamar da yakeyi ba,amma yasan mmn amir din taui hakane saboda akaucewa idanun yaran,saboda haka yace
"Shikenan,in zaki iya tasowa ki sameni a dakin nata" yafada yana miqewa yadauki manyan ledojin yafice.

        Sai data basu wasu mintuna sannan ta yunqura tamiqe tabi bayanshi
"Ai dama ko bakayi hakan ba nasani ba wani sona ko damuwa kayi dani ba,ta yaya ranar girkina zaka wani shige dakinta kuma ka aika wai naxo.....to wallahi bbn amir ni bazan dauki wannan ba,tun yanxu wallahi tallahi donma kasani" duk abinda take fada cikin kunnenta suka fada,amma sai tayi kaman batajiba tayi sallama tashiga,sallamar tata tasa bbn amir din bai maida mata amsa ba,saita samu waje tazauna tana yiwa mmn ummin sannu da jiki,zama yayi yasoma bude ledojin yafito dakayan ciki,yayin da take tsaye har yanzu taqi zama
"Gashinan,kayan fadar kishiyane,kowacce saita dauki leda daya" jiki a sanyaye mmn amir ta sa hannu tadauki leda daya tana cewa
"An gode,Allah ya amfana" tana daga tsaye tanajin kaman zata fashe da kuka,wani mugun kishi yana ratsata,wato dai da gaske yake bazai fasa din ba kenan,kai ta gyada cikin fada da bala'i tace
"Tabdijan,duk wani rashin adalcinka muraran yafito wallahi jibril,ka narkawa amarya kaya akwati akwati kalar wanda takeso,mu kuma shine zaka dubemu da wadan nan 'yan tsirarun kayan da basu wuce kala goma goma ba?" Ta fada tana nunasu cikin rainuwa,kai ya daga ya kalleta
"Ke kin manta kala nawa akayimiki?,shine yanzu yazama laifi don an yiwa wata?"
"Au hakama zakace?,wato bban amir gidan nan bau shegiya banza kamarni,to idan haka ne ita mmn amir daka yi mata kai daya da nawa,nan da wata uku kazo kasake mata na haihuwa taci tudu biyu kenan ni tudu daya?" Bacin ran baban amir yaqi boyuwa,cikin fada da hargagi yace
"Ke malama kin fara isata fa kin soma kaini bango,uwatace ke da dai abinda kika tsaramin zanyi?,don kinga ina daga miki qafa ina qyaleki?,to na rantse da Allah ki shiga hankalinki,banason hauka da iskanci kinji ko?" Da sauri mmn amir ta dakatar dashi
"Don Allah kayi a hankali yara zasu iya jiyowa,indai kaya ne ni saina qara mata a nawan tunda ni xakamin na haihuwa idan Allah yakaimu da rai da lafiya"
"Bata isaba wallahi saidai idan kada ta saka" ya fada yanajin nauyi da kunya da tuna sanda ya hana mmn amir din ko tsinke sanda zai auro maryam din da sunan kayan fadan kishiya,a sannan yace mata bashi da kudi,bayan ba haka bane ita kanta tasani amma ta qyaleshi bata sale daga maganar ba,sai kayan fitar sunan ahmad ta saka
"Lallai samu yafi iyawa" mmn amir din ta fada a ranta itama tana tuna lokaci irin haka da za'a kawo mata maryam din a matsayin kishiya,tunda harya riga daya rabtse gaka ta tattara kayan nata tafito tabar musu dakin,don ta tabbatar yau din Allah ne kadai yasan wainar da za'a toya tsakaninsu,tayi imani cewa da maryam ce uta a wancan lokacin da tuni tajima da barin gidan,cin kashin da yayi mata lokacin aurenta dashi a yanzu ko rabinsa baiyi ba,tayi imani Allah baya barci,kuma duk abinda kayi sai an maka mafiyinsa,gashi tun ba'aje ko ina ba tana dandana irin abinda ta dandana itama,ashe nata salama ne tunda ta iya haquri da mallakar kanta.

        _WASHEGARI_

  
        K'arfe shida na sassafiyar ranar maman amir na kwance saman gadonta,tun bayan data idar da sallar asuba bata koma ba,idanunta biyu sai azkar da takeyi wanda idan tagama saita sake dauko wani.

       Daga bakin uwar dakin nata taji sallamar ahmad,kamar yadda ta koyar musu shigo mata daki sai sun tsaya sunyi sallama tabasu izini,kai ta daga ta amsa masa sallamar sannan yashigo,ya gidata duk da qananun shekarunsa ta amsa
"Umma,mama batayi mana wankan ba,kuma lokacin makaranta yana qurewa" shuru tadanyi,al'adarsu shine duk wadda keda girki ita zatawa qananun wanka sannan tashirya musu abinci naci dana tafiya makaranta,tunda taga haka tasancewa lallai jiyan anyi bacin raine ita da baban amir
"Shikenan,bari na taso nayi muku,duba min kettle din idan da akwai ruwa kazo ka gayamin".

      Dai dai lokacin da yake duba kettle din abban nasu yashigo
"me kake anan?ina shirin makarantar taku?"
"Umma ce tace na duba ko akwai ruwa a ciki
" ba'ayi ma wankan ba kenan?"kai kawai yaron ya daga,sosai yaji ranshi yabaci,wato shi zata nunama iyakarshi kenan?,a fusace ya qarasa qofar dakin nata ya yaye labulen yashiga.

      Tana zaune gefan gadonta tana baiwa ummi nono,idanun nan a kumbure hakama fuskarta,gaba daya jin duniyar take ta juya mata baya,batajin dadin komai,kamar tafita tabar mishi gidan haka takeji,jiya kwana tayi kuka,har sanda mmn amir tafito ta daura alwalarta ta ka'ida takoma daki duk tana jinta.

      "Wadan nan yaran?,wa kika barwasu?,waye zai musu wanka?"wani kallo ta dago ta watsa masa
" oho,kaje ka kira wancan tantiriyar da zaka auro tayi musu,tunda mu bamu isar maka ba,kaga gwara mu zame hannuwanmu ita tazo tayi abinda mu muka kasa ko bamu dashi"yana sane yasaki murmushi
"Me kike ci na baka na zuba?,tana nan zuwa kuma zatayin,amma a yanzun dole ki tashi kiyi kafin nata lokacin" sosai maganar tashi tasake bata mata rai ta kuma dugunzumata,wato babu abinda zai fasa kenan gameda abinda ya niyyata,har yana ma mayar mata da magana,nan fa sa'insa ta kaure tsakaninsu,kowanne ranshi yabaci yasoma maidawa dan uwanshi da magana.

        Dai dai lokacin da mmn amir tafito tsakar gidan don hada kan yaran tayi musu wanka taji tashin muryoyinsu,gefe daya amir na tsaye fuskarsa cikin damuwa shida ahmad,kada yaran tayi dakinta sannan ta fada dakin mmn ummin
"Haba haba baban amir,bai kamata bafa,kuna abu kaman yara?,duk kunsa hankalin yara yayi kanku?,kiyi shuru mmn ummi mana haba"
"Kinga ba abinda yashafeki,ki qyaleni dashi wallahi,duk wani take takensa na gama ganeshi,tunda ke baki iya qwatarwa kanki 'yanci ki barni nina qwaci 'yancina"
"Don Allah kiyi shuru mmn ummi,haba mana"
"Qyaleta halima,barta tayi,dani take zancan na rantse da girman Allah,tunda aka tada zancan nan kin hana kowa hutawa?,saikace ke daya ce macw cikin gidan nan?,to kiyi duk haukar da zakiyi ki gama,aurene dai babu fashi sai nayishi"
"Ka fada duk abinda kakeso mana jibril,ai namiji kake,batulu,namiji ai dama hankaka ne,gabanka fari bayanka baqi,ka manta lokacin daka dinga daukarmin qawuran bayanni babu wata?,kamanta sanda kake neman aurena ido rufe kanason nashigo gidanka na haska maka shi na zamemaka fitila saboda gidan ya maka duhu acewarka a sannan?,shine zakayimin butulci a yanzu?"duk ya tuna,ya tuna komai,nauyi da kunyar mmn amir suka dabaibayeshi,gashi da alama mmn ummin tonon silili takeson masa,da sake tada husuma,tanasone ya rasa kwanciyar hankali da biyayyar da yake samu wajen haliman kenan?
"kinga maryam,tunda ke baki da mutunci,bakisan darajar mijinki ba to xama babu dole,ki tattara ya naki ya naki ki tafi,don bazan zauna kina haddasamin bala'i da masifa ba tun yanzu"
"Ashasha,haba baban amir haba?,wannan ma aiba zance bane" inji mmn amir duk ranta a jagule,baiko sauraretaba yafice abinsa,don tabarmar kunya yakeso ya nade dama da hauka kada ya baro wani zance daya shafi tsakaninsa da mmn amir din.

        Kuka sosai mmn ummin take,ta nemi gefan kujera taxauna tana ci gaba da kukanta,amir ta qwalawa kira tace yayiwa 'yan uwan nasa wanka,ya saka musu unifoarm tan nan fitowa,sannan ta sake maida hankalinta ga mmn ummi
"Kinga irinta ko?,kinga irin abinda nake gaya miki,akan wata can a waje da batama kai ga shigowa ba har yanzu zaki girgide aurenki,ki fita kibar yaranki wanda baki da yaqini ko tabbacin yadda rayuwarsu zata kasance,yanzu wa gari ya waya?" Itadai batace komai ba sai kuka da take faman sheqa,mamaki duk ya cikata tana tuna soyayyar da suka zuba ita da baban amir,ko a mafarki bata taba tsammatar irin haka zata faru ba,shuru ya ratsa dakin kafin mmn amir tamiqe tana cewa
"Ba inda zaki,ina zuwa" ta juya tafice daga dakin da niyyar baiwa baban amir baki,saidai koda taje dakin nashi bainan,ahmad ya gaya mata yafita,saboda haka ta sauya akalar tata zuwa dakin girki ta dorawa yaran ruwan tea,tanayi tana tunani cikin ranta.

       ******************

"Haba don Allah dear,nifa banason ka dinga bata ranka a banza a wofi,yanzu kamar kai ace kana teburin me shayi wannan ai zubarmin da mutunci kawai kayi" jim tayi ma wasu mintina sannan tace
"Aini wallahi banga wani abu da xakayimin da har zai kaimu ga haka bama,nidai don Allah ka koma gida koka qaraso nan gidam anty luba na hada maka break,tunda su duka basu damu dakai ba nina damu dakai" sake shuru tayi kafin daga bisani tace
"Toh shikenan,i love you" daga haka ta aje wayar tana murmushi
"Uhmmm,rufaida kenan,ke naga ko a jikinki ma,da aketa jiye miki shiga tsakiyar mata biyu" dariya tasaki kafin ta tabe baki
"Mata biyu ko muna mata,nifa wallahi anty ko a jikina,wadan nan niban daukesu a bakin komai ba,kada madai uwar gidan nan tashi taji labari,wadda ko isasheshen ilim boko bata da,yadda kikasan matar ladar noma,gwara gwara ma ta biyun itace kawai nakega tafi fada a wajensa fiye data farkon,haba anty,me zanji,kamata?,nida nake da karatu har matakin degree dame zasu tsoratani?,wancan mai kwalin diploma din ko dayar da banda kwalin secondry bata da komai?,wucenan wallahi"
"K'nnnn,to ai shikenan,yanzu yaushe zaki shiga kasuwar?" Dan shuru tayi sannan tace
"Ina tunanin anjima kadan,don akwai wasu magunguna da zan siyo wanda yakamata ace nashasu tun last week amma ban samesu ba,to tayimin waya ta kawo nazo na amsa" baki anty luba ta kama tana dariya
"Lallai rufaida,kurman tanadi kawai akewa auren nan" fari tayi da idanu cikin jin dadi
"Kedai bari kawai anty,burina kawai nazama tafisu,duk da yanzun ma nasan tafisu dince" dariya tayi ta juya tafice tana cewa
"Idan kin tashi tafiyar kimin magana inada saqo"
"Tohm" ta amsa mata tana maida kanta tasake gyara kwanciyarta,tanajin dadin yadda take juya jibril son ranta,kamar sitiyari a hannun driver ba tare da wata matsala ba,hakanan ba tare data nemi komai ta rasa ba.

Continue Reading

You'll Also Like

325K 23.4K 21
Fluff,BL,Short story. "အေး..အေးကွာ..ချစ်တယ်ကွာဘာဖြစ်လဲ။ မင်းကလူမိုက်..ငါကအုပ်ကြီး ဘယ်ကောင်က လှန်ရဲမှာလဲ။" အသုံးအနှုန်းအချို့အတွက် ၁၅ နှစ်အောက်ကလေးငယ...
168K 10.2K 47
ចន ជុងហ្គុក / គីម ថេយ៉ុង
609K 1.2K 28
နာမည်ကြီး သဘောကျခဲ့သော စာအုပ်များကို ပြန်တင်ပေးထားချင်းသာဖြစ်ပါသည်