SANGARTA COMPLETE

By ZulayheartRano89

120K 6.6K 88

labarin soyayya da ban tausayi More

part 1
BABI NA BIYU
BABI NA UKU
BABI NA HUDU
BABI NA BIYAR
BABI NA SHIDA
BABI NA TAKWAS
BABI NA TARA
BABI NA GOMA
BABI NA SHA DAYA
BABI NA SHA BIYU
BABI NA SHA UKU
BABI NA SHA HUDU
BABI NA SHA BIYAR
BABI NA SHA SHIDA
BABI NA SHA BAKWAI
BABI NA SHA TAKWAS
BABI NA SHA TARA
BABI NA ASHIRIN
BABI NA ASHIRIN DA DAYA
BABI NA ASHIRIN DA BIYU
BABI NA ASHIRIN DA UKU
BABI NA ASHIRIN DA HUDU
BABI NA ASHIRIN DA BIYAR
ASHIRIN DA SHIDA
ASHIRIN DA BAKWAI
ASHIRIN DA TAKWAS
ASHIRIN DA TARA
TALATIN 30
TALATIN DA DAYA
TALATIN DA BIYU
TALATIN DA UKU
TALATIN DA HUDU
TALATIN DA BIYAR
TALATIN DA SHIDA
TALATIN DA BAKWAI
TALATIN DA TARA
TALATIN DA TARA
ARBA'IN
ARBA'IN DA DAYA
ARBA'IN DA BIYU
ARBA'IN DA UKU
ARBA'IN DA HUDU
ARBA'IN DA BIYAR
ARBA'IN DA SHIDA
ARBA'IN DA BAKWAI
ARBA'IN DA TAKWAS
ARBA'IN DA TARA
HAMSIN
Complete

BABI NA BAKWAI

2.5K 134 1
By ZulayheartRano89


SANGARTA

©
ZULAYHEART RANO

7

Nanne ɗan murmushi ta saki, tana mamakin yadda maigidan nata yake farincikin sanar mata da maganar, ita ma nan take ta ji ta ƙosa ya sanar mata zaɓin da aka yi wa Asmad ɗinta.

"Aneesa na masa zaɓi, don nasan ita ce kaɗai zata iya zama da shi cikin mutunci."

Kara gyara zama Nanne ta yi, da jin zaɓin da aka yi wa Asmad, wani kyakkyawan murmushi ta saki, wannan shi ne burin da ta jima da shi a ranta, sai dai ta yi shiru ne don kar ta shiga haƙƙinsu, sai ga shi mijinta mai dogon tunani, shi ma ya yi irin nata nazarin."

Murmushi ta kuma sakewa a karo na biyu, wannan karon bakinta yaƙi rufuwa, cikin jin daɗi ta ce

"Allah Ya sa Albarka cikin wannan haɗin, Ubangiji Ya kaɗe fitina, Allah Ya ba su zama lafiya da zuri'a tagari."

"Allahumma amin, Hajiyar Asmad ga dukkan alamun dai wannan maganar ta yau ta yi maki daɗi?"

"Sosai kuwa Alhaji, ai wannan abin farin ciki ne, zumuncin mu da Hamma Bashir zai ƙara ƙarfi, lallai na ji daɗin hakan Allah Ya tabbatar da Alhairinsa."

Haka suka ci gaba da hiransu, cikin jin daɗi.

*************************

Ameesha ce zaune cikin falon su, waya ce a hannunta da alama game take yi ko chat, Haidar ne wato Yayanta wanda take bi mawa ya shigo falon da sallama.

Ta yi saurin ɗago da kai ta ce

"Yawwa Ya Haidar, wallahi tun ɗazun zaman jiranka nake."

Harara ya banka mata cikin ɗaure fuska, Allah Ya yo Haidar da iya haɗa fuska, baya ƙaunar raini ko kaɗan, ballantana kuma Ameesha da take da rawan kai.
"Kai Ya Haidar daga magana sai ka soma min harara to na fasa."

Zama ya yi yana faɗin
"Kin yi wa kanki, tashi ki kawo min abinci."

"Kai don Allah ni fa game nake yi, kuma ina tashi zasu cinye ni."

A shagwabe Ameesha ta ƙarasa maganar.

"Ba zaki tashi ba kenan?"

Ganin mugun kallon da yake watsa mata yasa ta miƙe, komai sai da ta haɗo masa sannan ta aje masa a gaba, komawa ta yi kan kujera ta lafe, cike da jin takaicin yadda Haidar ɗin ya mata.

" Yawwa ƙanwata kin san mene ne? Zo ki ji?"

Haidar ne ya yi maganar, wannan karon fuskarsa a sake take, kamar ba shi ba.

Banza ta masa tare da ci gaba da buga game ɗin.

"Meesha my lovely sister zo ki ji please? "

Kallon inda yake ta yi tare da turo ƙaramin bakinta ta ce

"Ba yanzu ka gama min masifa ba, kuma kaƙi tsayawa ka ji abin da zan ce."

"Oh! Sorry my sister, faɗi in ji mai kike so? "

Murmushi ta saki ta ce

"Dama so nake in ce maka laptop ɗina ya lalace, ji ya da zan dawo daga school."

"Yanzu ya kike son a yi?"

"Abba nake jira ya dawo, sai in amshi kudi sai ka sayo min sabo, tunda wancen ya tashi aiki."

"Je ki ɗauko in gani." Ya yi maganar yana aje plet ɗin.

Ta miƙe da zumar tafiya, sai ta ji sallama a ƙofar falo, amsawa ta yi tare da tambayar "Waye? Daidai lokacin ta isa ƙofar.

Ganin mai bawa fulawar gidan ruwa yasa ta ce

"Lafiya kuwa?"

"Lafiya lau Hajiya dama baƙone ya ce a kira ki."

"Baƙo?"

Ta yi tambayar tana kallon wanda ke tsaye gabanta.

"Eh Hajiya."

"To ina zuwa."

Shi ne iyakar abin da Ameesha ta faɗa, mamaki sosai ya rufeta, ita ai bata yi magana da wani akan ya zo gidan su ba 'To waye wannan?' Ta yi wa kanta tambayar da babu amsa.

Bedroom ɗin Ummiee ta nufa, don ko takan Haidar bata yi ba, akan sallaya ta samu Ummiee, zama ta yi gabanta tare da riƙo hannunta ta ce

"Ummi kin ji wai wani ya zo nema na?"

Shafa Addu'ar Ummiee ta yi ta ce "To ya baki tafi ba?”

"To ni ai Ummi ban san shi ba, kuma ai da na san da zuwan shi zai kira wayata."

Ameesha ta yi maganar ranta a ɗan ba ce.

"Haba Ummin Abba ba'a haka, tashi ki ɗauko hijab ki, ki je kiga ko waye daga nan ki haɗa masa abin sha kin ji ko?"

Ɗaga kai Meesha ta yi, badon ranta ya so ba, amma tunda Ummiee ta bata dama bari ta je, ji take kamar ba ita ba, tunda take bata taɓa zuwa harabar gidan su da suna nan tsayuwa da wani ba.

Amma yau gashi wani ya tako har gidansu, tana jinjinawa ko waye wannan da ƙoƙari. Ko ruwa bata ɗauka ba, ta nufi wajen dama jikinta fes yake, fuskar ta shafe yake da powder.

Cikin nutsuwa ta ke tafiyar, jikinta ko'ina iska ke kaɗa ta, tun daga nesa ta soma shaƙar daddar turarensa, tsaye yake ya jingina bayan sa jikin motar, waya ce a hannunsa da alama waya yake, can nesa da shi ta tsaya, tana kallon sa.

Bai san ta iso ba har sai da ya ji ƙamshin turarenta ya cika wajen, a hankali cikin nutsuwa ya juyo da fuskar sa zuwa gareta, fuskar nan tashi ɗauke da murmushi

"Barka da zuwa Gimbiya sarautar mata."

Shi ne abin da ya faɗa, yana kallon Ameesha, ɗan taɓe baki ta yi cikin jin kai ta ce

"Bawan Allah ban gane ka ba, daga ina kuma wajen wa ka zo? "

Murmushin dai ya kuma yi ya ce

"Haba Ameesha baki dai gane ni ba, da farko dai sunana *Najeeb Mansur* ɗan Alhaji Mansur abokin Abban ki."

Zaro ido ta yi cike da mamaki ta ce

"oh! Sannu da zuwa Ya Najeeb ya Alhaji da Momi? "

Ameesha ta tambaya fuskar ta ba yabo ba fallasa.

"Lafiya lau Ameesha, na san zaki yi mamakin gani na a gidanku ko? To wannan ba'a bin mamaki ba ne domin kuwa mai son ɗan tsuntsu shi ke binsa da jifa, gaskiyar magana dai na zo maki da wata magana ne mai muhimmanci, sai dai tunda baki san da zuwa na ba, ina son ki ba ni lokacin da zan dawo mu tattauna."

Kallon sa take tunda ya soma magana, Najeeb dai kyakkyawa ne son kowa ƙin wanda ya rasa, da ganinsa kasan da nutsuwa a tattare da shi, sannan kalaman da ya yi amfani da su wajen yi mata magana sun yi mata daɗi. Amma sai ta basar ta ce

"No ni kam ba ni da wani time, don kullum ina school yau ma ka yi sa'a ne ka iskoni a gidan."

"Haba Princess Meesha ki taimaka, matuƙar baki ba ni dama na fayyace maki abin da ke raina ba, tom zan iya shiga wani hali, ki yi haƙuri ki ba ni dama domin Allah."

Da muryar tausayi ya ƙarasa maganar.

Yadda ya yi maganar har ya kusan bata dariya ya yi, amma sai tayi saurin fuskewa ta ce

"Kana iya dawowa nan da two weeks."

Zaro ido ya yi a ɗan firgice ya ce

" Haba Princess ina laifin two days, wallahi two weeks ya min yawa."

Ta gaji da jin maganar, tana son komawa cikin gida don haka ta ce

"To one week ya yi? Don ina da test a school, a cikin week ɗin nan."

"Allah Ya kai mu amma ba haka naso ba, sai dai kuma tunda Princess ce ta zaɓa ba ni da yadda zan yi."

Har ta kama hanya zata tafi ya ce

"Princess baki ba ni phone number ɗin ki ba please ki ba ni?”

Wayarsa ta amsa tasa masa numbers ɗinta sannan ta wuce. Shi kuma a nashi ɓangaren wani nannauyan ajiyar zuciya ya sauke, da ya gama da wannan, don yasan tunda ya samu number ɗinta ya yi mai wuya.

Maimakon ya yi farinciki da ya samu ta ɗan amince da shi, sai takaici ya rufe shi, don yasan abin da zai aikata ba abin kirki bane, tunda yaudara ce zai yi, takaici sosai da tausayin ta suka rufe shi.

A gefe ɗaya kuma yana yaba kyaunta da nutsuwarta, tabbas da a ce ba shi da Rufaida tofa zai iya aurenta, sai dai shi yanzu Rufaida kawai yake kallo a matsayin mace.

Ko da yake jan motar haka ya yi ta tunanin abin da zai aikata, Allah ya sani umurni zai cika ba yin kansa bane.

*********************************

Zama ya yi kusa da Nanne ya ce (o jod'i haa kombii Nanne! owi

"Nannena da alama yau dai kina tare da farinciki?" ("Nanne aam ko fe'i hande banta ad'on seyi? ")

"Sosai kuwa Asmad tunda burina ya kusa cika." ( "sosai mid'on seye gam heje aam badake hubugo Asmad." )

Dariya ya yi wanda ya kuma fito da asalin kyaun shi ya ce ( o jali ha wad'ega mako beddi wartugo dendenta owi)

"Nannena kenan, hala Saudiyya zaki kuma zuwa? " (" Nannena aam d'oo kaam makka na alorata? ")

"A'a ba Saudiyya ba ne mafarkina na son Asmad ɗina ya yi aure shi yake shirin tabbata." (' a'a na maka sam miyahata koid'ol aam on badake wartugo gonga Asmad aam badake bangugo. ")

"Kai Nannena yo ni da ko budurwa ba ni da ita kike maganar aure?" ("Kai Nanne aam min mowala ko berajo awolwinta hala banga?")

"Ai uba nagari tuni ya samar maka da mata 'yar kirki."( "ai dottijo gonga hebani maa debbo jabdubo")

"Nanne kina nufin Bobbo ya samar mini mata? Oh! Shet." ( "Tani wiaam bobbo aam subani aam debbo? Or toskiyam")

Asmad ya yi maganar cikin wani irin yanayi. (Asmad wi'ika der mettam beram)

"Eh ya zaɓar maka kuma mata yar kirki, wacce kai kanka zakayi Alfahari." (" E of subani Maa debbo kand'o bema to'o larima ko an alarima saito a mani moo")

Nanne ta yi maganar cikin kwantar da hankali. (Nanne wii banjin don wallina moo hakkilo.)

"Wacce mai sa'ar Bobbo ya zaɓa mata ni a matsayin mijinta na aure? " (" mard'o sa'a to be bobbo subani aam?")

"Aneesa!"

Nanne ta faɗa babu shamaki. (Nanne not moo)

Wani irin zabura Asmad ya yi bakin sa na rawa ya ce "What...?" (Asmad haftii hunduko mako don wama owi "d'ume..?")

Yar Mutan Rano

Continue Reading

You'll Also Like

812K 16.3K 112
Yaszy Romano has been through so much pain and suffering her entire life but it makes her who she is. Dark Angel...Dangerous, Powerful. An Assassin...
22.2K 699 29
the story takes place in Nevermore where Wednesday meet a tribrid that is Hope's twin sister who was misplaced at birth. her name is Faith Mikaelson...
14.3K 1.1K 32
This story is related to brother sister bond. Where brothers are strict yet loving and caring and sister is fully troublemaker and apple of her broth...
21.2K 662 28
Unicode α€„α€šα€Ία€€α€­α€―α€‘α€›α€™α€Ία€Έα€™α€―α€”α€Ία€Έα€α€¬α€•α€²α€œα€¬α€Έα€™α€™α€™α€―α€”α€Ία€Έ α€žα€²α€„α€šα€Ί α€„α€«α€·α€˜α€α€™α€Ύα€¬α€™α€„α€Ία€Έα€€α€­α€―α€‘α€™α€―α€”α€Ία€Έα€†α€―α€Άα€Έα€•α€² α€α€…α€Ία€žα€€α€Ία€œα€―α€Άα€Έα€™α€―α€”α€Ία€Έα€”...