SANGARTA COMPLETE

By ZulayheartRano89

120K 6.6K 88

labarin soyayya da ban tausayi More

part 1
BABI NA BIYU
BABI NA HUDU
BABI NA BIYAR
BABI NA SHIDA
BABI NA BAKWAI
BABI NA TAKWAS
BABI NA TARA
BABI NA GOMA
BABI NA SHA DAYA
BABI NA SHA BIYU
BABI NA SHA UKU
BABI NA SHA HUDU
BABI NA SHA BIYAR
BABI NA SHA SHIDA
BABI NA SHA BAKWAI
BABI NA SHA TAKWAS
BABI NA SHA TARA
BABI NA ASHIRIN
BABI NA ASHIRIN DA DAYA
BABI NA ASHIRIN DA BIYU
BABI NA ASHIRIN DA UKU
BABI NA ASHIRIN DA HUDU
BABI NA ASHIRIN DA BIYAR
ASHIRIN DA SHIDA
ASHIRIN DA BAKWAI
ASHIRIN DA TAKWAS
ASHIRIN DA TARA
TALATIN 30
TALATIN DA DAYA
TALATIN DA BIYU
TALATIN DA UKU
TALATIN DA HUDU
TALATIN DA BIYAR
TALATIN DA SHIDA
TALATIN DA BAKWAI
TALATIN DA TARA
TALATIN DA TARA
ARBA'IN
ARBA'IN DA DAYA
ARBA'IN DA BIYU
ARBA'IN DA UKU
ARBA'IN DA HUDU
ARBA'IN DA BIYAR
ARBA'IN DA SHIDA
ARBA'IN DA BAKWAI
ARBA'IN DA TAKWAS
ARBA'IN DA TARA
HAMSIN
Complete

BABI NA UKU

3.6K 186 2
By ZulayheartRano89

3

“Wa ye ubansa a north Nigeria da har zai kai hannu fuskar ki da sunan duka?” Kai da jin yadda yake maganar ka san a zazafe ya yi ta.

Ɓangaren Ameesha kuwa hawaye ne suka cigaba da zuba tamkar an saki famfo, domin kuwa ba ƙaramin shigar ta marin ya yi ba. Don haka murya a sanyaye ta fara magana, “Abba ba ɗan kowa ba ne hasalima shi ɗin wani ƙasƙantaccen mutum ne, wanda ba shi da ko sisi, Motar da yake hawa ko kyauta aka ba ni ba zan iya hawanta ba.” Ta dire maganar tana ƙara fashewa da kuka.

“Maza ɗauko mini lambar motar, zan yi maganin kowaye shi.”

Ɗago kan da Ameesha za ta yi sai taga wayam! Babu motar babu kuma mai motar, wani tuƙuƙun baƙin ciki da takaici ne suka taru suka lulluɓeta, “Abba ya wuce ban san ma lokacin da ya wuce ba.” Ta faɗa cikin takaici.

“Maza ki dawo gida, ko in zo in ɗauke ki ne?” Ya faɗa cikin sigar lallashi.

“No Abba ba sai ka zo ba yanzu zan dawo.” Ta gama maganar tare da buɗe mota ta shiga ciki, a ranta ta ƙudirta ba za ta ƙara zuwa Sahad store ba, domin a yanzu wajen ya zamar mata wajen jin kunya.

Cikin gida kuwa Abba sai kai komo yake, sai jan tsaki yake yi mtswwww! Don kuwa hankalin shi ya tashi matuƙa da jin maganar abin da ya samu Ameesha, Hajiya Halima da ta fito daga kicin ta tsaya tana kallon maigidan nata, har za ta wuce sai kuma ta ga rashin dacewar hakan, don haka sai ta fara magana cike da kulawa “lafiya kuwa Alhaji?”
Bai tanka mata ba sai ya ƙara sakin tsaki tare da aikawa Ummiee harara, sannan ya fara magana  “Yo ina fa lafiya Hajiya? Wai daga fitar yarinyar nan, har an samu wani ɗan-iskan ya zazzabga mata mari, ta ya hankalina zai kwanta ban ga dawowarta ba.
Cike da mamakin furucin shi na ƙarshe ta fara magana “Wai wace aka mara ne?”

“Inada wata 'yar ce bayan Uwata? Ya cigaba kin ga Hajiya karki kuma ɓata mini rai, dama fa na kula tun farko baki so fitan yarinyar nan ba, don haka burinki ya cika tun da an wulaƙanta mini ita a waje.” A masife ya ba ta amsa.

Girgiza kai Ummiee ta yi, ita dai har kullum lamarin mijinta yana ɗaure mata kai, wani lokacin idan ya yi abu sai ta ji kamar ta rufe shi da duka, zuciyarta na tuƙuƙi ta fara magana, “Ni kam Alhaji abubuwanku yana ba ni matuƙar mamaki, musamman idan ka faɗi wata maganar, ta ya za ka ce wai na ji daɗi saboda an wulakanta Ameesha? Karka mata fa ni na haife Ameesha, kuma banƙi ace Ameesha ta fi kowace 'ya mace nutsuwa ba, na tabbata Ameesha babu ta yadda za a yi wani ya ɗaga hannu ya mareta ba tare da ta yi masa komai ba, wata ƙila ma irin rashin kunyar da saba da yi ne ta yi masa ta yi masa shi ya sa ƙila ya mareta, amma kai ba za ka yi bincike ba, sai dai ka yanke hukunci ka ɗaura laifi a kan wai mutum daban kuma magana ta gaskiya ba hakan babu kyau.”

Ɗaga mata hannu ya yi alamar ta yi masa shiru, daidai lokacin Ameesha ta shigo, kai tsaye jikin Abba ta faɗa tare da sakin wani sabon kukan.
Bubbuga bayanta Abba ya soma yi alamar rarrashi ya fara yi mata magana cikin rarrashi “Yi haƙuri Uwata karki bar wannan ya dame ki, In Sha Allah zan ɗauki mummunar mataki a kan koma waye shi, duk ranar da Allah Ya haɗamu.”

“Da zan baka shawara ka ɗauka, to da sai na ce  ka bi komai a hankali zai fi, amma wannan maganar da kake ba shi ne daidai ba.” Ummiee ta yi maganar tana zama a kan kujera.

“Haba Ummiee kin ga kuwa irin wulaƙancin da ya yi mini, da har kike cewa a bi komai a hankali, wallahi Abba karka bi a hankali.”

“To uwar rashin kunya, da ke na yi magana? Da har kike cewa kar ya bi a hankali? To shi kenan ku je ku yi, na tabbatar wata rana sai kun yi nadamar duk abin da kuke aikatawa nadamar ma mara amfani.”

“Ni fa wallahi Hajiya bana son irin wannan maganar da kike yi, ke kullum bakinki ba ya furta Alhairi a garemu kullum sai mugun baki, to wallahi ta Allah ba ta ki ba.”

“Ku dai Gaskiya ce baku so, ni kuma dole sai na faɗa."

“Ki rike gaskiyar ki bamu so ɗin.”

“Yawwa Abba ina son duk lokacin da kuka haɗu, karka saurara masa ka nuna masa ni ɗin 'yar gatan ka ce.”

“An gama Uwata maza je ki ɗaki ki ɗan watsa ruwa ko za ki ji sanyi.”

“To Abba sai na yi sallah zan fito, don a hanyata ta dawowa na ji an kira.”

“A fito lafiya ɗiyar Abba.”

Murmushi Ummiee ta yi, don wannan halin na Ameesha kaɗai ke burgeta, duk abin da take yi da zarar ta ji an kira sallah, bata bari lokaci ya wuce ta, kusa da Ummiee ta matsa tana cewa

“Ummiee yau me kika dafa mana ne?”

“Tuwon shinkafa ne miyar wake.”

“Wowww! Ummiee kin yi abin da nake son ci.”

Da fa kanta Ummiee ta yi ta ce, “To ga can a dining komai is ready.”

“Ok bari na fito.” Ameesha ta yi maganar ya yin da take taka matakalar benan don hayewa sama.

Farin ciki ne ya kama Alhaji Taheer mahaifin Ameesha ganin yadda suka yi magana cikin walwala da farin ciki.

Shigarta bedroom ɗin ke da wuya sai ta wurgar da Jakkarta dake hannunta (hand bag) tare da cire gyalen da ta yafa, kai tsaye toilet ta nufa ta sakarwa kanta ruwan sanyi, ƙila ko ta samu sassaucin abin da take ji a zuciyarta, ta jima sosai sannan ta fito bayan ta ɗauro alwala, zanen da take sallah ta ɗauko tare da hijjab ɗinta sannan ta tayar da sallar.

Bayan ta idar da sallar, ta shirya cikin wani wando da riga wanda suka yi mata matuƙar kyau, wandon pencil ne kalar pink, rigar kuma body top ne kalar white, sun amshi jikinta, ta yi pakin kanta da ribbon kalar wandon ta, tsaf ta feshe jikinta da turaruka masu ƙamshi.

Masha Allah, Gaskiya Allah ya yi halitta don Ameesha kam babu inda Allah ya rage ta, ta fannin halatta kyakkyawa ce wato (First Class) ajin farko, gata doguwa, bata da ƙiba ko kaɗan, amma fa akwai ta da hips and braest, komai cif.

********************************

Cikin ƙwarewa yake driven motar, fuskar sa ɗauke da wani special smile, haka kawai in ya tuna yarinyar sai ya ji zuciyar sa fes! Sai dai wani ɓangaren na zuciyarsa tana fama da raɗaɗi tare da dana sanin marin da ya mata. A fili ya furta, “Shi is very Beautiful Girl, duk wanda ya samu wannan budurwa a matsayin matar aure babu shakka ya gama morewa a duniya.”

Wayarsa ce ta soma ruri a lamar tana neman agaji, da sauri ya ɗauki wayar ganin mai kiran ya sa shi sakin murmushi, picking ya yi tare da karawa a kunne, “Hello Allah hokke sabbugo Nannena, mid'o a nyalli jam, noi sare?” (“Allah ya baki tsawon rai Nannena, fatan kina lafiya ya gida?”)

“Jamni tawon Asmad mid'o yela wala billare fere kam...” (“Lafiya lau Asmad fatan kai ma baka da matsala?”)

“A'a Nanne wala ko d'ume, jottama mid'o lawol Wartugo sare.” (“A'a Nanne babu matsalar komai, yanzu haka ina hanyata ta dawowa gida”)

“Allah wadde jam amma a hakkilina lawol anani naa barkantejo...”  (“Allah ya dawo min da kai lafiya amma ka kula da kyau ka ji ɗan Albarka.”)

Murmushi ya yi lokacin da ya kammala waya da mahaifiyar na shi, yana jin farin cikin yadda Nannensa ke ba shi kulaww, cikin mintina ƙalilan ya iso unguwarsu, a bakin wani makeken get ya tsaya, horn ya yi cikin sauri maigadin ya wangale masa get ɗin, wowww! Ma Sha Allah, gida ne babba ginin zamani, kai da ganin gidan kasan an kashe kuɗi, da ka shigo gidan da ɗakin maigadi zaka soma karo, gefen dama kuma, wani ɗan ɗakine aka gina da alama na generator ne, sai wasu flowers da aka daddasa masu kyau, su suka kuma sa gidan ya haɗu, gefe guda kuma parking space ne, motoci jere a ciki masu dan banzan kyau.

Sai mutum ya yi dan tafiya kafin ya ida sa shiga ainihin cikin gidan. A parking space ya faka motar shi, sannan ya fito tare da ɗaukan laidar da ya yi sayayya a Shahad ɗin, ƙofar babban falon gidan ya shiga bakinsa ɗauke da sallama, wata kyakkyawar mace wacce ba zata wuce shekaru 40 zuwa 42 ba zaune cikin haɗaɗɗen  falon, babban falo ne wanda aka ƙawata shi da wasu manya-manyan kujeru  na alfarma, ga wani carpet mai shegen kyau wanda ya fito da ainahin kyaun falon, kalarsa da kujerun ɗaya, wato brown color, haka ma labulen, babban Plasma TV ne manne a bangon falon.

Kallo ɗaya za ka yi wa matar ka san bafulatana ce, fara ce fuskar ta ƙunshe da annuri, mace ce mai riƙo da Addini don hannunta riƙe yake da wani littafin Addu'o'i tana karantawa, jin sallamar dan nata ya sa ta yi saurin d'agowa fuska d'auke da murmushi ta amsa masa sallamar.

Inda take zaune ya ƙarasa, zama ya yi kusa da kafarta tare da lanƙwashe ƙafarsa, ya soma gaidata, shafa kansa ta yi tana faɗin, “Ja66ama Asmad, awartii Jam...” (“Barka da zuwa Asmad ka dawo lafiya?”)

“Jamni tawon Nanne, sai welo minanata...” (“Lafiya Lau Nanne sai dai ina jin matuƙar yunwa.”)

“Ta damu mitimmini nyamdu...” (“Karka damu akwai abinci, ban daɗe da gamawa ba.”)

“Yawwa Nanne 6ewaddina aam sudu aam, hiddeko mi wurta yiwugo...” (“Yawwa Nanne a kawo min bedroom dina yanzu, kafin na fito wanka.”)

“To ha ladidi waddine...” (“Ba ri Ladidi ta kawo maka”.)

“A'a Nanne miyid'a 6ingel d'o nastimi sudu aam, toi aneesa ko'o huwata, hokku moo ne o wadda...” ( "a'a Nanne ban son wannan Yarinyar tana shigar min bedroom, ki dai baa Aneesa ita aikin me take yi?”)

“To yahu hami hokka aneesa man waddine...” (“To je ka Aneesa zata kawo maka.”)

"Yawwa Nanne hanju wad'i miyid'i Ma...” (“Yawwa Nanne shi ya sa nake ƙara sonki.”)

Asmad ya yi maganar yana miƙa mata, ɗaya daga cikin ledar da ya shigo da shi, amsa ta yi tare da sanya masa Albarka, shi kuma ya fita tare da nufa ɓangarensa.

Continue Reading

You'll Also Like

190K 20.3K 56
"කේතු දන්නවද මම කේතුට කොච්චරක් ආදරෙයි කියල ?" "හැමතිස්සෙම වචනෙන් නොකිව්වත් සර්ගෙ ඇස් මගේ ඇස් එක්ක පැටලෙනකොට ඒ දිලිසෙන ඇස්වලින් මට පේනවා සර් මට කොච්...
21.2K 662 28
Unicode ငယ်ကိုအရမ်းမုန်းတာပဲလားမမမုန်း သဲငယ် ငါ့ဘဝမှာမင်းကိုအမုန်းဆုံးပဲ တစ်သက်လုံးမုန်းန...
18.5K 2.6K 22
දන්නවද ආර්ය්‍ය..❟ පෙති තලලා මල කැඩුව පමණටම බඹරෙක්ට මලක් අයිති වුන්නැහැ..! සේමිය- උබ කියන මගුලක් මට තේරෙන්නෑ ඕයි හැබැයි මෙච්චරයි බඹරෙක් නෙවෙයි මොකෙක්...
42.8K 995 6
Hiroki has recently discovered that the four women he once knew and loved, his girlfriend (Nao), sister (Kanoko), best friend (Ayumu), and mom (Kaede...