MAHREEN

By HAERMEEBRAERH9900

1.8K 437 71

A Koda yaushe muna Jin labaran zama da kishiya Mai ban mamaki da ban al'ajabi....Labarin MAHREEN labari ne na... More

MAHREEN PAGE 1
MAHREEN PAGE 2
MAHREEN PAGE 3
MAHREEN PAGE 4
MAHREEN PAGE 5
MAHREEN PAGE 6
MAHREEN PAGE 7
MAHREEN PAGE 8
MAHREEN PAGE 9
MAHREEN PAGE 10
MAHREEN PAGE 11
MAHREEN PAGE 12
MAHREEN PAGE 13
MAHREEN PAGE 14
MAHREEN PAGE 15
MAHREEN PAGE 16
MAHREEN PAGE 17
MAHREEN PAGE 18
MAHREEN PAGE 19
MAHREEN PAGE 20
MAHREEN PAGE 21
MAHREEN PAGE 22
MAHREEN PAGE 23
MAHREEN PAGE 24
MAHREEN PAGE 25
MAHREEN PAGE 26
MAHREEN
MAHREEN PAGE 27
MAHREEN PAGE 28
MAHREEN PAGE 30
MAHREEN PAGE 31
MAHREEN PAGE 32
MAHREEN PAGE 33
MAHREEN PAGE 34
MAHREEN PAGE 35

MAHREEN PAGE 29

31 7 5
By HAERMEEBRAERH9900

💅  MAHREEN  💅


WRITTEN BY HAERMEEBRAERH

PAGE 29:

Gaba ɗaya hankali na ya tafi wajen kallon ajin da matar ke tattare da shi wanda ya sanya idanu na cika da ganin kyan ta duk da cewa ba wata kyakkyawa bace sosai, yanayin shigar ta da ajin ta ne ya qara fito da kyan ta, gaishe ta na yi sannan na maida hankali na gefe guda ina tunanin yanda Maman Abdurraheem ta ke ta murnar ganin matar da alama ta na da mahimmanci a wajen ta, bangaren Maman Abdurraheem suka shige su na ta murnar ganin juna, ni kuma se na tashi na tattara kaya na na shige nawa bangaren na yi alwala na yi sallah sannan na hau girki, ina yi ina karatun wani novel da na aro wajen Aunty Sumayyah, (Maman Amirah) ban gama girki na ba Maman Abdurraheem ta shigo muka zauna mu na hira, anan take sanar da ni qawar ta ce ta zo nuna mata motar da mijin ta ya sai mata kwanan nan,hirar maganin mata ta hau yi min har kalar wanda qawar ta ta ke amfani da shi,mamaki duk ya kama ni, daga Shan maganin mata se a maka kyautar mota? Ko dai dama can mijin ya yi niyya ne? Daga sama na jiyo muryar Maman Abdurraheem ta na cewa,

"Na taya ta murna, amma mu da mazan mu ba su da halin siyan mota ko albarka aka saka mana ai mun gode"

Dariya mu ka yi a tare, ina ci gaba da jinjina lamarin.

"Ke bari ma zan baki wani magani ki gwada ya na da kyau, sannan akwai lalle da zan baki ki qunsa a qafar ki, da wani ruwa, ke in ki ka sha ruwan nan ko? Hummmm ba a cewa komai, ki bari kawai zan baki su ki gwada mugun tsada ne da su in ya qare se kin nema"

"To ni ina na ga kuɗin siyan maganin mata musamman me tsada? Ai kedai kawai ki bani domin Allah na sha a samin albarkar nima "

Dariya mu ka sake yi, cikin zuciya ta ina addu'a kar Allah ya bata ikon bani maganin nan, musamman lallen.

'wanne irin lalle ne na mallaka ko farin jini? Me aka saka a ciki? Sannan menene a cikin ruwan da zan sha ina aka samo shi? Ba zan iya sha ba gaskiya'

A fili kuwa ina ta biye mata mu na magana, nan take na tuna wani maganin mata da karambani na ya kai ni na sha shi da jimawa, awanni kaɗan da sha Yah Maheer ya dawo, sai da komai ya kankama na hau zubar da jini ba qaqqautawa ba tsayawa se da na yi kwanaki biyar sannan ya tsaya, na zaci period ne na sake gwada sha, jini ya sake balle min har da guda guda, abun tun ya na ban mamaki ya dawo bani tsoro,duk sanda na sha maganin mata za a yi abu d'ayan uku ne.

Ko na dinga zubar da jini har se aikin maganin ya qare a jiki na.

Ko na dinga qunci da yawan neman faɗa da masifa da bala'i Dan a Kula ni na yi fushi na qi bada haɗin kai.

Ko kuma qatoton qurji ya fito min guda ɗaya tall raina kama ka ga gayya wanda motsin arziqi ba zan iya ba har se aikin maganin ya qare a jiki na.

Ganin haka ne ya sa na sawaqe wa kai na wahala, gashi ba zan iya ce mata kar ta bani ba se ta ga na raina qoqarin ta, tunda akwai wadda ta taɓa sanar da ni cewar a garin Kebbi mace ta nuna ta na son ki da alkhairi shine ta baki tsarabar maganin mata, a haka dai maganar bani maganin mata ta tashi ba a ban lallen da ruwan ba se aka bani gumba da madara na sha cikin iko na Allah sai ban zubar da jini ba, amma fa haka nan Yah Maheer da kan shi ya ɗauke wuta, za mu kwana waje ɗaya yanda muka saba maqale da juna amma ba zai nemi komai a waje na ba har safiya ta waye, haka da safen ma za mu koma baccin safe kamar yanda muka saba amma haka za mu tashi ba abinda ya gitta, gajiya na yi da wahala na cire rai akan komai na sa wa raina se maganin ya bar aiki jiki na komai zai koma mana normal, tunda ni kaina se na ji ba zan iya fara miqa kai na da kai na ba se ya nema.

Rayuwar mu muka ci gaba da gudanar wa kamar wasu 'yan uwan juna na jiki, zama muke mu sha hira duk ta san mutanen gidan mu a baki na wanda dama zai wahala ka zauna da ni baka san Mama...Baba...Innata...da yaran gidan mu ba gaba dayan su, saboda su ne rayuwa ta, yanda kuwa Yah Maheer ke kula da ni be taɓa damun Naman Abdurraheem ba dan ban taɓa gani ba a fuskar ta ko a maganar ta, duk watarana ta kan tsokane ni  in ta ga ya min wani abu takan ce, 'Uhmm ka ga masoya/ mu ma dai Allah ya sa mu na da masoyan' wata rana kuma in ya yi wani abu da ya burge ta sai dai ta hau yaba masa, ba dai ta kushe ba, ta ce na roqi Allah ya sa ita da mijin ta su koma kamar yanda muke, murmushi na kan yi na janyo wata hirar a bar maganar mu.

Mu na nan zumuncin mu na ta qara qarfi da Maman Abdurraheem, zaman lafiya na ta wanzuwa tsakani na da Yah Maheer, sai dai kun san a koda yaushe ba a rasa sabani irin na harshe da haqori, to muma mu na samun wannan lokaci zuwa lokaci,watarana mu na zaune ana hirar gida da ni da Yah Maheer sai na ce,

"Kaiiii amma ban taɓa zuwa gidan da ya yi bala'in yi min dad'i ba sama da wanda mu ka yi d'innan ba hayaniya,ba takura ba tashin hankali,zallan zumunci aka sha aka dawo,komai cikin sauqi gwanin sha'awa"

Wata kalma Yah Maheer ya jefe ni da ita da ta sanya ni hantsilawa daga kujerar da nake zaune na kifa qasan carpet ba shiri tare da sauke masa idanu na da ke cike da tsantsan mamakin kalaman shi.

"Me ka ce? Me ka kira ni da shi?"

Cikin nuna rashin danasanin kalaman shi ya maimaita abinda ya ce,

"Cewa na yi dole ki ce wancan zuwan ya maki dad'i mana tunda kin haɗa munafurci kin taho"

Ji na yi kamar ya buga min guduma akai na, tsabar yanda na ji kalmar munafurcin ta dake ni, mutumin da banza ko wani sunan zagi be taɓa haɗa ni da shi ba ke faɗin na haɗa munafurci, to wanne munafurcin na haɗa, nan da nan na ji ido na ya taru da hawaye, Suwaidatu da ke zaune a gefen mu sai ta hau raba ido a tsakanin mu, zama na yi da kyau ina fuskantar shi na ce,

"Wanne irin munafurci na haɗa ni kuwa har da ban sani ba tsahon lokacin nan da muka ɗauka da dawowar mu, ashe na haɗa munafurci shine ba ka taɓa faɗa min ba? Ba dan an dakko maganar gida ba kenan haka za ka dinga min kallon munafuka ba zaka sanar da ni komai ba ko?"

Nan take idon shi ya nuna nadamar abinda ya faɗa amma bakin shi ya kasa qaryata kalaman shi, zama na gyara na ce se ya sanar da ni munafurcin da na haɗa, nan ya fara zayyano min wani zancen qarya da aka tuqa shi aka ce ni Mahreen ni na faɗa kuma ni na hada komai, ashe bayan tafiya ta Bauchi daga liman Katagum har gaban manya aka zauna aka tattauna, direct a gaban mutane Yah Maheer bai kare ni ba saboda kar a ga ya bi baya na sai ya furta musu cewa 'Ashe Mahreen ita ce munafukar da ta haɗa komai ta tafi' nan take Kabeer  ya ce 'Kai ma ka san ba zata taɓa aikata hakan ba a dai sake bincike'.

Wani irin duhu na ji ya mamayen ido na tsabar hawayen da ke zuba min ba na gani sosai kwata kwata, nan take na zauna na zayyane masa duk abinda ya faru iyakar gaskiya ta,alamun gamsuwa da kwanciyar hankali ne suka bayyana a saman fuskar Yah Maheer wanda ya bani mamaki matuqa, kenan da ban masa bayani ba ya yarda ni munafuka ce har ya iya furta hakan a gaban mutane? A duniya be taɓa min abinda ya qona min rai irin wannan ba, wani irin haushin shi da ban taɓa ji bane ya mamaye zuciya ta.

Nan take mu na zaune ya sa waya ya kira Kabeer  ya bashi labarin kaff da na bashi, ina Jiyo sanda kabeer ya ce masa,

'Ai na faɗa maka ba zata taɓa yin abinda aka ce ta yi ba, habaa kowa fa da kalar tarbiyyar shi, kuma mun san halin kowa, kowa da abinda in aka ce maka ya aikata to fa ba makawa ya aikata ɗin in kuma aka ce maka be aikata ba to fa be aikata ba'

"Hakane, Allah ya sa mu dace ya haɗa kan iyalan mu, Allah ya shiryar mana da su"

"Ameeen ya Allah"

Sallama suka yi da junan su, sannan Yah Maheer ya miqe ya na so ya kama ni dan ya bani hakuri, wani irin kallo na watsa masa da ban san ma zan iya yi masa irin kallon ba har abada, jikin shi ne ya yi mugun sanyi, ya durqusa gaba na ya na so ya kamo hannu na, kuka na fashe da shi sosai, zuciya ta na quna matuqa.

Ina son da yake min?
Ina kulawar da yake bani?
Ina qaunar da ke tsakanin mu?
Ina aminci da yardar da ke tsakanin mu?
Ta ya za a yi abu bana nan iya tsahon wannan lokacin ya kasa sanar da ni?

Ta ya za a yi abu bana nan ya kasa tsaya min har ya kira ni da munafuka a gaban mutane?

Me yasa ba zai bada shaida akai na ba tunda ya san ba hali na bane ba zan taba iya bata zumuncin da ke tsakanin mu ba se dai na gyara.

Miqewa na yi na shige daki na barshi duqe a wajen,ya rasa ma abun faɗa dan ya san na riga na yi mummunan fushi da shi.

Allah Allah nake ya fita Masallaci na siyo katin waya na kira Habibah na ji dalilin da ya sa ta min haka,ina nan zaune na ji ya na faɗin,

"A tashi a yi sallah, se na dawo"

Banza na yi da shi, tunda dama ai da hankali na ba se an fadan na je na yi sallah ba, na san daidai, murguda baki na yi da na ji ya fita, da sauri na yi zillo na sakko daga gado na fita parlour riqe da ɗari biyar a hannu na, Suwaidatu da ta yi alwala na ba wa na ce ta siyo min katin waya na MTN na duka kuma ta yi sauri kar ta jima.

Ai kuwa ta na karba bata jima ba ta dawo, ina nan zaune daga ni sai vest dina me kyau kalar pink da gajeren wandon ta na daure gashi na da ribom kalar pink se pink dankunne qarami da na sanya,ina ta kad'a qafa ina tuna kalar cin mutuncin da Habibah da Mommy matar Abubakar suka yi min, dan wannan cin mutunci ne ya taba mutunci na abinda suka min.

Ina karba na loda a waya ta, ya na gama shiga na nemo lambar Habibah na kira, cikin Sa'a kuwa ta hau ringing ba jimawa ta dauka, ashe an sa ni a handsfree ne ban sani ba, nan na fara tuna mata abubuwan da suka faru na ce me ya sa ta juya magana kai na? Dariya ta yi ta hau yi min maganar banza wadda har yanzu ban gama gane inda ta dosa ba wanda na ɗauki hakan a matsayin shirme da sambatun kare kai.

Muryar Mommy na ji matar Abubakar da Abubakar ɗin kan shi su na dariya nan take Mommy ta daga murya ta min magana, murmushi na yi bayan na gane inda suka dosa, kawai se na kashe waya ta, raina na qara ɓaci ina jin haushi matuqa akan abinda suka min, wato na yarda da su dukan su, kuma a zato na duka daya muke, kullum Mommy ta kawo min sukar Habibah zan hana na ce ta dena saboda kar zumunci ya rabu, ita ma Habibah koda yaushe se ta yi complain akan Mommy da Abubakar, ban tsaya na zama 'yar tsakiya munafuka ba a tsakanin su na yi qoqarin nuna wa kowa kuskuren shi da yanda ya kamata ya gyara ashe ban kyauta ba, shawarar kuma da na bawa Habibah akan kuɗin takalmin ta nan ma da ta ce Isma'il ya cinye shima na yi laifi, kad'a kai na yi tare da share kwallar baqin ciki da ke zuba min a kumatu na sannan na ce,

"Wato su nan su na nuna cewa su 'yan daki ɗaya ne ni da Yah Maheer mu ne bare, duk kalar qiyayyar da suke nuna wa juna ina qoqarin haɗa kan su se suka ware ni suka haɗa min munafurci? To da kyau gwanda da aka yi haka, Allah ya bamu rai da lafiya"

Da kyar na tashi na je na yi alwala na yi sallah, ina sujjadar qarshe ina addu'a tare da kuka a cikin sallah ta akan Allah Ubangiji ya bayyana gaskiya ta ya saka min qazafin da su ka min Yah Maheer ne ya shigo ya ganni ina sallah ina kuka, hankalin shi ba qaramin tashi ya yi ba, saboda shi fa duk abinda za a kai shi qara wajen Allah baya so, nan take ya zauna a gefe na, ina idar da Sallah ya rungume ni ya na bani hakuri, cikin fushi na fizge kai na na ce,

"So ka ke in yi halin nawa na munafurci na ce maka na yafe maka bayan a zuciya ta ba haka bane? Dan Allah ka kyale ni ni"

"Ba zan kyale ki ba Baby na har se kin yafe min, ban fad'i haka ba sai dan bana so su ga kamar na bi bayan ki ne ba tare da an yi binciken gaskiya ba, amma dan Allah ki bar maganar komai ya wuce"

"A wajen ka ba? Yanda suka bata min rai suka yi qoqarin bata suna na ba zan yafe ba,"

"Dan Allah ki yafe ki yi hakuri haba baby na ke fa ba kyau fushi"

Ganin ya na so ya maida abun wasa ne ya sa na kalle shi kallo na ba fa wasa ake ba anan malam, jan bakin shi ya yi ya tsuke amma yinin ranar ba inda ya sake zuwa, daga masallaci se gida ya na faman ban hakuri, ni kuma ina sake hawa dokin zuciya dan gani nake komai ya ce min ma sake raina min hankali yake ni ce munafuka duk qoqarin da nake na daidaita zumunci a tsakanin matan shine na zama munafukar shi, zai kuwa ga aikin munafukai.

Ina cikin wannan fushin ne Uncle Inuwa ya tashi zai yi tafiya, sai Maryam ta roqi azziqin mu ara mata Suwaidatu ta koma wajen ta da zama, ba bata lokaci muka tattara Suwaidatu da kayan ta ta koma wajen Maryam, ni kuma na ci gaba da fushi na, Yah Maheer ya san me ke saurin saukar da fushi na, nan take kuwa ya dinga bani cin hanci chocolates da Apple green din, se ya ciko baqar leda da su ya kawo min ya ajiye ni kuwa dake ban huce ba se na buɗe da ya fita se na dauki ɗaya ɗaya yanda ba zai gane ba a gani na kenan, se na cinye, da ya dawo na ci gaba da fushi abu na.

Wata ranar juma'a se ya kawo chocolates da Apple da chewing gum da biscuits, ya ajiye a fridge ya fita, ya na fita na ja leda na hau ci ina jin dad'i har qoqon zuciya ta ina addu'ar Allah ya kai mu aljannah mu ci na can mu ji ya yake, dariya na ji ta na tashi a baya na,dan kuwa ta qofar kitchen ya shigo parlourn, bata rai na yi baki cike da Apple, na qi na ci gaba da taunawa abunka da me kumatu sutum sutum se suka qara hayewa sama, cikin dariya da hawaye Yah Maheer ya ce,

"Baby na ba Kya fushiiiiii"

Wata iriyar dariya ce ta kama ni ban san sanda na kece da dariya ba, a hankali ina dariya na cinye na baki na na sake kaftar wani, nan da nan aka shirya aka hau hira, ya so na bashi ko da Apple ne na hana, na ce punishment ɗin kira na munafuka ne, ya ce,

"Kashhhh ba Kya mantuwa, to na gode da aka yafe min na horu iya horuwa diba fa ki ga har ramewa na yi"

Daga nan salon namu ya sauya ya koma na masoyan asali, komawar Suwaidatu gidan Maryam ya bamu damar cin amarcin da bamu ci ba a baya, daga ni sai shi,haka muka dinga ririta juna mu na faranta wa junan mu, wasanni ba kalar wanda ba ma yi, goyo kuwa na sha shi kamar zan balla masa baya, in ya qi goya ni se na taso da laifin da ya min, na ce biya na b'acin ran da ya saka min zai yi, ya kan ce,

"Ohhh ni Maheer na shiga uku kamar ni ma ba a min laifi na ke hakuri na kau da kai amma ni an kasa min uziri"

Ina jin shi zan banza da shi se dai ya goya ni ɗin, gani da shegen nauyi amma se ya na kira na da 'yar paper, Wai saboda shi baya jin nauyin nawa, shi yake benefiting da goyon nawa a cewar shi.

Wata rana mu na zaune mu na shan iska da Yah Maheer a parlour sai ga su  Suwaidatu an taso su daga makarantar islamiyya ita da su Ameerah sun biyo dan a gaisa anan ne take bani labarin wani gida a baya da mu an yi gobara, matar na da jariri sabuwar haihuwa, nan take na ji hankali na ya tashi, ta na bani labari ita da su Ameerah da suka biyo ta dake unguwar da suka koma ya fi kusa da gidan Maryam ɗin Uncle Inuwa, nan take suka hau bani labari su na dariyar matar yanda ta rud'e, ina jin haka na tsawatar musu ina cewa,

"Ku dena dariya ba kyau, ba wanda ya wuce Allah ya jarabce shi da gobara Allah ya kiyaye mu, ku zo maza ku tafi magariba na gabatowa, a je a yi alwala kafin a fita, kar a manta a yi addu'a kafin a fita kuma a hanya kan a isa gida a na tafe ana azkar kun ji ko?"

"To aunty"

Alwala suka yi ina tsaye ina kallon su ina musu gyara a inda suka yi kure har suka gama suka tafi.

Wannan tsarin alwala in Za a fita daga gida daff da magariba tsarin Mama ne, takan ce,

'Ku yi alwala in ta kama dole se kun fita daff magariba saboda a lokacin shaidanun aljanu ke fitowa cin kasuwar su, gudun kar ka hadu da mugayen se ka yi alwala ka nemi tsarin Allah daga gare su'

Ni kuma se na ɗora da yin azkar a duk sanda na fita magariba ta taho ina tafe ina yi har na isa inda zani, in da yara nake tafe nan ma haka muke yi gaba ɗaya.

******************************

Ranar 5th January shekara ta 2012 rana ce da Adda Ummuna ta haifi 'yan biyu rana ce da ba zan taɓa manta ta a rayuwa ta ba, domin rana ce da ta tara min abubuwa da yawa na farin ciki da baqin ciki.

Bana manta wa da safe na je gidan Maman Ameenah karbar garwashin wuta domin na yi hayaqin habbatussauda da ke cikin magungunan Islamic da Yah Maheer ya siyo min nake sha, ina gidan Mama ta yo min waya tare da yi min albishir da haihuwar da Addah Ummu ta yi na yara biyu mace da namiji, tun a gidan na ke ta murna ina sanar da su abun farin cikin da ya same ni, taya ni murna suka dinga yi na dawo gida na sanar da Maman Abdurraheem wadda ta yi shiri tsaf zata fita unguwa ita da mijin ta da yaron su, fatan alkhairi suka yi mana da sanya albarka suka fita suka bar ni ina ta murna, na kira Addah Ummuna mun gaisa na mata barka tare da sanya albarka, se na zauna ina yi wa Yah Maheer kukan ina so in je in ga yaran, hakuri ya dinga bani ya na nuna min zuwa gida a wannan lokacin ba zai yiwu ba, amma na qara hakuri akwai lokacin da za mu je ɗin, murna ta bata boyu ba har mu ka yi sallahr azahar, mu na nan zaune cikin zafi ba wuta mu na hirar haihuwar Addah Ummu tare da jiran NEPA su kawo wutar 3 o'clock.

Dika-dika Sati ɗaya kenan da yin wata gobara a bayan layin mu, dake in sanyi ya zo haka ake yawan yin gobara a garin Kebbi musamman a unguwar,nan take na ji hankali na ya tashi, da misalin qarfe biyu da arba'in da wasu 'yan mintina Suwaidatu ta zo an aike ta Siyan kayan Miya ta biyo take bamu labarin gobarar, jiki na duk ya mace,daga baya muka koma yi mata faɗan qazanta duk ta dafe alamun bata wanka, Maryam dai ba qazama bace balle na ce ko a can ta ga ana rashin wanka, tunawa da kafiya da taurin kai irin na Suwaidatu ne ya sa na hau yi mata faɗa sosai saboda ta gyara ta dena zama ba wanka daga qarshe nake mata albishir da haihuwar 'yan biyu da Addah Ummuna ta yi mace da namiji, murna ta taya ni sannan ta musu addu'a ina ta jin dad'i a raina.

Kamar wadda aka yi wa wahayi ina zaune kawai se na kalli kai na, kamar kullum baqar shimi ce a jiki na me siririn hannu da guntun wandon jeans,tashi na yi na shiga daki na dakko wata doguwar riga ta armless na sanya na daura zanin atampa ta me adon flower purple da milk sannan na kalli qofa na ga hijabi na na nan saqale kamar kullum, zama na da abinda be fi minti huɗu ba mu ka ji an buɗe gate ɗin gidan namu da qarfi an shigo ana ihun.

"Malam Maheer gobara ! malam Maheer gobaraaaaa !! Ku na ina Gobaraaaaa !!!"

A guje mu ka fita har mu na rige-rige da ni da Yah Maheer da Suwaidatu wajen fita daga parlour....................

*Assalamualaikum mutanen kwarai masu albarka...kamar yanda na nemi shawarar ku wasun ku sun amsa ni da karrama wa da mutuntawa, dan haka inshaa Allahu za mu raba novel din Mahreen kashi biyu, da zarar kashi ɗaya ya qare wanda yake kyauta ne, kashi na biyu zai fara shi kuma zai zo maku ne a matsayin paid book da yardar Allah sai dai ni ba zan karbi kuɗi ba se bayan na kammala gaba ɗaya saboda halin yau,ba zan iya typing kullum ba, kuma ba zan yi alqawarin ga time da zan na posting ba duba da yanayin wasu uzururruka da nake da su,duk mai son ta shiga group din paid book ta min magana ta PC sai na saka ta a duk sanda na gama part one sai a fara part two d'in bayan na kammala dika sai a yi payment, bana son haqqin jama'a a kai na tunda Allah kaɗai ya san gawar fari shi kuwa bashi masifa ne in ba a sauke maka shi ba sanda ba ka a duniya...dan haka se na kammala za a yi payment,wataqila in na tuna 'yan kuɗaɗen na maida hankali na gama da wuri😂😂 kar ku ga Lehi na wa ya qi kudd'i??😂 Allah ya sa mu dace da rabon alkhairi.*

Continue Reading

You'll Also Like

5.4M 484K 98
✫ 𝐁𝐨𝐨𝐤 𝐎𝐧𝐞 𝐈𝐧 𝐑𝐚𝐭𝐡𝐨𝐫𝐞 𝐆𝐞𝐧'𝐬 𝐋𝐨𝐯𝐞 𝐒𝐚𝐠𝐚 𝐒𝐞𝐫𝐢𝐞𝐬 ⁎⁎⁎⁎⁎⁎⁎⁎⁎⁎⁎ She is shy He is outspoken She is clumsy He is graceful...
542K 34.5K 70
"Sshhhhh....." he hushed and pinned us against the wall leaving no space between us. I held onto his biceps with my hand in reflex. He shook his head...
3.4M 38.8K 31
Diana is an 18 year old girl about to start her senior year until she bumps into a woman at the bookstore who has quite the personality. The woman ta...
846K 8.4K 68
𝐢𝐧𝐜𝐥𝐮𝐝𝐞𝐬 𝐚𝐥𝐥 𝐨𝐟 𝐭𝐡𝐞 𝐛𝐨𝐲𝐬 ✦ .  ⁺   . ✦ .  ⁺   . ✦ don't forget to vote, share and comment. 🤍