YADDA NA KE SO

By Dijen-sy

968 110 44

YADDA NA KE SO burin Ummi ta auri mijin novel ,Mai arziki ba ta son talauci ya rayuwa zata juyawa mata a sand... More

Shafi 1
Page 2
Page 3
Page 4
Page 5
Page 7
Page 8
Page 9
Page 10
Page 11
Page 12
Page 13
Page 14
Page 15
Page 16
Page 17
Page 18
Page 19
Page 20
Page 21
Page 22
Page 23
Page 24
Page 25
Page 26
Page 27
Page 28
Page 29

Page 6

28 3 1
By Dijen-sy

    YADDA NA KE SO🌺


BY DIJENSY

PAGE 6

   Mukhtar bayan ya raka abokansa ya rufe masu gidan tare da komowa ciki,bai sameta a parlour ba a ranshi ya raya watakila d'aki ta koma.Kai tsaye ya shiga d'akin  ya isketa tsaye bakin mirror ,sallama yayi ba ta amsa ba sai juyowa da tayi tare da folding din hannayenta biyu a 'kirji tana binsa da wani kallon raini.

   'Lallai wannan abun Baba ya aura min ,ji be shi wani ba'ki da shi '

   Wani nazari Muhktar ya soma yana ganin yadda Ummin ta kafesa da idanu tana kare masa kallo ,a ranshi yayi tunanin tohm ko ita admiring dinsa take ne?

  Bai gama nazarinsa ba ta yi magana wanda ya dawo dashi daga tunaninsa "Are you wondering why I am staring? Kodayake ba abin mamaki bane idan ka ga ina kallonka domin na ga irin zab'in da Baba ya min ne ,tamkar yadda nayi zato haka na gani ba yadda nake so bane ,ta tako har gabanshi duk da ya kere ta ko a gefen silifas dinta ba wani respect ba tsoro ma a ranta.

  "Wallahi idan zuciyarka ta raya maka cewa akwai d'igon damuwarka a raina ta yaudareka ,I am open minded ba zan boye maka ba bana kaunarka na rantse maka ba aurenka a tsarin rayuwata ,dole  a ka tursasa min kai kuma ka bada gudumawa instead kayi rejecting  kai accepting ka sanya a ranka ma ba kai aure ba don kar kayi tsammanin duties na house wife daga gareni the door is open you are free to look for a house wife amma Ummi is excluded".

   Froze! Sunan wani abu shi ba ma maganganunta suka shayar dashi mamaki ba zallar rashin kunya da confidence nata yake gani ta tsaya a gabansa har take fad'a masa wannan maganganun rainin ,ko Rasheeda da take aure bata iya hada ido dashi sosai ko da kuwa shawara take bashi and see who is talking yanzu?

    Ashe daman ba ta so? Ashe daman Baba auren za'bi yayi wa yarsa?amma mene ya sa?

Tambayoyi da bai da mai amsa masa ya shiga jerawa ganin ba mai amsawa ya hakura ya na duba ta ya ma rasa mai zai ce mata.

   Gyaran murya yayi kafin yace "Yanzu dai ki ajje kayan makamanki ki yo alwala muyi sallah sai na saurareki".

   Wani kallo ta suake masa ya ma raina mata wayo me yake nufi oh bai ma saurararta yanzu?

   Wucewa ta ga yayi ya zaro wayarsa a aljihu ya ajje , pointing din toilet yayi mata ta tafi tare da tura kofar ta shiga tana karewa toilet din kallo Bai mata ba don ba colour din tiles din take so ba wata xuciyar ta fad'a mata daman ai ba zama kika zo ba.Alwala tayi ta fito ,ya shinfida musu sallaya  ya ja su jira take duk ya gama adduoinsa ba wacce tace ameen sai kallon kasa da ya kammala ta Yi saurin tashi ya dubeta yana daga zaune ta kewaya wajen wardrobe ta bude ta na duba yadda aka shirya mata kayanta ,night ware ta dakko ta ajje kan gadon sannan ta rufe ta tafi gaban mirror duk binta yake da ido  yana bawa zuciyarsa hakuri da shawarar yadda ya kamata ya bi da ita don ya ga ma yarinyace sharaf yadda take abu ma yan biyunsu sun fita manyance.

   Dan kunnayenta ta cire da agogon hannunta ta ajje su sannan ta waiwayo garesa "Tunda munyi sallahr you can excuse me zan kwanta".

  Tashi yayi ya ninke sallayan ya maida drawer da yake ya dubeta wayarsa ya mika hannu ya dauka ta bi hannunsa da kallo wayar ta ke so ta ga ma wacce iri ce ,ta ga android tayi tsaki a ciki.'Allah kadai yasan wa Baba ya Bata ,don da ganin gidannan Bai da wani arziki ga wayar da yake rikewa? Kowacce mota yake ja ma oho?"

Ta raya a ranta yace "Ba Zaki ci wani abu ba kafin ki kwanta?"

   "Idan zanci ai kna da bakin tambaya".

  Hadiye yawu yayi yana swallowing din duk wani anger da zata taso masa ya fita daga d'akin akwai d'aki a opposite ya shiga d'akin wanda shima anyi furnishing dinsa da kayan gado.Kayansa ya cire kamar ya sani suna d'akin ya bar su don haka ya  sanya jallabiya brown ya shinfida kan gadon yunwa yake ji amma ya nemeta ya rasa ya manta da wata kaza ma.Tunani kawai yake yadda zai bullowa da yarinyar can ba tare da an samu damuwa don she doesn't even seems to be calm da har zata sauraresa.Mafitar ubangiji ya roka kafin ya kashe light ya kwanta.

A bangaren Ummi kuwa yana fita ta rufo kofarta ta koma ta cire kayanta sannan ta sanya na bacci riga da wando ta kwanta.

  Washegari da safe 6am ta farka ta ga asuba ta wuce ,Koda tayi sallah wata yunwa ta ji ta addabeta ta fara tunanin me zata ci,wanka tayi tukun ta sanya doguwar rigar atampa ta fito ta duba kitchen shi kansa ta raina kitchen din ba haka ta so shi dukda yana da girma kawai tsarin ne bai mata ba ,ta hau bude fridge ba laifi da kayayyakin bukata a ciki ,sai dai ita ba ta Jin tana da energy girki ,locker ta duba ta ga kayan tea har da quicker oat da cornflakes tayi saurin dakko conflakes din ta hada ta aha sannan ta fito ,tana duba ko Ina ta ga dining madaidaici ta wuce d'aki ta zauna.Kamar saman yana biyw da ita ta gansa ya turo kofar d'akin Bata ko dago Kai ba tana ta latsa waya.

   "Kin tashi lafy?"Ya furta ba tare da ta dago ba tace "Akwai wata matsala ne?"

  "Babu".Ya amsa tare da juyawa kamar zai fita kawai ya dawo ,takowa yayi sai sannan ta dago ido ta sauke kansa yana sanye da jallabiya brown a ranta tayi tsaki don wani haushi da tsanarsa ta sake ji ,banda ba'ki ashe harda rashin iya dressing duk ya hada.A ranta ta fad'a.

  
  Zama yayi bisa gadon ta day'an gefen ta bisa da ido.

  "Khadija,ina so ki sani daga ni har ke wannan auren a kaddara ya zo mana ,ko ni ban taba zaton hakan zata kasance ba rashin yarda bashi zai daidaita matsala ba ,bance sai dole kin nuna min kulawa ba ko makamancin haka what I want is just respect from you, please idan na samu wannan I will be delighted shi kadai ma is enough ko da bazan samu sauran ba.Kiyi hakuri na shigo rayuwarki ,ba yadda zanyi ne nima nayi accepting offer mahaifinki ina so ki san da wannan".

   "Duk abinda kike bukata kada ki gaza tambayarta in sha Allah zan iya kokarina na dauke miki shi"

  Tashi ta ga yana yunkurin yi ta dubesa "Dakata,nan ka zo ka min waazi ne ? Ko kuwa gargadi kake so ka min ban fahimta ba?  See I am not hear for all arrange marriage wahala zancen hakuri ma bansan jinsa don ba yi zan ba indai kana son zaman lafy free me that is the only way zan san da gaske kake and ta wannan kadai zaka samu respect a guna".

   Tashi yayi bai mayar mata ba ta ga ya tashin cikeda jin haushi  "Magana nayi fa?"Ta furta.

  Tashi tayi ta taka gunsa ya waiwayo Kai da ganin yanayinsa Bai shirya wata rigima ba he is not ready for all this fight childish thing da kyar ya iya budar baki yace.

  "You need some rest ,na ji ana knocking a kofa".

  Harara ta bisa da ita kamar ta shakosa ta ga ya fice wai shi baya fishi?

   Tsaki ta ja "Dan iska maye".Ta fad'a don mamaki ma ya fara ba ta ta ya bazai yi fushi bane shi? Ta zaci tun jiya zata sare masa ya fara shawarar canja raayi meke damunsa?

***

Kannensa ya gani maza sun kawo masu abinci a lunch box yayi godiya suka tafi bayan ya basu kudin mota ya koma ciki ,a plate ya zuba mata ya kai mata d'akin ya ajje ya fito parlour ya zuba masa ya soma ci yana hadawa da tea ,kwai ne da chips Umma ta kawo.

 
Duba abincin tayi ta juya shi a wulakance ,guda d'aya ta dauka tasa a baki ta ji yayi dad'i suyan nan ta sakko dashi ta soma ci shayin dai taki sha da ta gama a masai ta juye shayin tunaninta ko ya sa magani a cikin shayin tazo tayi baci haka kurum ya haike mata?

    Tunda tayi breakfast ta rufo kofarta ta kwanta tare da kunna data ta shiga Netflix Muhktar yana parlour ya Lula duniyar tunani don ya ji sanda ta karkame kofarta , tambayar kansa yake a haka za su cigaba da zama?

'Ka bata lokaci idan aka kwana biyu zata canja '

  Zuciyarsa ta fad'a,wayarsa ya Bude ya soma dan duba chat's wasu duk na Allah sanya alkairi ne reply ya danyi kafin ya fita ya ajje wayar shingida yayi a kujera bacci ya dauke sa.Ya shafe wajen 2 hrs kafin ya tashi lokacin 12 tayi.

  Kamar dazun Umma ta sake kawo musu abincin rana ,Bai kasa a gwiwa ba yayi knocking din d'akin hakimar kallo take ba ta ji ba ya yi bugu ya gaji ya kira sunanta shiru shi tsorata ma yayi ya fara tunanin ko wani abu ne ya faru da ita ,d'akin da ya kwana ya shiga ya dakko spare key ya bude ta Yi ruf da ciki ta dora kirji Saman pillow tana kallo ya tsaya bayanta more than 2min ba ta sani ba don ta juya baya sai da ya karaso ya cire earpiece daya ta waiwayo a masifance.

   "Me ye ne?"Ta furta tana masa kallon banza.

   "Ina ta magana".Ya fad'a ba tare da daga murya ba.

   Tsaki ta saki tana zare dayan kunnen ta mike zaune.

  "Sabida zaka min magana sai ka taban kunnen? Beside kofa ta a rufe take da me ka Bude?"

   Yayi second 20 kafin ya amsa ta "Spare key , sorry for distracting abinci aka kawo na ajje miki a dinning ki taso mu ci".

  Gira ta dage"Kai da wa zaku ci abincin?"

  "Ni da ke".Ya amsa a ta'kaice".

  "Sabida?"

  "Ni mijinki ne".

Wata dariyar raini tayi "Sabida ka biya yan canji ka ke ganin you have right a kan komai nawa?".

  "Ya rabbil Al'ameen"Ya furta a fili.

  "Ka koma ta bana ci idan kana so naci order zaka sa a kawo min ba wani kwashe kwashe ba na zuba a ciki"Ta kare maganar kasa kasa.
   
    Zuciyarsa ba dad'i ya fita daga d'akin ya zauna kujera parlor yana zabga tagumi.A tunaninsa kyautatawa ce zata karkato da zuciyarta ,kojarinsa ya dan faranta mata ko yaya ne amma ya ga yadda ta ke behaving ma.

   "Allahumma ajirni fi musibati".

    Ummi kuwa maida headphones dinta tayi "Aikin banza dole sai nasan da existing dinsa".

     Wunin ranar dai ba dad'i yayi shi da daddare kamar jiya ta rufo kofarta abinci kuwa kin ci tayi karshe sai bawa almajirai yayi ya wankewa Umma kwanta ya ajje ya shiga d'aki  ya kwanta.

   Kwana uku Umma tayi tana Aiko da abinci yau ne na hudu da safe ya tashi da kansa ya dora doya ya fere ya dafa sannan ya zo ya soya da kwai ,inda Allah ya taimakesa yayi zaman hostel ya dan iya girki.Tea ya hado ya zo ya zauna ,ita kuwa baya sa ran ma zata fito don kwana hudu dinnan tana d'aki indai ta fito kitchen zata shiga shan qaucker oat ko cornflakes su ta mayar abincinta sai indomie.

 
    Tunda bai gama cika 1 year da aiki ba he is not entitle for leave ,hutun nasa sati daya ne don haka litinin mai zuwa zai koma.Wanke wanke yayi ya dawo parlour nan ya ga kiran wayar Baba ,ko da ya dauka bayan ya gaishesa a ladafce Baba ya ce masa yana waje.

    Tashi yayi ya duba ta a daki ta fito kenan daga wanka ba ta rufe kofar ba tunda ta tabbatar yana da spare key ,duk abinda ya gani shi ya ja ma kansa ta fad'a a ranta yanzun da ta ga shigowarsa tsuduk ta basar daga ita sai towel dan karami ko wuce cinya bai ba.

  Da har ya dan cake daga kofa kar ta masa rashin kunya tace ya shigo mata ba knocking ya ga ba ta ce komai ba.

"Idan kin shirya ki fito Baba yana waje zai shigo yanzu".

  Tun shigowarshi bata dago ido ba sai yanzun tsoro ta ji ko kararta ya kai ta amsa da toh a sanyaye ya fita ta Yi saurin ciro kayan da zata sa tana 'Allah yasa ba karata ya kai ba'.




Dijensy

 
 
   

Continue Reading

You'll Also Like

32.6K 111 17
When 12 year old Alex steals a diaper from the daycare his mom works at, he goes down a rabbit hole of his new addiction.
89.8K 1.3K 47
stray kids x reader scenarios, imagines and reactions that hopefully won't make you absolutely cringe and die, lower caps intended - this book contai...
220K 19.3K 27
Maybe sometimes love needs a second chance because it was not ready for the first time 🥀... Ekansh Malohtra a youngest buisness tycoon (28).. A man...
2.5M 187K 71
RATHOD In a broken family, every person suffers from his insecurities and guilt. Successful in every field but a big failure when it comes to emotio...