MAHREEN

By HAERMEEBRAERH9900

1.8K 437 71

A Koda yaushe muna Jin labaran zama da kishiya Mai ban mamaki da ban al'ajabi....Labarin MAHREEN labari ne na... More

MAHREEN PAGE 1
MAHREEN PAGE 2
MAHREEN PAGE 3
MAHREEN PAGE 4
MAHREEN PAGE 5
MAHREEN PAGE 6
MAHREEN PAGE 7
MAHREEN PAGE 8
MAHREEN PAGE 9
MAHREEN PAGE 10
MAHREEN PAGE 11
MAHREEN PAGE 12
MAHREEN PAGE 14
MAHREEN PAGE 15
MAHREEN PAGE 16
MAHREEN PAGE 17
MAHREEN PAGE 18
MAHREEN PAGE 19
MAHREEN PAGE 20
MAHREEN PAGE 21
MAHREEN PAGE 22
MAHREEN PAGE 23
MAHREEN PAGE 24
MAHREEN PAGE 25
MAHREEN PAGE 26
MAHREEN
MAHREEN PAGE 27
MAHREEN PAGE 28
MAHREEN PAGE 29
MAHREEN PAGE 30
MAHREEN PAGE 31
MAHREEN PAGE 32
MAHREEN PAGE 33
MAHREEN PAGE 34
MAHREEN PAGE 35

MAHREEN PAGE 13

56 10 3
By HAERMEEBRAERH9900

💅   MAHREEN   💅



WRITTEN BY HAERMEEBRAERH











PAGE 13:




Garin Bauchi shine tushen Baba zama ya kawo Kakammu garin kano har aka haifi su Baban, shima da ya tashi sai ya yi aure anan garin kanon, a hankali sai ga wata kwarya-kwaryar zuri'a ta tashi.

Sai ya kasance mu dake tasowa ba musan komai na al'adun mutanen Bauchi ba,mun san dai Bauchi garin masa ne,se dai tinda iyayen namu suka tabbatar da za su aurar da yaran su a can sai aka fara sanar da mu dikkan wasu abubuwan masu mahimmanci da ya kamata mu sani.

Na farko an nuna mana kar mu na gaishe da mutane a tsaye, domin mutanen bauchi na so a girmama su sosai, na daga cikin girmamawar in zaka gaida babba sai ka durqusa har can qasa, ba a son mata su na yawan saka kaya wanda zai bayyana tsiraicin su, wannan dalilin ne ya sa mutanen bauchi har yanzu suka riqe d'abi'ar d'aura zani da sa babban hijabi, bana mantawa da girma na an kusan aure na sai da Mama ta dinga koya min yanda zan d'aura zani, da ta ga har a wannan lokacin na kasa se aka d'inka min dogayen riguna da zani 3pieces.

An koya mana kwanon miji daban yake dole a killace shi a tsaftace shi na musamman, cokalin miji daban, takalmin miji da butar miji daban, wajen zaman miji ana gyarawa a tsaftace a sa turare, ballantana uwa uba d'akin da miji zai kwanta, an koya mana abubuwa da dama saboda kar mu shiga dangi mu zama daban.

Isma'il ya fara da tab'a duk wani abu da na killace na ce wannan na miji na ne, to inshaa Allahu shi kuma wannan abun shi zai zama abun tab'awar shi, da fari in ya d'auki abu sai dai in yi murmushi in kyale shi a zato na bai gama gane abubuwan da na ware ba, hakan da nake yi sai ya bashi damar yin abinda ya ga dama, har ta kai ya kai ni maqura na kasa jurewa sai da na tanka.

Wataranar juma'a ina kitchen na gama abinci na raba Suwaidatu ta kai wa Isma'il da Abubakar nasu,mu kuma muna zaune a kitchen d'in ni da Suwaidatu da Hauwa'u 'yar gidan qanwar Yah Maheer da ta dawo gidan da zama saboda ya fi kusa da makarantar da take zuwa, mun saka tabarma saboda girman kitchen d'in ya sa mu na iya zama a ciki mu ci abinci, sai ga Isma'il nan ya shigo.

"Ahhh abinci ake ci,"

"Eh, an kai muku naku ko?"

"Eh an kai amarya uwar gida daga kan ki wallahi an rufe qofa, cokali na zo na dauka wannan ai ba inda zai kai mutum, tinda na saba da manyan nan yanzu bana son amfani da wannan"

Waje yaran suka fita dan wanke hannu, kafin ya kai hannun shi zai d'auki cokalin da nake wa Yah Maheer amfani da shi na dakatar da shi,

"Dakata Isma'il,kar fa ka ga ina shiru ka dinga min abinda ka ga dama, wannan cokalin ka sani sarai na Yayan ku ne, amma saboda dai dole sai na yi magana an ga laifi na shine ka ke d'auka, to gaskiya daga yau kar ka sake d'aukan kayan miji na, tinda akwai wasu se ka d'auka ka yi amfani da shi da can ba da irin wannan d'in ka saba cin abincin ba"

Baki ya saki ya na kallo na, daga baya ya yi kamar be ji me na sanar da shi ba, ya ajiye cokalin hannun sa ya d'auki wanda nake wa Yah Maheer amfani da shi,ba tare da na b'ata lokaci ba kuwa na fizge na mayar na kalle shi ido cikin ido na ce,

"Da za a kawo ni ban san zan zauna da kai ba, dan haka kayan miji na kayan shi ne kar ka sake tabawa, plates d'in shi cokalin shi ba abun amfanin ka bane, ko ku a gida kuna amfani da kayan Baban ku ne?"

Fad'in haka da na yi sai ya yi mugun bashi mamaki, abun har ya kai haka? Har zan iya fad'a masa haka? Ya na gani na yarinya, gani da yawan fara'a ashe na iya fad'a? Ko d'aya cokalin be d'auka ba ya kama hanyar waje inda su Hauwa'u suka tafi wanke hannu, ya wanke hannun shi ya zo ze wuce, mu kuwa har mun fara cin abincin mu, se muryar shi na jiyo ya na fad'in.

"Allah ya bamu yatsu biyar mu sa mu tsaida sunnah" ni kuwa na d'aga murya yanda zai ji ni na ce,

"Ai ya kamata a fara tsaida ita sunnar ne tin fari ba sai an nemi magana ba wajen aikata bidi'a"

Mamaki na ya qara kama shi, kawai sai ya kad'a kai ya shige parlour, ina jiyo shi yana hira da Abubakar, ban san dai akan me suke magana ba, mu kuwa muka ci abincin mu muka tashi.

Isma'il be daddara ba ya fito zai maida plate kitchen tsabar neman magana, ga takalmin shi nan amma se ya jawo na Yah Maheer da nake kaiwa gefe na ajiye in ya fita, ya tura qatuwar qafar shi zai saka, cikin sauri na isa gaban shi na janye takalman na ce,

"Wai kai me ke damun ka ne? Ko rashin kunyar taka ta kai ka dinga ganin kan ku d'aya da miji na ne? Kar ka qara tab'a kayan shi na fada maka, ba tarbiyyar da aka mana ba kenan a gida yaro ya na saka kayan manya"

"Ni kenan bani da tarbiyya ba a min tarbiyya ba a gida?"

"Wannan kuma kai ka fad'a, amma kar a qara saka takalmin miji na"

"Sannu me miji, muma dai Allah ya aurar da mu"

"Ameeen ya Allah"

Sai ya maida abinda ya faru wasa, ya ajiye plate ya koma d'aki.

Bayan kwana biyu muna zaune da Maimunah a tsakar gida kowa na aikin da yake gaban shi yara na makaranta, se ga Ismail ya dawo daga wajen aiki, bayan ya mana sallama se ya shige ciki,mu ka ci gaba da aikin mu da hirar mu,se ga Isma'il da butar da Yah Maheer ke amfani da ita zai wuce mu ya shiga bayan gida, ban bata lokaci ba wajen amshe butar na ajiye gefe na ba tare da na ce masa komai ba,kallo na ya yi cikin jin haushi dan da alama a matse yake da koma menene ya koro shi gida, ni kuma na ci gaba da aiki na ban kula shi ba, k'wafa ya yi ya koma ya dakko butar su ya shige band'aki, muna zaune sai tusoshi muka ji suna fita da qarfin tsiya, nan fa muka dinga kokawar rugawa cikin d'akunan mu saboda kar ya ji dariyar mu, a guje na shiga parlour na na dinga zuba dariya, har da hawaye, se dariya zata tsaya se qarar tusa ta qara karad'e gidan, ina zaune a haka na jiyo motsin shi zai shigo parlourn kifa kaina na yi a hannun kujera ina kallon waje ta window fuskata ta yi jawur saboda dariyar da na sha ga kuma wata na neman kwace min, kallo na ya yi ya kad'a kai ya shige d'akin su ya rufe qofar da qarfi, wata mahaukaciyar dariya ce ta kwace min na kuwa bud'e murya na dinga dariya kamar zan yi yaya, bud'e qofar ya yi ya kalle ni kamar ze yi magana se kuma ya fasa, ya dau takalmin shi ya bar gidan, ni da Maimunah me za mu yi banda dariya, ranar haka muka wuni da mun tuna sai mun yi dariya.

A kwana a tashi sai ya fito da d'abi'ar kwashe min ruwa a drum, ba ya tashi wanka har sai an d'auke ruwan pampo, se idan ni ko yaran mun tara ruwa daga pampo sannan zai zo ya kwashe wanda aka tara ya ce zai wanka, ni kuma haka ne ba zan lamunta ba, duk randa ya bari aka d'auke ruwa be d'iba ba to fa ba zan bari ya kwashe wanda aka tara ba, domin kuwa idan ya kwashe zuwa yamma muka zo amfani da shi se fa yaran sun fita rijiya a waje sun samo ruwa, hakan da nake yi na rashin bari a taka ni se ya jawo min tsana wajen Isma'il.

Watarana mun gama tara ruwa ya na d'aki be fito ba har aka d'auke na pampo, na kuwa ce ba zai d'iba a drum ba, dan ko mu bamu gama d'iba ba aka d'auke ruwan, nan da nan ran shi ya b'aci ya hau bambamin masifa, na masa banza na ce ba dai zai d'iba ba, maimunah ce ta fito ta ce,

"Isma'il ka deb'i ruwan drum d'ina dama muna so mu kwashe a zuba wani"

Nan fa ya d'auki bokiti ya hau kwasan ruwan drum d'in Maimuna,tare da fad'in,

"Ke dai Allah ya tsunduma ki a aljannah ya sa oga ba zai maki kishiya ba, Allah ya maki albarka"

Ni kuma na ce,

"Ameeen in da gaske ka ke, in ma ka fad'a ne dan na ji haushi to ban ji ba, domin kuwa kullum ta Allah se miji na ya samin albarka ya min addu'a,kuma na ga aljannar nan dai ba kai za ka kira ni ka ce zo ki shiga ba balle ka hana ni, dan haka ka gama dad'in bakin ka kai ka sani"

Dariya ya yi ya d'auki bokitin shi ya wuce.

Haka rayuwa ta ci gaba da shurawa abubuwa da yawa na ta faruwa ciki har da sake ziyarar liman katagum da muka yi,da samun aikin Yah Maheer a wata sakandire da ke wani qauye mai suna Bura, bai fara zuwa ba a wannan lokacin saboda wasu abubuwa da yake so ya kammala kafin ya tafi d'in.

*****************************

Watarana ina zaune ina wanke wanke, gefe kuma na d'ora girki, gida kuwa na share shi qal ga qamshin turaren wuta ya na ta tashi, sanye nake da qananan kaya kamar kullum, sai na saka wani hijabi na kalar coffee me yadin roba, na shagala wajen wanke wanke na ji ana kwankwasa gida, sai na tashi na leqa ta 'yar bulin da ke jikin qofar shiga gidan, wani matashi na gani wanda na tabbatar da na tab'a ganin shi amma na manta a ina na tab'a ganin shi, bud'e qofar na yi na amsa sallamar shi,

"Barka da rana Aunty, Yayah ya na gida kuwa?"

Daga jin haka sai na fad'ad'a fara'a ta, nan take na tuna inda na tab'a ganin shi, qani ne ga Yah Maheer, d'an gidan qanin Baban Yah Maheer ne, hanya na bashi ya shiga ciki, na masa jagora har parlour sannan na shiga d'aki na d'aura zani saman dogon wandon da na saka.

Bayan na fito na shiga kitchen na duba abincin da na d'ora se na ga ya dahu, dafadukan shinkafa da waken da ya ji alayyahu da kifi na yi a ranar,ban koma wajen Safiyanu ba sai da na had'a masa abinci da abun sha sannan na kai masa, ina zaune mu na ta hira, na sake da shi kamar dama can na san shi dan kawai kar su ga banda sakin fuska,(tinda sun tab'a cewa fuska ta kamar ta shanu take da ina amarya se daga baya suka gane ashe ina da fara'a) maimunah ta ji ni shiru ban koma na ci gaba da wanke wanke ba ga rana ta kwalle, se ta doka sallama na amsa na fita,kallo na ta yi sannan ta yi qasa da murya ta ce,

"Ke Mahreen ki je ki qarasa wanke wanken ki mana, ga rana ta kwalle, ba fa haka ake yi ba, tinda kin kai masa abinci da ruwa sai ki je ki d'an qarasa aikin ki kafin nan ya gama cin abincin sai ki koma"

Dariya na yi sannan na shagwab'e fuska na ce,

"Yaayah Maimunah ranaaahh ni gaskiya bana so na shiga rana yanzu"

Qasan raina ina ganin rashin dacewar na tafi na bar baqo shi kad'ai, sannan na san a yanda Maimuna ke ji da ni zata taya ni wanke wanken, aikuwa kyale ni ta yi ta fice tsakar gida, ina ganin haka na sa dariya har da toshe baki, na tabbata wanke wanken zata qarasa min.

Ina komawa parlour kuwa na jiyo ta fara wanke wanken, murmushi na yi ina jin son matar har cikin raina.

Hira muka ci gaba da yi da Safiyanu ya na bani labarin mutanen Liman katagum,ina bashi labarin kanawa,a haka muka gama hirar mu ya tafi ba tare da ya had'u da kowa ba.

Bahaushe ya ce wai rashin sani ya fi dare duhu, a iya tunani na na qure gudu wajen kyautatawa Safiyanu, dan haka banga abinda na aikata masa ba na yi min sharri,ba tare da na sani ba Safiyanu ya tafi Liman Katagum a ranar, be tashi qulla min munafurci ba sai da yamma, manyan iyaye mata na gidan sun had'u ana cin abinci a bangaren su Yah Maheer ciki har da Maman suwaidatu da Isma'il da kuma Kakar Hauwa'u da nake riqo sai mahaifiyar shi.

Gefen su ya samu ya ja qaramin turmi ya zauna akai ya rafka uban tagumi tare da sauke ajiyar zuciya a jejjere,Maman su Suwaidatu ce ta kalle shi tace,

"Baffa Safiyanu lafiya ka zo ka sa mu a gaba ka zabga tagumi kamar raqumin ka ya b'ace a sahara?"

"Hummm ai Mama abinda na gani gwanda b'acewar raqumi a sahara da shi,"

Nan take kowa ta bashi hankalin ta, shi kuwa ya ci gaba da magana,

"Daga Bauchi nake wajen neman aikin polio d'innan da na ce maku ina nema, se na biya na je gidan Yah Maheer, wallahi su Suwaidatu da Hauwa'u su na shan wahala, kun ga a inda suke kwana kuwa? A dandaryar qasa suke kwana kai abun fa se wanda ya gani"

Allah ya zuba wa Mama son 'ya'ya,duk da halayya ce ta iyaye amma nata ya fita daban, nan take hankalin ta ya tashi ta ce bauchi zata, da kyar aka taushe ta akan ta bari se da safe ta zo.

Haka kuwa aka yi, ba tare da na san me ke faruwa ba, da sassafe na gama yi mana abun karyawa wanda ya kasance fanken da ake sanyawa nama da attaruhu da albasa se maggi da dan sugar kad'an na dafa baqin shayi kowa ya ci ya sha har ya ragu,se na deb'i wake na je tsakar gida dan na gyara da rana ina so na yi mana shinkafa da wake.

Na gama gyara wake na bushe zan shiga cikin gida Suwaidatu da ke tsaye saman d'an dutsen tsakar gidan ta daka tsalle ta d'ale baya na, ga hannu na da plate d'in wake, gashi ta shaqe wuyana da sunan na goya ta, ina tsaka da kokawar kwace kaina a hannun ta na ce,

"Kin san Allah in baki sake ni ba zan zane ki, kin shaqen wuya fa"

Ba zato ba tsammani muka ga an bud'e qofa sai ga Mama ta bayyana bakin ta dauke da sallama fuskar ta ba yabo ba fallasa, da sauri Suwaidatu ta saki wuyana ta ruga da gudu wajen Maman ta, ta na fad'in,

"Maamaaa Oyoyo ! Mama oyoyooo !!"

Da sauri nima na isa wajen ta ina mata sannu da zuwa cike da girmamawa, a haka na raka ta muka shiga cikin gidan har parlour, ban zauna ba sai da na deb'o mata fanken nan da na yi na had'o mata baqin shayi itama, sannan na zauna muka hau gaisawa, kallon mu kawai take da ni da Suwaidatu ta na so ta ga irin wahalar da 'yar ta ke sha, bata gani ba, ga yarinya nan tsaf,gashin ta ya sha kitso, domin hannu na ya karb'e ta nan da nan gashin ta ya cika ya yi tsaho saboda kula da shi da nake akai akai.

Ga ta nan fess dik da a lokacin ma ba mu yi wanka ba dikammu,babu wani alamun damuwa ko wahala a tattare da ita, ajiyar zuciya ta sauke sannan ta ce mana,

"Ina Yayan nasu ko ya fita aiki?"( Idan tace Yayan su Isma'il take nufi ba Yab Maheer ba dan shi da sunan shi take kiran shi kai tsaye bayan ya girme wa Isma'il da shekaru masu nisa, sannan dika yaran ta suna cewa Isma'il Yayammu, shi kuma Yah Maheer Yaya Maheer kamar shi ne qasa da Isma'il d'in)

"Ah ah ya na ciki, be d'au murya ba bari ta kirawo shi"

Kiran shi Suwaidatu ta yi bayan ya fito sun gaisa se na tafi d'aki na basu waje.

Isma'il be b'ata lokaci ba wajen qaryara Safiyanu se ya qara da cewar,

"Ni ne ma dai muke d'an takun saqa da ita, amma ba komai komai zai wuce watarana,"

Haka dai suka dinga magana ta a parlour na a cikin gidan aure na, ba tare da na sani ba, ina shiga sai akai shiru ta miqe ta ce tafiya zata yi ga wannan ta kawo mana, ina bud'a ledar na ga kuka, daddawa, quli, da tasoyu, (gyad'a me gishiri) godiya muka hau yi mata sannan ta tafi.

Ashe tsugunno bata qare min ba, dan kuwa gulmar Safiyanu ba anan ta tsaya ba har gidan Yayar Baban Hauwa'u da ta riqe ta kafin ni sai da ya je ya guntsa mata Hauwa'unta na can na shan wahala.

Itama ta niqi gari ta zo bauchi amma se bata zo wajena ba, ta yi zaman ta gidan qanin ta, sai da weekend ya yi Hauwa'u ta je ganin gida, sai ta tarar da goggon ta ta zo, Goggon ta dik ta duba komai da ya kamata ta duba bata ga wahala a tattare da 'yar ta ba, dan haka Hauwa'u na ninke kayan ta da ta je da su ta kalli Goggon ta ta ce mata,

"Goggo kin ga wannan kayan Aunty Mahreen ce ta bani su fa,har da wannan da wannan"

Gyara zama Goggon ta tayi ta kalle ta sosai sannan ta ce,

"Ni kam "yar Goggo (haka suke kiran ta) da gaske ne kuna shan wahala a wajen matar Maheer?"

"Goggo me ki ka gani?"

"Zuwa aka yi aka sanar da ni abinda ke faruwa shi yasa na kasa nutsuwa na ce se na zo na gan ki, se kuma na ke ta ganin sab'anin abunda aka sanar da ni"

"Lallai kam duk wanda ya ce maki ina shan wahala qarya yake, ki duba fa ki ga abubuwan da ta bani, ga girki yanzu da na iya,"

"Ance a parlour kuke kwana a qasa"

"To Goggo in bamu kwana a parlour ba d'aki zata shigar damu tinda d'akin d'aya ne? Kuma Goggo sabon bedsheet d'in ta me tsadar me laushi shi ta bamu muke kwana akai fa,wai ke Goggo wa ma ya fad'a maki wannan qaryar ne?"

Nan take ta sanar da Hauwa'u cewar Safiyanu ne ya je har gida ya sanar da ita, shine ta zo ta gani da idon ta, nan fa Hauwa'u ta zauna ta dinga sanar da ita yanda muke zaune da yanda na riqe su, tabbas idan suka min laifi ina zane su tasssss, sannan ina musu fad'a sosai in ta kama, amma baya hana in yi wasa da su, dan ina jin kaina da kad'an na fi su, hatta da 'yar carafke yi muke a parlour ko tsakar gida, har da 'yar gala gala muke zanawa da gawayi a tsakar gida mu yi.

Bayan Hauwa'u ta gama weekend d'in ta ta dawo take sanar da ni abinda ya faru, nan take Suwaidatu ma ta ce ai Safiyanu ne ya ce wa Mama tana shan wahala shi yasa ta zo ta gani, na yi ta kukan baqin ciki a ranar , na tuna yanda na tarbe shi da girmamawa da karramawa da kulawa, na tuna ko had'uwa ma da yaran beyi ba, me na masa na yi min sharri?

Tin daga ranar se Maman Suwaidatu ta qara qaimi wajen zuwa akai akai, har na shiga makarantar Wayar makafi dan ci gaba da Secondary school d'ina da ban qarasa ba, inda na had'u da mata nagartattu masu so na,a nan na had'u da qawata me abun dariya me suna 'yar Malam, (alkhairin Allah ya kai maki)

Ina nan ina zuwa makaranta ni da yaran cikin nasara ba wata damuwa,dake qarfe tara ake shiga makarantar dan haka kafin na fita sai na yi abincin safe da na rana, na gyara waje, wanke wanke ne kawai bana yi shima kuma watarana kan na dawo Addah ta min, watarana ma har girkin kafin na dawo ta d'ora min, idan ban bar abinda zan dafa a waje ba zata tabbatar ta gama nata abincin saboda na ci idan na dawo se na mana namu.

Haka rayuwa ta ci gaba da tafiya da dad'i da ba dad'i halayyar Isma'il na damu na, saboda kullum da sabon salon takalata fad'a da yake fitarwa, gashi idan sun min abu gaba d'ayan su har Abubakar d'in sai su yi sauri su sanar da Yah Maheer, saboda gani suke ko ina sanar da shi abubuwan da suke min dake shi ba me magana bane ya kyale su ne kawai ya na kallon su da abun,ni kuwa ba su san ban iya kan qara baz na fi qaunar duk wanda ya min abu ko wanene na tsayawa kai na, in sun sanar da shi shi kuma baya sanar da ni nan take,sai dai in muna kwance muna hira da dare sai ya ce,

'Baby na ni kuwa me ya had'a ki da wane? Na ga baku jituwa kamar da?'

'Wani abu aka ce maka na yi?'

'Ah ah tambaya ce kawai nake maki'

Anan zan zayyana masa komai ba tare da na yi ragi ko qari ba, ko da kuwa na banka rashin kunya to zan fad'a tinda ni aka fara tab'a wa sannan na maida martani, anan Yah Maheer ze sanar da ni dama sun fad'a masa ya na so ya ji daga baki na ne, watarana ya ce yanda na fad'a masa haka suka fad'a ko a samu sab'anin magana wanda daga wajen su ne dan kawai su kare kan su, haka zai ta bani hakuri ya na min nasiha, tare da tabbatar min dika rayuwar wani d'an lokaci ne qayyadadde dan haka na qara hakuri watarana sai labari, haka zan hakura na dole ba dan na so ba musamman in sun min qarya, dan na tsani a min qarya a rayuwa.

Bangaren Abubakar kuwa zaman mu muke lafiya ba tare da wata matsala ba, wanda ni ban sani ba ashe ta qarqashin qasa Abubakar shima na nan na zagi na a duk inda ya zauna ko ya samu dama, dake yana da wayo kuma baya so na ji se ya yi gulma ta ya san yanda ya danne kar na sani, ina zaune da su da zuciya d'aya ba tare da wani mugun nufi ba,a hankali na sanya wa zuciyata cewar duk abinda Isma'il yake mun zan na d'aukar shi kamar irin samun sab'anin nan da ake in zama ya kama ka da wani ba dan komai ba sai dan samun nutsuwar raina da kuma cire qiyayyar kowa a raina.

A hankali halayyar su ta fara min yawa ta yanda ba a wuce sati d'aya ba tare da mun samu sab'ani da su ba, har ta kai ta kawo shima Abubakar da ke b'oye qiyayya ta a ran shi ya fara bayyana min wasu halayen da ba su yi min dad'i sam a raina.

A hankali na zama masifaffiyar qarfi da yaji dan ni ban yarda ni da gidan aure na ba wasu su takura min har na rame ko na shiga damuwa da tashin hankali ba,sai ya zamana mun koma rayuwar kana yi min in mayar maka da me zafi.

Haka ne ya janyo watarana da rana bayan na dawo daga makaranta kwatsam sai na zuba wa kowa abinci na shiga wanka, ina fitowa daga wanka na yanke shawarar zan kwanta na huta, ban kammala sanya kaya na ba se ga Mama ta sallama ta zo, parlour ta wuce kai tsaye Suwaidatu da Isma'il da ke d'akin su sai suka fito akai ta hira, se da na gama shiryawa sannan na je, ga ba abinci na Hauwa'u ne kawai ya rage ita ba a lokacin take dawowa ba kowa na riga ta tashi daga makaranta.

Ruwan sha na kai wa Maman muka gaisa na tashi na basu waje kamar yanda na saba, na shiga d'aki na yi shimfid'a a qasa saboda zafin da ake,na yada pillow na sa a qasa na kwanta, ban jima da kwantawa ba na ji alamun tafiya da sand'a ana dosowa qofar d'aki na, shiruuuu na yi na luma kaina cikin pillow ina sauraren wanene me yi min sand'a, a hankali na bud'e ido na ta yanda zan dinga ganin me tahowa ba tare da ya yi zargin ido na biyu ba, ai kuwa ba a jima ba sai na ga inuwar mutum a saman kaina..............

Mutanen k'warai masu albarka in an karanta sai a dangwala min yatsa a star din nan hilis...sannan a Yi sharing da abukkai....se a zuba sharhi saboda shine taki na... love 💕 all.

Continue Reading

You'll Also Like

843K 8.4K 68
๐ข๐ง๐œ๐ฅ๐ฎ๐๐ž๐ฌ ๐š๐ฅ๐ฅ ๐จ๐Ÿ ๐ญ๐ก๐ž ๐›๐จ๐ฒ๐ฌ โœฆ . ใ€€โบ ใ€€ . โœฆ . ใ€€โบ ใ€€ . โœฆ don't forget to vote, share and comment. ๐Ÿค
10.2M 640K 168
What will happen when an innocent girl gets trapped in the clutches of a devil mafia? This is the story of Rishabh and Anokhi. Anokhi's life is as...
192K 14.7K 47
[Under editing]* "Charche nashe ke chal rahe the main zikr teri aankhon ka kr aaya, jab baat sukoon ki chidi main baat...
119K 15.8K 34
#Book-3 Last book of Hidden Marriage Series. ๐Ÿ”ฅโค๏ธ This book is the continuation of the first and second book "Hidden Marriage - Amazing Husband." If...