page 1

132 4 0
                                    

https://chat.whatsapp.com/DgTUlodRcp2AHM4rmfKTqK

KISWAH

(Linked through surrogacy).

Na CHUCHUJAY ✍️

Book 1⃣

Episode 1⃣

A/N

Assalamu Alaikum masoyana abun alfahari na,Fatan na sameku cikin koshin lafiya ,

Ina kaunarku a koda yaushe kuma bazan daina ba domin kuwa Allah ne ya haɗa ni daku wanda ba yine 'na mutum ba,

Ina rubutu kuna kaunarsa sannan kuna bani kwarin gwiwa wajen so da yaba abunda 'na rubuta,😪ni ba kowa bace idan Babu ku ❤.

So yarda Allah ya bani ikon haɗa Littafin AURE UKU da AHALINA ina Addu'ar 'ya ara mana rayuwa da lafiya domin kawo muku wannan littafi nawa Na KISWAH(Surrogacy was the cause ) amma a wannan zagayyen tafiyar ta dabance domin kuwa littafin 'ya kasu kashi biyu ma'ana book 1&2

,book 1 zai zo maku kyauta ne book two kuma na kuɗi,kamar yarda na nishaɗantar daku a series biyu da 'ya gabata ina fatan nima zaku nishaɗantar dani da beautiful sales na wannan littafin Na KISWA,kilan kin taba ko ka taba jin story line ɗin kilan kuma wannan ne na farkon ka,abu guda ɗaya na sani wanda shine ,insha Allahu zai ilimantar,zai nishaɗantar .

Na sake faɗa Book two 'na kuɗi ne kar ki fara karantashi ya katse kiji haushina akan bance 'na kuɗi bane saida mutum ya fara' thats what happpend a Abla Adnan amma insha Allahu zaizo muku akan farashi mai sauki cos biyan zai zo da tsari,iya kudinka iya shagalinka❤

  TSOKACI.

◽Surrogacy Wani method ne da turawa suka kirkira wanda idan ma'aurata biyu na san haihuwa misali idan ɗaya daga cikin ma'auratan bazai iya haihuwa ba ko kuma matar bata san ta haihu ɗin sai su samo wadda za'a sakawa Maniyi na mauratan biyu,da taimakon technology zasuyi developing ciki jikin Matar da wannan halittar samun ciki na Ma'aurata biyu,

Surrogate mother ɗin zata masu rainan cikin ta haife ta basu abunsu wanda shi yasa a kasashen yahudu surrogate mothers suna nan aikinsu ne iyakacin su haifa maka su baka abunka aikinsu 'ya gama kenan,wannan kana ji aikine na nasara domin kuwa Musulunci yayi Allah wadai da wannan tsari,sannan baya da gurbi ko waje ko wata ɗauraya a addinin Islama.

Wannan kenan.

       DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAI JIN KAI.

Ko wanne ɗan Adam dake numfashi a rayuwa An haliccesa ne sannan aka rubuta masu ƙaddararsa sai dai yiyuwarta da wanzuwarta a lokacin rayuwa domin kuwa sai tazo kuma sai ta faru jira ne kawai bawa ke yi,

A haka rayuwa da ƙaddarar KISWAH UBAID ke tafiya a rubuce cikin tsari da godiyar Allah domin kuwa duk wani musulmi na ƙawarai yana daga cikin Imaninsa 'ya yarda da ƙaddara wala mai kyau ko kuwa akasinta ,

Iyayen KISWA biyu Malam UBAID da Zubaida ,Mutane yan asalin jihar Bauchi,a rayuwar Aurensu sun jima basu samu rabo ba domin rabon nasu na chan nesa,Zubaida bata samu ciki da mijinta ba har sai da suka shekara huɗu da Aure ,a lokacin kuwa da sanin cikin ya ziyarci Malam UBAID ba ƙaramun mirna yayi ba da farin ciki domin kuwa yana mutuƙar kaunar Ace yau zubaidarsa ta basa Farin cikinsa wanda shine ganin yaronsa ko yarinyarsa a hannunta.

    A lokacin da Ya samu labarin cikin kamar ya zuba ruwa a ƙasa yasha dan murna,idan kuwa ka haɗu dashi a wannan rana To tabbas sai yayi maka ihsani saboda wanda ubangiji yayi masa.

Mutane da dama kan faɗi masa maganganu iri iri akan rashin samun cikin Zubaida dan harda masu ce masa rashin haihuwa Ya saka mijinta na farko sakinta domin bashine Ya fara Aurenta ba a bazawara Ya Aurenta,

KISWAH 1✔Where stories live. Discover now