Murmushi Ammah tace " I always want you to be happy Asmah Allah ya kiyaye hanya ,go and prepare your luggage ".A wani medium Luggage ta shirya kayan ta ta saka kayan a gaba tana ta kallon su Murmushi yana subce Mata yau dream dinta ze tabbata,she can't believe it .

Rik'o hannun Samad Momy tayi tace "Me kake nufi da ka fasa auran Asmah?K'ananun mutane kakeson ka maidamu?meyasa In zakayi abu baka tunani Sammad "

"Yess Momy na fasa auren ta ".
"Saboda me "?
Momy ta daka mishi tsawa
Atsawace yace "Haka naga Dama Momy please can you leave me alone ? Nace na fasa aurenta saboda batada tarbiya and so fucking what "?
Marin da Mamy ta kiifa masa a lafiyayen fatan sa ne yasa yayi shiru batare da ya Karasa ba ,huci kawai yake fitarwa kamar zakin dayasha kasa .
"Bazanyi tolerating stupidity Dinka ba Sammad am tired na gaji da halinka da kai da mahaifin naka da yake daure maka k'ugu kake abunda kaga dama and lastly kaji tsoron Allah.alhakin 'Yayan mutanen da ka cuta baze barka kayi surviving lafiya ba ".
Hannun Fattu Taja da take zubar da hawayen tausayin Asmah da kuma kunyar ta ,Seda suka haura stairs sannan Momy ta saki hannun ta hawaye na taruwa a idonta
Kaiconta! Kaiconta ! Wannan wani irin rayuwa ne Allah ya jarabceta da ita yaron ta a duniya babu wanda yake shakka kuma yake tsoro duk abunda yake so shi yake aikatawa babu wanda ya isa ya hanashi,Mahaifin sa na ganin wannana a matsayin soyayyah besan yana jefa rayuwar danshi acikin rami bane,besan yana saka danshi acikin halin k'ak'anik'ayi ba .
Duk wani abunda Sammad zeyi awurin Mahaifin shi daidai ne,itada take mahaifi Yar shi batada katab'us se abunda ubanshi ya zartar,
Durkushewa tayi awurin tana daga hannunta sama hawaye na zubo Mata cike da rauni da tausayin rayuwar danta tace "Ya Allah ka shirya Sammad ka ganar dashi gaskiya dashi da Mahaifin shi ,Ya Allah karkasa ya mutu yana aikata kuskuren da yakeyi ayanxu ,Ya Allah kaga zuciyata nayi iya bakin kokarina na kasa shawo kan alamarin nan ,Kaine maji rokon bayanka Allah ka amsamin dua'ina Allah ka daura min su atafarki madaidaici ".
Da sauri Fattu ta dukusa kusa da ita tana riko hannunta "Momy kiyi hakuri komai me wucewa ne insha Allah Ya Sammad ze gane gaskiya ,ni abunda yafi damuna Momy da wani ido zan kalli Asmah,yayana mafi soyuwa agareni ya yaudareta ni nasan Asmah bazata taba aikata abunda yake fada ba,tun lokacin dayace min yana sonta nayi iya kokarina naganin hakan be faru ba saboda banso abunda yakewa sauran mata itama ya gwada Mata amman abun yaci tura Momy duk laifina ne "
Ta karashe tana sakin wani sabon kukan.
Rarashinta Momy ta farayi tana nusar da ita shi komai arayuwa muqaddari ne daga ubangiji,kuma bawa baya tsallake kaddarar sa duk abunda ubangijin talikai ya tsarawa mutum babu makawa seya sameshi,Allah yayi duk abunda ya faru seya faru .

Da daddare wurin 9 Noorain yazo gidan .Har cikin parlour ya shiga ya tarar dasu duka a zaune Sosai fuskan Ammah ya kara washewa ganin Noorain,sosai mutuncin shi da kimar shi suka ninku a idanunta bazata taba mantawa Da wanda ya ceci rayuwar 'yarta ba ,Noorain ya taka muhimmiyar rawa
Gaisheda Ammah yayi fuskan shi Adan sake ta amsa da faararta tana mishi bangajiya,sosai yaji kunya yace Mata "Ammah babu komai Asmah kamar Su Nabila take a wurina kome na mata ban fadi ba "
Gyada kai Ammah tayi taji dadin maganar sa sosai tace "Hakane Noorain Nagode sosai Allah ya kara zumunci "
Da Amin ya amsa yana sunkuyar da kanshi ,daya bayan daya suka gaishesa sabida Kaf cikin su babu saansa adacan ma suna mishi kallon me girman kai amman yanzu sun gane ba hakan bane rashin fahimta ne kawai .
"Bara a kira maka Asmah "
Da sauri ya dago yana kallon Ammah yace "Ammah ba se an kira taba kawai nazo duba jikin ta ne "
Duk da idanuwansa suna kwadayin ganinta , amman bayaso ya daurawa kansa abunda yasan ba samu zeyi ba .
"Aa ka bari a kirata din gobe zasuje Maldives kuma zasu dan kwana biyu itada Yayan ta ".
Gyada kai yana cewa "Allah ya tsare hanya "
Kafin ya gama magana ta fito sanye da doguwar riga Nude colour se kuma veil din da ta rufe kanta dashi
Tana zama Ammah ta tashi ta shiga dakin ta , Kallon kasan idanu yake Binta dashi ,ji yake kamar ya dauketa ya gudu da ita ta mishi kyau ba kadan ba .
"Ina wuni ya Noorain "
Ta fada da sanyayen Muryanta me cike da yarinta .
"Lafiya lau Ya jikin naki "
"Alhamdullilah,Nagode sosai Allah ya saka da alkhairi "
Murmushin gefen baki yayi yace "You deserve More Allah ya kara lafiya "
Amin tace tana kara sunkuyar da kanta ,duk da kasancewar shi Miskili bamason magana ba hakan nan ya tsinci kanshi da ce Mata "Ammah tace you're going to Maldives tomorrow "!
Gyada kai tayi tace "Eh my brothers suprise me , basason na saka damuwar fasa aurena da akayi shiyasa sukayi deciding Haka kuma am so Happy with them ".
A zabure Noorain ya dago jin abundata fada "Fasa aure "?
Ya nanata a zuciyar shi "Auren ki aka fasa Asmah "
Hawayen da ke shirin zubo Mata ta share tace "Eh Sammad ya fasa aurena am no more important "
Tayi matukar kokari wajen Hana kanta kuka so take ta bawa kanta hope she can't continue living like this barinshi rayuwarta ai ba shi yake nufin tata rayuwar tazo karshe ba ,yana can yana farin cikin shi bayan ya zalumce ta Dan haka ita daya zalunta bazata hana kanta walwala ba saboda shi ,he didn't deserve this .
Sosai Noorain ya kadu dajin maganar Asmah ,ya kuma tausaya Mata ,as she is young dinan this situation is very high for her ."Allah yasa hakane mafi alkhairi dont bother your self Allah ze kawo mafita insha Allah "
Jingina kai tayi tace "Thank you Amin "
Wani babban Leda ya Mika mata yace "Take this "
Dagowa tayi tana Dan kallon shi tace "Noo "
Harara ya Mata yace "Common My friend "
Babu yanda ta iya ganin yanda ya tsare ta da ido yasa dole ta amsa tana mishi godiya , seda yaga shigarta sannan ya fita .
"No karki damu Ni'ima ,she is safe muma dai abunda ta fada mana kenan tunda Allah ya kawota gida lafiya shikenan ,karki damu basekin zo ba "
Daga can bangaren Anty Ni'ima tace "Wallahi banji dadi ba Anty amman insha Allah ina tafe dole zanzo na duba Asmah nah my regard to her inata kiran number ta ma a kashe "
"Eh wayan nata ya fadi amman Hammad ze siya mata wani gobe "
"Toh agaisheta Nagode "
"Toh madallah agaida yara "

Sallama sukayi Ammah ta ajiye wayar tana bin Hannun Asmah da kallo ajiyewa tayi tace "Ya Noorain ya kawomin "
Sauke numfashi tayi tace "Baya gajiya kin mishi godiya ba "
Murmushi Tayi tace "Eh Ammah "
"Good girl "
A kan gadon Ammah ta kwanta tana cewa "Ammah gobe by now bana nan I will missed "
Tabe baki Ammah tayi tace "Kinje Maldives dai nasan bazakiyi missing kowa ba "
Dariya ta kyalkyale dashi tace "Allah Ammah I will missed you "
"We shall see "
Hira suka cigaba dayi har tayi bacci .
Washe gari wurin 11 Ammah ta tashe ta saboda jirginsu by 1 ze tashi ,Seda ta fara gyara gadon Ammah sannan ta wuce dakin ta , wanka ta shiga ta dade tana gurxa jikinta tana waka ,bayan fitowarta ta dade a gaban mirror tana shafe shafe seda Ammah ta turo Bilkisu tace "Wai ko ta fasa zuwa ne sunata jiranta "
Da sauri ta tashi tana kallon Bilkisu tace "Haba billy "
Dariya Billy tayi ta fita tana cewa sakon Ammah ne.
Babban Closet dinta ta nufa da sauri tana zugewa ,Jeans ta ciro sky blue ta zura ya Mata cif a jikinta ta kasan kuma ya tsuke sosai ga Dan tsaga kadan ,se wani t shirt da ta saka me blue da pink ajiki wanda yazo mata har cinyar ta ,veil ta zaro sky blue ta daura akanta ta xiro ragowan ta gaba hat ta daukko shima a side dinsu pink ta daura akanta se ta saka talakmi plat black . Sosai shigan yayi mata kyau ya haskata , turare ta fesa ta zari jakarta ajikin bag hangers ta fito , Kallon ta Ammah tayi tace "You look beautiful my girl "
Peck tayiwa Ammah a Kumatu tace "Thank you Ammah "
Kallonta Ansar yayi yace "Yan matan Ammah "
Fari ta mushi da ido tace ya son ranka . Dariya sukayi gaba daya Ammah ta kira billy ta kawo mata breakfast dinta sharp sharp ta faracin abuncin saboda 12 ta wuce .
Bata wani jimaba suka fito har parking space Ammah ta rakosu tana kara ja musu kunne su kular Mata da 'yarta karta jii karta gani .
Har suka fita Tana waving Ammah .

The journey is staying now don't forget the book is paid just 500 call or chart me via 08100312134.love you all .

ALAQAR MUWhere stories live. Discover now