free page 3-4

30 1 0
                                    

Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/Hjo66unukKI8zkrQwHEAzp

🖤🖤🖤🖤🖤🖤🖤🖤🖤🖤

       🩸 *AKWAI DUHU*🩸

🖤🖤🖤🖤🖤🖤🖤🖤🖤🖤


*STORY/WRITTEN BY.*✍🏻

   _KHADEEJAH SANI JOURNALIST._

_*AKWAI DUHU* ba free book bane na kuɗi ne #150 ta acct idan kati ne mtn na #200, biya kuɗin karatunki ta wannan asusun bankin 0270983859 Khadija sani umar Gt'bank sai ki turo shaidar biyanki ta wannan lambar 07067750885 ko ki turo hoton kati ta lambar amma banda vtu dan Allah_

*بسم الله الرحمن الرحيم*
*____________________________________*

*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
'''{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}'''
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation

*domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan*👇🏻

https://bakandamiya.com/group/71/kainuwa-writers-association

*____________________________________*
°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
*MARUBUCIYAR.*
_RASHIN UWA._
_RAYUWAR GIDAN KAWUNA._
_KALAR TAWA KADDARAR._
_RAYUWATA CE HAKA._
_KOMAI NUFIN ALLAH NE._
_DEEN NA DEENA NE_
_GAMSHEƘA PAID BOOK #200._

   🖤🖤🖤🖤🖤

🅿️ree 🅿️age *3-4.*


  Bayan nagama duk aikin da zanyi na koma daki na kwanta,

Ban Dade da kwanciya ba bacci da daukeni cikin baccin naji Mami na kirana bude Ido nayi da sauri na ganta a tsaye tana fadin

"Sannu hakima wato kinzo kin kwanta nice zan dafa abincin rana ko saboda kin ajiyeni to wallahi inaso ki sani duk wani aikin dake gidan nan kece Mai yinsa nadaina yin komai Kuma kisani nakira ladi Mai aiki nace karta dawo tunda gaki agidan azaune wallahi mundaina asarar kudi ai zama kikace kinaso muyi ko to muzuba dake aga Wanda zaigaki"

mikewa zaune nayi Raina duk ya baci na kalli mami nace

"Mami yanzu fa nagama wanke wanke Kuma naga lokacin Dora abincin baiyiba shiyasa na kwanta kaina ke ciwo"

"Koma meke ciwo babu ruwana tashi ki wuce kifita kije kiyi gyaran dakina da falo sannan kiyimin wankin da yadan taru kafin lokacin Dora abincin yayi ai kindaina hutawa a gidan nan Indai bazakiyi abinda mukace miki munaso ba wallahi"

Kuka nafara yi tare da sakkowa daga gadon nayi waje,

Haka nagama gyaran falon nashiga bedroom din Mami itama na gayara sannan na koma bayan gida nafara wankin da Mami ta hadamin,

Duk aikin da nakeyi Ina hawaye nake yinsa dama haka akeyi don kawai Allah Bai kawomin mijin aure ba sai abi a tsangwame ni a takura min ahanani sakat acikin gidanmu,

Cikin zuciya ta nafara kokwanton Anya Mami ce ta haifeni duba da yadda takemin dama tun can baya batason yadda Abie ke lallabani akan Abu,

Magana kadan sai tafara yimin fada wani lokacin harda duka don daima yanzu ya Hana dukana,

Bayan nagama wankin na dawo kitchen na Dora abincin rana,

Haka na yini a gidan ranar babu wani sukuni duk jikina Banda ciwo babu abinda yakeyi don nidai rabona da nayi wanki haka harna manta,

Washegari natashi da zazzabi Mai zafi don tun cikin dare nake jinsa sama sama Amma zuwa asuba da kyar natashi nayi sallah,

Rauda ce tabani magani nasha na kwanta sannan ta fita a kitchen ta sami Mami Nan ta fada mata cewar bani da lafiya da zazzabi na kwana,

AKWAI DUHUWo Geschichten leben. Entdecke jetzt