MAH~NOOR🌹

By AfricanQueen300

87.2K 8.2K 1.3K

Free book I grew up with this, I had best friends became enemies and then best friends again. I love it now... More

Prologue
destinations
Welcome to Hamoud Boualem Company...
Meet Mr Hot Guy
She take my position
Hamoud Boualem Family
Promotion
Personal information
Sisterhood
Big Mistake
Dreams
Interview
MR Arrogant
hateatfirstsight
My Nikkab
The Name
hypocrisy
Kidnapped
Escape
Injured
Exclusively
Approched
Mine
My Favorite
Silent
You are my Destiny
i'm in luv
Contract Marriage
Confessing
Bonus page
Tracking
stupidly
Chased Game
The Game is Over..
My wife...
Hopefully
Am sorry
Other side
The Family
Faruq
Happy end.... Mr And Mrs Mahir Hamoud Boualem
Lover

Courage

1.7K 173 26
By AfricanQueen300

https://my.w.tt/Ewo0CLV9ccb
MAH~NOOR✧✧
   My First Wife♡
        Chapter 1️⃣4️⃣
     MrsUsman400
Free book 🤩
For You Jikar kulu

BISMILLAH RAHAMANI RAHEEM

  ~#Courage~

"Sai na lalata maka duk wani ji kanka!" Ta faɗa cikin karfin hali.
"Duk ranar da kika yi nasarar haka, na miki alƙawarin, sai na baki mamaki a rayuwarki balle poor girl like you, me zata iya min. Me zaki iya? Cigaba da Rubutu."
"Mahir! Sai nayi destroye nasarar ka da ka gina."
"Ni kuma na zame miki karfen kafa, duk inda kika shiga sai na hana ki sukuni, ke me gadin kamfanina baki isa tab'a kimar shi ba, balle kuma Dolna dan karen da ake kiwo."

       Har biyar suna muhawara, tare da kudirin abinda zasu aikatawa junar su, ana tashi ta zubda takardun, sannan ta sauke ajiyar zuciya, me tafe da kuka. Dan bata jin zata iya motsa legs din ta..
       ......
    , ya kirga takardun yaga bata yi wani dayawa ba, amma sun jike da kwalla tare da gumi, table baki yayi sannan ya d'aga kafad'arshi.
"Gobe daga farko zaki fara!"
"Idan ka ganni anan kenan, sai kayi abinda yayi maka dan ni ba gantalalliya bace da zan zauna ka kashe ni a iska,mugu kawai."
Ta juya da sauri tana jan kafarta, zuwa bakin kofar.
Yana zuwa bai damu da yadda take bin bango ba, ya sharbeta ta zube.
"Zan so ki kira ni da Boss."
"Wallahi da na kiraka da boss gwara na rasa harshe na."
"Yau daya kin sani nayi magana da yawa."
Ya faɗa tare da lashe bushashen lips d'inshi, sannan ya taka kafarta, sai da ta sake ƙara,.tare da rike kafar tana yarfe hannun, haka ya fice tare da rufe ta a cikin office din, yayi tafiyar shi.

          Domin shi bai san bata fito ba, dan ya san zata mike, kuma kofar tana iya tsayuwar minti biyar idan babu wanda ya gifta sai ta  rufe kanta, tashi tayi zata fita kofar taki budewa. Cire nikkab din da hijab ɗinta ta sake kuka. Sai da tayi ya ishe ta, sannan ta mike tare da shiga niman wayarta, ta samu, tayi kokarin kiran Tasleem, amma bata dauka ba, tayi iyaka kokarinta amma bata dauka ba, karshe ma wayar a kashe. Kamar yarinya karama haka tayi ta kuka tana ja mishi Allah ya isa.

        Shiga dakin tayi ta duba taga har da bowl tub, da sauri ta cire kayanta tare da cika  ruwan zafi ta shiga cikin ruwan, dogon gashin kanta, wanda ya kasance baƙi na asalin larabawa da fulanin asali ta sauka a jikin tub din, bata cika son jika gashin ta ba,idan bai zama dole ba,  wanka tayi tare da fasa kafarta, sannan ta fito daure da towel, a hankali ta fito, dake ta kwaso kayanta a Office din.

      Tana jin ana magana sama sama.
"Kasan ba zai tab'a saka hannu ba, me yasa kace nazo Office din shi?" Shiru aka yi dan ba zata ce tasan mutane ba, sake lek'awa tayi bata ga fuskar su ba, domin akwai abu a rufe a fuskar su,
Haka suka gama abunda ya kawo su, suka fita.
Da sauri ta saka kayanta, sannan tayi maza ta fito, saura  minti ɗaya kofar ta rufe kanta ta sami damar fita. Kusan rabin kamfanin wutar a kashe yake, dan haka nake tafiya a hankali, hango wasu manyan police dog nayi ban san lokacin da na dawo da gudu ba, na bakin kofar na danna makulin,.yana budewa na koma cikin office din da gudu zuciyata tana rawa. Ubangiji ya daura min tsoron kare wallahi. Dan haka na koma gwada kiran Tasleem wayar a kashe, sannan banyi saving Number nazzir ba, Badar kuma na kira yana busy.

            A hankali na shiga duba dube, a cikin office din shi, anan na kuma hango wata kofa, ta inda kujerar shi yake, tab'a inda nake tunanin shine Mabudin nayi na ga kofar ya buɗe, a hankali na fito, gurin shakatawa ne ko  hade da yar karaman hot tub, sai bar da yake gurin, a hankali na isa inda nake jin hayaniyar mutane, taka abu nayi na saka yar karamar camerar da Badar ya bani na shiga daukar su,  ina gamawa.

Na dawo dakin na kuma zama nazarci ɗaukar. Sannan na cigaba da Niman hanyar da zata kai Ni cikin part din, leka katangar nayi naga a shirye yake da Kwalba, tsaki nayi na sauka kasa, cikin yawon da nake na hango wani katon rariya, da zai kai ka har cikin wancan side din, a hankali na rarrafa har cikin gurin, na shiga bin ko ina ina daukar hoto, da video har zuwa cikin, inda shima na shiga ne ta kofar baya, ina gama abinda Zanyi na koma fitowa ta wannan rariyar, na koma Office din shi, shiru nayi ina nazarin kamar na ga wani katon lambatu. Da sauri na kuma hada kayana, na fito na shiga bin hanyar, ta karka shin kasa kwatar dakatar na fito babban hanyar kamfanin, anan na samu damar kiran Badar tare da gaya mishi inda nake, lokacin sha daya na dare, da kanshi yazo ya dauke ni.
"Noorh! Sannu. Kinyi aikin da na gaza yi, gashi kin dauko wani shashi na Abinda yake faruwa. Gaskiya nagode sosai."

"Ni yanzun ka barni na gaji, gida zaka ajiye ni, Amma wallahi sai na gwadawa Mahir ni yar halak ce."

   "Kinga don Allah ki ajiye wannan rigimar, mu  fuskanci abinda yake gaban mu.".
       Lumshe idanun yayi tare da jin zunzurutun k'iyayyar Mahir, yana kuma samun mafakar siyasa a zuciyata, sai na gwada mishi iyakar shi."

      "Noorh ki rabu da mahir!"
"Wallahi ba zan rabu dashi ba, sai na wulakanta shi a garin nan, wannan kamfanin sai na tsayar da kome na shi." Ta faɗa dai dai isar su kofar gidan su.

Fita tayi abunta, tare da buga kofar gidan, me gadi ya bude min na shiga, ina isa bakin kofar na sami Tasleem a zaune, shareta nayi na wuce abuna, dan na fahimci da gayya ta rufe wayarta.

      Ina isa bakin kofar mu, Dad yace.
" Ba zaki janyo min abun kunya ba idan kin gama service ɗinkin koma Bisra, ban ce mishi kome ba nayi wucewa d'akin mu, Sallah isha nayi sannan na Kwanta, sai lokacin Tasleem ta shigo itama ta Kwanta, ya zata kowa gantalalle ne irin ta, ta shiga min magana a hankali tare da tambayana.
"Ba dai kema kinyi losing virginity dinki ba?" Ta faɗa tare da kallona.
"Au wannan shine tunanin ku  a kaina? Hmm. Ni ba ballagaza bace na san inda nake dariya, sannan ba a haifi namijin da zai karb'an daraja ba, domin Ni nasan ciwon shi, kuma nasan darajar shi.

         Balle kuma da na fito a kabilu guda biyu, da suka san kimar shi ba zan tab'a watsi da al'adar mu da addinin mu ba."
.daga haka tayi juyawarta kamar ta da bayan ta suke mata ciwo.

           ---
Washi gari tana idar da sallah asuba. Ta koma abinta, har karfe bakwai Tasleem ta shirya bata ko d'aga kai ba, domin zazzaɓi yake damunta.

        Karshe da taga Noorh bata mata magana ba, shine ta tab'a tare da cewa.
"Ba zaki bane?"
"A'a Babu inda zani!"

        ....
A can kamfanin kuwa, hankalin shi kwance, ya shiga cikin office din shi, yana bin ko ina da kallo. Murmushi yayi tare da isa dakin shi , gadon da yake yatsine ya kalla, yana nazarin can kuma ya tuna ai ya kwanta. Amma me yasa ba a gyara dakin ba,.dan haka ya fita tare da danna bell din da zai kira masu aikin part din su.

         Dukkan su, suka shigo Cigaba yayi da aikin shi, tunda suka ga haka, jikin su yayi sanyi. Zai yi wuya idan ba koran su zai yi ba.

       "Yallabai!"
"Malam Abba! Kaje na baka hutun sati biyu"ya faɗa.

       "Don Allah kayi hakuri, wallahi ina da yara ƙanana." D'ago kan shi yayi, yagan su duk manyan ne, ba yara ba, sunkuyar da kai yayi sannan yace.
"Kuje! Amma kusami Nazzir, zai baku sako, wannan lokaci kamata yayi ku koma gefe kuna tare da kasuwanci wannan aikin ƙarfi ne, kuma shekaru yaja."

Ya fadi haka yana isowa gaban su, ya arde hannun shi a kirji, "karku damu, zan bawa Nazzir damar ya sallame ku da kyau."

    Daga haka ya wuce dakin, da kanshi ya gyara d'akin, tsaf ya goge. A ban dakin ne ya hango ribom din mace.
Cikin wani irin mamaki yake kallon ribom ɗin.

     Dauka yayi ya fito daga ban dakin, sannan ya koma Office din shi.  Ajiye kome yayi yana jiran jakar shi tazo.

      Bata zo ba shima kuma bai saka kanshi damuwa ba, ana tashi ya tattara yayi gaba abinshi.

   ---
Karfe biyu na rana, ta shirya zuwa kasuwa, anan ta samo yar karamar wayarta, me kyau, amma androind. Kuma ta hannu ce, tana isa gida ta daura layin da ta saya, a hannun irin masu sayar da kati suna tafiya.

   Dake mtn ne, take tayi transf din data, ta tura face book, da tweeter, tare da IG.
Sunanta da take amfani da shi a wancan wayar ta sauya, tare da bude har da Gmail.

Tana gyara face book ɗinta, tare da tweeter ta fara rubuce-rubuce akan kamfanin Hamoud Boualem da CEO din su, sosai tayi magana akan wulakanta mutane da yake, tare da yunkurin fyade ga yar bautar ƙasa.
         Sannan tayi alkawari sai ta bayyana musu, sharrin da Kamfanin yake dauke dashi wanda mutane basu sani! Sannan ya kamata mahukunta tare da gwamnatin! Jahar Adamawa! Gwamnatin tarayya! Hukumar lafiya ta jahar Adamawa, da ta kasa baki daya su shiga alamarin kamfanin Hamoud Boualem Company, sannan Tana kira da Malaman musulinci da na Kirista su fito suyi wani abu akan kamfanin Hamoud Boualem, sabida rashin amana da suke yi ga kamfanin.! Idan kuma ana kalubantar ta, toh ita taji zata bada shaida ga abinda idanun ta suka gani! Amma na farko hukumar yan bautar ƙasa, suyi da gaske domin daya daga cikin mutanen su, rayuwarta yana cikin hatsari sakamakon yadda CEO yake niman kashe, karku ce kashe kai ne idan haka ya faru, aka kisan kai ne! Domin bai dauki rayuwar kowa da daraja ba. Sai tashi.

          Sannan a musulunce dai an san giya haramun ne? Toh ya kamata hukumar hani da fataucin miyagun kwayoyi na kasar da jahar Adamawa, su fito su kalubalanci Hamoud Boualem, idan since karya ne, ita tana da shaida.

         Sannan zunzurutun rashin adalci, koran ma'aikata ba bisa ka'ida ba, ana cin zarafin su. A kamfanin Hamoud Boualem, ya ta'azzara. Abubuwan na cin mutuncin sai da Noorh ta rubuta, akan kamfanin Hamoud Boualem, sannan ta kuma jaddada bayanin akan wahalar da Mahir ya bata, ta hanyar kare sunanta. Sannan ta sake sakon tare da sake murmushin jin dadi.

         Bakuwa ce a tweeter, kafin kace me. An shiga watsawa a kafaffen sadarwan zamani. Tare da ririta alamarin ya girmama..

       (Matsala ta da fada da dan jarida! Mawaki! marubuci! Dan wasan kwaikwayo! Alqur'an suna tashi maka gwanjo sai ka ƙasa b'oya a duniya!)
Yarinya kiyi fatar kar Mahir Hamoud Boualem yasan kece kika mishi wannan daurin goron, dan shi talala zai miki!

_Zaku ji ni shiru na wasu kwanaki Insha Allah! Haka zai faru ne sabida uzurin da ya taso min! Don Allah karku zarge ni da wulakancin_

Continue Reading

You'll Also Like

404K 41.7K 23
انا العاصفة الحمراء ألتي تراهن وتربح انا القوة العظيمة الذي سوف تنهك كُل الارواح الجنون والتلاعب بحد ذاته هنا أستطيع ان اتلاعب بعقلك حَد الجنون امر...
222K 19.4K 27
Maybe sometimes love needs a second chance because it was not ready for the first time 🥀... Ekansh Malohtra a youngest buisness tycoon (28).. A man...
170K 7K 34
အဖိုး လက်ထပ်ပေးခဲ့တဲ့ အိမ်ထောင်ရေးက တည်မြဲပါ့မလား ဂျစ်ကန်ကန် ကောင်မလေးနဲ့ ဆရာ၀န်မမတို့ရဲ့ အလွဲများစွာ....
125K 8.9K 64
ရယ်စေ၊ မောစေ အသက်ရှည်စေ ဟာသနှော၍ ရယ်မောပျော်ရွှင်စေရန်အလို့ငှာ လုလင်မောင်မောင်(ပစ်တိုင်းထောင်) နေမင်းပုည(ရွှေဒင်္ဂါး) (Own Creation) Starting Date...