ƘAWATA CE

By Oum_Nass

1.6K 189 20

Labari ne akan ƙawaye biyu masu halayya ɗaya! Labarin sadaukarwa a inda bata kamata ba! Ƙauna marar algus! Ya... More

SHIMFIƊA
FITA TA BIYU
FITA TA UKU
FITA TA BIYAR
FITA TA HUƊU
FITA TA SHIDA
FITA TA BAKWAI
FITA TA TAKWAS
FITA TA TARA
FITA TA GOMA
Goma sha ɗaya
Fita Ta Goma sha Biyu
FITA 13
FITA 14
FITA 15
FITA 16
FITA TA 17
FITA TA 18
FITA TA 19
FITA TA 19
FITA TA 20

FITA TA ƊAYA

153 14 1
By Oum_Nass

ƘAWATA CE!

    ®NAGARTA WRI. ASSOCIATION

©OUM-NASS
  
     BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM.

GODIYA TA TABBATA GA ALLAH S W. A MAI KOWA MAI KOMAI, INA FATAN ALLAH YA SANYA ALKHAIRAI ACIKIN ABABAN DA SUKA HAƊA MU.
   Wannan karon ma gani na dawo muku da wani sabon labari wanda ya sha ban-ban da labaran da na saba kawo muku.
   Wata ƙila salon da ke cikinsa yayi dace da wani abu na sashen rayuwar ku, wata ƙila kuma ababen cikinsa ya baku takaici da kuma ban haushi.
  Lallai duk abin da kuka ga a cikin labarin Arashi ne da kuma kwaikwayo na rayuwar da ke faruwa.
 
    GIRMAMAWA

FITA TA ƊAYA

  ABUJA, NIGERIA.

  A hankali ta ke fito da wasu takaddu tana duba su, sannan ta mayar da kallonta ga mutane biyun da suke tsaye a kanta, mace da namiji.
  Murmushi ta yi tana lumshe idanuwanta da kuma ciza bakinta, hakan ke nuna tana cikin tsananin ciwo ne.
   "Ko zaka taimaka min da takardun can a loka Nu'aym?" Bai jira ta ƙarasa ba ya buɗe durowar ya futo da wasu takardu a cikin ambulan ɗinsu ya miƙa mota.
  Fuskarsa akwai damuwa sosai, kamar yanda itama ɗayar ta ta fuskar take cike da damuwa.
    Karɓa ta yi sannan ta ɗauki biro ta sa hannu a jikinsu.
   Da hannu ta yima ɗaya macen alama akan ta matso, matsowa ta tayi sannan ta miƙa mata da nuna mata jikin takardun "Kisa hannu anan."

Kallonta ta yi sai ta tsinci kanta da kasa sa hannun, idanuwanta sun cika da hawaye taf, kafin ta yi magana hawayen sun samu damar gangaro akan kyakkyawar fuskarta.
   "Me yasa zaki yi haka? Kin bani komi na rayuwarki Nabeeha! Ban taɓa kallon abu da sigar sha'awa ko birgewa ba ya kuskure min, muddum ya kasance naki ne! Sai dai wannan ban taɓa masa kallon sha'awar ba, ban taɓa jin cewar zan same shi! ba nawa ba ne Nabeeha! Baya cikin ababen da zaki iya sadaukar min da su. Wannan naki ne! Gwagwarmayar da kika sha, da faɗi-tashi dan ki same shi ne! Ya yi girma a tare da ni ace kin sadaukar min da shi.
  Ba zan iya amsar wannan ba Nabeeha! Bani da ƙwarewa da gogayya akan mallakarsa." Hawayen da ke kan fuskarta ya ci ƙarfinta, maganarta ta sarƙe sosai.
   Murmushi Nabeeha ta yi, tana lumshe idanuwanta da kuma ciza bakinta, wanda ke nuna tsananin ciwon da ta ke ji a jikinta.
    "Wannan ma naki ne Nabeela! Ban taɓa ganin abin da na mallaka a matsayin nawa ba face na mu, ni da ke. Ko wata rana ina yin aiki da tsammanin jira daga gare ki, ko zaki zo gare ni dan ki amshi wannan aikin!"
  Murmushi ta yi wanda da ganinsa na na ciwo ne da takaici, tana ƙara yamutsa fuskarta "Ko wata rana idan naga an kira wayana, ko nayi baƙuwa sai na tsammaci ke ce kika zo dan ki nuna ƙaunar nasarar da muka samu. Amma hakan ya gagara, ban ganki ba ban kuma ji daga gareki ba, duk inda ya kamata ace na samu labarinki sai ace bakya nan.
  Lallai rayuwar duniya 'yar ƙarama ce Nabeela, kamar yanda mutanen cikinta suke ƙananu da kuma manyan burika a cikinta. Burikan da ba su fiya  cika ba har sai lokaci ya ƙure musu, waɗan da suke samun cikar burin nasu kuma basu da yawa a duniya, kaɗan ne masu nasara da samun damar cika shi.
  Ni bana farin ciki akan ɗaukakar da na so ace ke ce a kanta!  Bana jin daɗin duniyar da na samu kaina a cikinta a yayin da ƘAWATA ta yi nesa da ni! Duk inda na juya ina ganin dubbanin mutanen da suke girmama ni da kuma nuna soyayyarsu a kaina, sai dai ni banji cewar su ɗin masoya na ba ne. Ina jin kawai suna bin ɗaukakar da take tare da ni ne! A yayin da ƙawar da muka taso ciki ɗaya ta guje ni saboda ɗaukakar."
  Hawaye ne ya gangaro akan fuskarta, hawayen da take jin raɗaɗi da zugin sa na taso mata tun daga ƙasan zuciyarta, zafinsa na kwanciya akan kyakkyawan kuncinta.
 
   Ita kanta Nabeela kuka ne ya ci ƙarfinta, kukan da ta manta yaushe rabonta da ta yi irinsa? Kukan da ta kasa bari ya sauƙar da hawayenta har sai da sautinsa ya futo ya ke amsa amo a jikin ɗakin.
   Shi kansa matashin Saurayin da yake tsaye kasa jurewa ya yi saida hawaye ya sauƙa akan fuskarsa, yana kuma rufe bakinsa da tafukan hannayensa.
   Ba zai iya tuna adadin lokacin da take ambatar sunan Nabeela ba a rayuwarta. Kamar yanda ba zai iya tuna lokutan da ya hanata magana akanta ba. Bai san cewa ƙaunar da take mata ta kai haka ba, kamar yanda bai taɓa tunanin tana gwagwarmaya a cikin dubbanin mutanen da suke da ikon faɗa a ji ba ne saboda ƘAWARTA kawai!
  Idonsa ya lumshe wasu hawayen suna sauƙa akan kyakkyawar fuskarsa. Yana jin inama zai iya dawo da jiya yau! Inama zai iya juya hannun agogo ya koma ba ya, da babu abin da zai hana shi cika ko wani buri na ta. Da bai dage akan ƙara nesanta su da junansu ba, da ya barta ta ci gaba da kula da Nabeela, da kuma bata duk abin da take da iko a kansa. Sai dai babu dama, wannan damar an barta, kamar yanda aka bar kari tun ran tubani.

   "Har yanzu banga ta inda na can-canci wannan sadaukarwar ba? Har yanzu faɗuwata na ke gani da kuma raunina a duk lokacin da na ke tsaye a gabanki! Mutane da yawa suna cewa na samu Lu'u-Lu'u mafi daraja a rayuwata, a yayin da suke hasko min fuskarki a tafukan hannayensu.
   Na ɗauka Nasarata zata zo ne bisa dagewata da aikina tuƙuru, ashe ɗaukakata na gare ki.
Bana so na ci gaba da yin rayuwa sadaka da kuma ɗaga matsayin da ba gumina ba ne Nabeeha, wannan matsayin ba zan taɓa samunsa ba, domin zuciyata bata da kyan da zata kula da shi! Ba zan iya ci gaba da gani na akan matsayin da kika sadaukar min ba!" Ta ƙarasa maganar hawaye na sauƙa akan fuskarta, hawayen da take ganin kamar sun gaza wajen nuna damuwarta da kuma tsananin nadamarta.

     "Wa ya faɗa miki gwagwarmayar ba taki ba ce? Wa ya faɗa miki a matsayin sadaka na baki?" Ta yi saurin katseta, tana murmushi akan fuskarta, a yayin da take ƙoƙarin tsayar da hawayen fuskarta.
    Ɗagowa suka yi duka suna kallonta dan jin amsar maganar da ita kaɗai ce zata ba su.
     Ruƙo hannunta ta yi ta ɗora akan nata, sannan ta ɗan matsa shi da ƙarfin da ya rage mata. Zafin hannun nata na ratsa ko wata ɓula ta jikin Nabeela tana jin yana tatsa ko ina na jikinta.
   "Daga lokacin da na fara aiki sai nake ji a raina burinki nan wannan matsayin, ni bani da sha'awar samun damar da sunan da na samu. Hakan yasa na ci gaba da yin aiki kamar yanda nasan da ke ce a wannan matsayin za ki yi shi, zaki kuma so sunanki ya dinga yawo a duniya.
   Sunan ne yake futowa kawai a jikin aiyukan da nayi, amma zuciyata na cike ne da hasashen yinsa kamar yanda zaki yi. Yana kuma tuno min da abubuwan da kike yawan faɗa inda kin samu damar yinsa. Sai dai ban same ki ba, ban ji daga gareki ba har sai a ƙarshen watan da ya rage min."
  Murmushi ta sake yi tana lumshe idanuwanta "Ƙaddara ta daɗe tana bibiyar mutane da sauya musu arashin su. Lokacin da na yanke duk wani buri da kuma sa rai akan ganinki, a lokacin kuma ƙaddara ta bayyanar da sunanki a gabana."
  Idanuwanta ta sake lumshe tana jan numfashi, ba zata iya tuna yaushe ne ta yi doguwar magana haka ba. Kamar yanda ba zata iya tuna adadin lokutan da ta samu kanta fayau babu nauyi ba. Wata ƙila dama ce Allah ya bata, damar da take ji itace ta ƙarshe a gare ta. Sai dai ko ba komi burikanta ya cika, ta cika mafarkin da ta daɗe tana son tabbatarsa.

    Ƙara matsa hannun Nabeela ta yi, tana jin kamar za'a iya ƙwace mata "Ki sa hannu dan Allah!!" Ta faɗa cikin raunin muryarta da ta fara ja baya.
   A yanzu bata da zaɓi, duk yanda ta ke son ta guji faruwar hannunta akan takardun ba zata iya ba, karon na farko da Nabeeha ta roƙeta akan abin da ta saba bata ba tare da ta roƙa ba.
   Hannunta har rawa yake ta sa hannun, tana jin hawayenta na tsananta zuba a kan takardun.
  Har zuwa lokacin da ta gama sannan ta miƙa mata takardun. Da kai ta yima Na tsayen alama ya ƙaraso wajenta.
  "Ka kira Lutfi ka ba su suna jira dan Allah." Bai bari ta ƙarasa ba ya kara waya a kunnensa ya yi magana, ba daɗewa ya amshi takardun ya futa da su.
Mintuna uku ya sake dawowa ya matso kusa da ita yana shafa kanta da murmushi akan fuskarsa.
   "Na basu, sun tafi, duk da sun so ganinki  kafin tafiyar su."
  Ido ta lumshe tana murmushi, sannan ta kama hannunsa ta ɗora akan na Nabeela sannan ta ɗora ɗaya hannun nata akan nasa, hakan ya sa suka kalleta a tare, suna buɗa idanuwansu duka a kanta.
    "Ina da sauran burin da bai cika ba. Burin da yasa na yi nesa da ƙasata ya ƙara matsar da ni daga inda na ke." Ta yi maganar tana shigar da idanuwanta kan nasa, da ya ke jin kaifinsu da tasirinsu na huda zuciyarsa, wani shauƙin da ya daɗe yana ji akan su yana ƙara tasirantuwa a zuciyarsa.
    Nabeeha da ban take, ita kaɗai ce mace guda da yake jin soyayyarta a duk tsawon rayuwarsa.

      "A lokacin da idanuwana suka rufe nasan idanuwan duniya za su dawo gare ku, bani da tabbaci akan sanu kwanciya mai kyau da amsa tarin tambayoyin da za su zo gare ni a bayan babu ni. Amma idan kuka zama a ƙarƙashin inuwa ɗaya kalmar son kai da son zuciyar da nake tunanin ina da su za su ɓacewa idanuwana na.
  Ba iya yau kaɗai ba, nasan lokuta masu yawa na sha yin addu'a akan cikan wannan burin. Dan Allah Nu'aym ka maye gurbina da Nabeela a bayan idanuwana! Ka bata matsayin da ka bani a zuciyarka! Ka mata kallon da kake min! Wannan kaɗai nake buƙata a wajenka, wannan kaɗai nake so daga gareka! Na tabbata itace mace ɗaya da zata kula min da yara na. Itace mace ɗaya da zata zauna da kai ta so ka kamar yanda nake sonka.
   Ina so na ji a raina ban bar ɗayanku cikin neman madogara da samun mutumin da zai jingina da shi ba. Ina so na samu aminci a lokacin da mutuwa zata ɗauke ni a yayin da mutane biyun da nake so a duniya sun zauna ƙarƙashin inuwa ɗaya! Ku min alƙawarin zaku zauna a tare da juna? Ka mun alƙawarin maye gurbina da Nabeela. Dan... Allah .. Nu.. Nu'aym!" Ta yi maganar tana jan numfashi, muryarta ta fara sarƙewa daga saurin da take, kafin wani lokaci numfashinta ya fara marazanar barinta.

   "Dan Allah!" Ta yi maganar tana ƙoƙarin sakin hannunsu.
   Ruƙe hanunta ya yi gam akan nasu yana  jin sauƙar hawaye na ƙaruwa akan fuskarsa, ji yake kamar zuciyarsa zata iya tsalle ta faso ƙirjinsa.
   "Ba abin da zai same ki Nabeeha! Ba zaki mutu ki barni ba! Zan auri Nabeela kamar yanda kike so na miki alƙawari, amma kada ki mutu ki bar ni dan Allah!" Ya yi maganar a ruɗe yana jin kalmomin suna tafiya suna gujewa daga gare shi.

     Sai dai kamar ya makaro, dan baya jin akwai kalmar da zata iya sake futowa daga bakin Nabeeha bayan murmushin da ta masa tana lumshe idanuwanta da ƙoƙarin sakin hannunsa.
    Da sauri ya danna ƙararrawar da ke kusa da gadonta, yana dannawa kamar zai iya fasata saboda gani yake kamar bata isa inda ya kamata ace ta je.

    Nabeela da jinta ya yi ɗaukewar wucin gadi ya samu dawowa a lokacin da ƙaran ƙararrawar ya cika kunnenta.
  Gani take kamar mafarki ta ke ba wai gaske ba ne, duk abin da Nabeeha ta ke faɗa mata kamar kunnuwanta ne suka yi kuskuren ji kamar yanda suka saba. Ko kuma ruɗewar mafarkin da ta saba yi ne a cikin mafarkanta.
  Nabeeha ta bar mata komi, komi da ta mallaka harda mijinta tana kuma kiran zata mutu ta barta.
  Bata san ya akayi ba sai da ta tsinci wasu mutane masu fararen kaya na jan gadon Nabeeha suna futa da ita, tana kallon Nu'aym na binsu kamar zai tashi sama, gani take kamar shima yayi zaucewar da ta ninka ta ta.
  Da ƙyar ta cira ƙafafuwanta tana bin bayansu tana son ace ta kai inda suke, sai dai takunta baya gamsar da gangar jikinta, asalima kamar yana ƙara matsar da ita ne zuwa baya.
  Har zuwa lokacin da ta ga sun shige da ita wani ɗaki sun rufe musu ƙofar.
     Tana jin sautin kukan 'Yan uwan Nabeeha da kuma 'yan gidansu, tana jin kaiwa da kawowar da Nu'aym yake wanda ita ta kasa.
   Idanuwanta na tsaye a kan ƙofar ɗakin da aka shigar da ita ɗakin tana ga kamar idan ta lumshe idanuwata ƙofar ba zata buɗe ba.
  Bata san adadin lokutan da ta ɗauka a tsaye a wajen ba, sai dai taga ƙofar ta buɗe a karo na biyu. Likitocin sun fara futowa, ya yin da 'Yan uwa suka yi caa a kansu suna tambayar ya take.
  Daga inda take tsaye bugun zuciyarta na ƙaruwa, kamar zata faɗo daga maɗaukarta, tana jin lokacin da kunnunwata suka yi mugun ji daga bakin gajeran Likitan mai kakkausar muryar da bata taɓa jin irinta ba.
   "Ku yi haƙuri Allah ya amshi rayuwa Nabeeha Nameer! Ina miƙa ta'aziyyata gare ku!"

  Bata tsaya jin ƙarshen kalmar ba, bata kuma buƙatar jin ta'aziyyar da yake mata ba, sai dai tasan jinta da ganinta ya ɗauke ɗif, tana fatan wannan ne gani da kallo na ƙarshe da zata yi a rayuwarta.....

    🌹🌹🌹🌹🌹

    Alhamdulillah! Wannan ina fatan kun gyara zama! Ina fatan kun shirya amsar saƙon farko a cikin labarin ƘAWATA CE! Zan Girmama ku a cikin ko wani shafi na labarina, domin nasan akwai ƙauna da mutuntaka a cikin wannan tafiyar.

#ƘWTC
#DABANNE

   PLEASE SHARE

Oum-Nass

Continue Reading

You'll Also Like

7.1K 493 9
"Alright you dumb door!" Backing away you took a big breath "You better take me to the surface-" You declared, pushing it open with both hands "Or im...
105K 5.5K 40
مرحبًا بكم في المملكة لا لا، يجب أن أحذرك أولًا من يدخل المملكة لا يخرج حيًا. يمكنك المغادرة الآن.. سأترك لك بعض الوقت للتفكير. حسنًا .. قررت؟ هل ه...
31.7K 1.2K 30
"Come on, come on, don't leave me like this I thought I had you figured out Something's gone terribly wrong You're all I wanted Come on, come on, don...