A SIMPLE DARE (WASA DA SO)

By marteybee

434 7 16

More

new book
Page 2
Page 3
Page 4
Page 5
Page 6
Page 7
Page 8
Page 9
Page ten
Page 11
Page 12
Page 13
Page 14
Page 15
Page 16
Page 17
Page 19
Page 20/21
Page22/23
Page 24/25

Page 18

24 0 0
By marteybee

✨✨

SIMPLE

DARE

                              ✨✨

(WASA DA SO)

WRITTEN AND STORY
  BY
NERNAH MARYAM
(MEEMARH)

 
             Kofa a bude take ga duk me son yin joining group dina😌,Amman Hajiya don Allah in kin san ba yin comment ko karanta littafi na zai kawo ki ba I beg you in the name of Allah kiyi zaman ki ba sai kin shigo ba!!haka zalika wanann group din na mata ne zalla don Allah Maza should stay away from my group👏

       My What's app group link👇🏻

           https://chat.whatsapp.com/EUrVVaKJnIBDTlQsxurZv0

Bismillahi Rahmanin Raheem............

(    In the name of Allah the most beneficient,the most merciful)

 
  Kofa a bude ta ke ga duk wani me good quality product da ya ke son Advertising ɗin shi,as Kaya masu kyau,da inganci (TALLAH) should contact me via :
                              08100046388

Page 1️⃣8️⃣

TALLA!!TALLA!!TALLA!!!

       https://chat.whatsapp.com/ImtxMSS1tuSKqvBpPqc03P

Assalamu'alaikum sisters🤗
KAMSHI* mace Mai kima, mace Mai daraja, mace Mai izza, mace Mai aji itace tasan darajan kamshi, if your perfume is not unique hajiyata you're just using ordinary air freshener🤣, hajiyata ko nawa Zaki kashe indai a turare ne baki Fadi ba😘 matan da suka gane suka San yanda zasu kankaro da martabar su, suke amfani da turare, a *BAKHOOR BY FAIXY* Zaki Sami Main chic, Bachelor, Husband snatcher, Her royal sexiness, Mysterious girl, Pleasure, Boovilous, White khumra, Maroon khumra, Black khumra, Hair perfume, Turaren wanka, Turaren  wuta, Turaren tsuguno, Turaren mopping,Turaren carpet Shu'umat khumra,and more, yar uwa kar kibari abaki lbr, (wholesale and retail) WhatsApp 09067621681, siyan na gari Maida kudi gida🥳

Instagram @Bakhoor_by_faixy

******************************

Dakin Mama Zuhra ta shige tare da fadawa jikin ta inda ta sake kukan bakin ciki,dago ta Mama tayi saurin yi don ya jima da ta ga kukan Zuhran haka,domin kuka ne taki yin shi daga cikin zuciyar ta na bakin ciki,duk da ba sosai take jiyo su ba amman shakka babu ta san sa'bani suka samu da Sabeehar wace tun shigowar ta daman ta fahimci akwai matsala,ta so shiga ta ji ba'asin zancen amman sai tayi tunanin ta bar su kawai suyi tsakanin su tunda duk babu wace bata mallaki hanklain kan ta ba a cikin su.


"Ya isa haka kukan nan Zuhra yi shiru in banda abun ki ma miye na kukan to?Wani zama ne aka ce miki ba a samun Sa'bani don kuma shedan ya ingiza ku duk biyun kun yi fadi in fada,ita ta fice rai bace tana fadin ba ta kara zuwa gidan nan ke kuma kin zo nan kina kuka,ina amfanin irin haka?"

Cikin kuka Zuhran tace "Haba Mama!!haba Mama don Allah ni miye laifi na da Sabeeha ta kasa gane wa,wai har ni Sabeeha za ta ce wai ashe za a iya hada baki da ni a cutar da ita?Wlhy ba karamin zafi da ciwon kalman nan na ji ba,Mama duk fa kan Faizan take maganganu da fushin nan fa,yau ya je gidan su ta gan shi shike nan ta yi masa cin mutuncin karshe,ya zo gidan nan ya gama fada mun kamar zai yi kuka,tare da roko na in taimake shi na mata bayani tare da shawo kan ta Wlhy Auran ta yake son yi,amman ki ga abunda ta zo tayi mun,yau na dauka Goofy angel ko wani can na bashi number din ta za ta mishi kara sanann zai ci albarakaci na na dau ina da wannan right din a kan ta tunda Aminiya ta ce na tun yarinta,amman baki ji mugayen maganganun da ta fada mun ba,wallahi tallahi Mama Allah ne sheda na ba don komai nayi haka ba sai don ina son ta da Alkhairi da arziki,Mama duk duniya babu kawa irin Sabeeha ya sanya duk wani abun arziki nake fatan ta Riga ni samu,Wlhy yau da ace yaron nan don wasa da hanklain ta ko kuma yaudara ko bata lokaci ya zo yana son na hada su,ko zai mutu ba zan hada ba,amman Auran ta yace mun yana son yi Mama laifi ne yau don na so Sabeeha tayi aure?Auaran ma Auaran gata Auran nuna wa sa'a"ta kare tana share hawayen ta.

"Ya isa haka kukan bashi fa da amfani Zuhra tunda aikin gama ai ya Riga da ya gama,duk na san komai tunda Ai tare da ke muke cikin gidan nan,kin san kowa da irin fahimtar shi,so kar ki dauki maganganun da ta fada miki ki kai su zuciya har ya dame ki,Sabeeha Aminyar ki ce ko na ce yar uwar ki,yanda kike fadin kina kaunar ta na tabbatar ke ma tana kaunar ki fiye ma da hakan,ke dai shedan ne da bayi son zaman lafiya,abu ne karami amman ya ya hura ya zamo babba don a samu tashin hankali,yanzu dai kiyi hakuri ya sanya tun farko na so da kin sanar mata tunda kin ce mun tun farko bata kaunar yaron,kila da duk hakan be faru ba"

"Mama sabida Allah Sabeeha haka za tayi ta zama ke nan har karshen rayuwar ta ba aure saboda kawai tana tsoron kar abunda ya faru da Adda Nawwara kar ya maimaitu a kan ta?Ashe da ko haka ne nima ko inda maza suke ba zan kalla ba saboda halin Mahaifi na,Mama Wlhy babu abinda nake so a duniyar nan irin in ga Sabeeha tayi Settling down nima zan fi samun kwanciyar hankali,ina tausayin kan mu ina tausaya mata,domin marainiya ce daga ita sai Umman ta,da rayuwar kuncin da take kullum gidan su ba gwamma tayi Auran ta samu yancin kan ta ba,Wlhh Mama FIK ya canza daman abunda ya sanya ta tsane shin matsala suka samu har ta mare shi,Wlhy in kin ga yanda yake rawar kafafuwa akan ta sai kin yi mamaki,sai yanzu na gane harda karyan mutane in suna fadan halaiyan sa,amman rashin kirkin nashi be kai haka ba,ke dai sheda ne zuwan shi gidan nan a sau nawa don kawai na shawo masa kan Sabeeha,Umma ga kyauta ga hakuri Wlhy da wani ne ta mare shi sai yanda karfin shi ya kare,kila sai ya sanya an daure ta tunda dan gidan masu kudi ne na ban mamaki,amman sam be yi hakan ba,wallahi Mama Faizan irin shine ko wace mace ke son samu,daga shigan shi rayuwar Sabeeha farin ciki da walwalan da ya sanya ta har ban san adadi ba,tsakani da Allah Allah da kanshi ya hallici soyayya sanann Aure sunnah din Annabin mu ne amman ke Sabeeha kiyi depriving kan ki wa wanann right din akan me?Ko kundin dokar kasa ma ta bada daman ka so kuma a so ka,amman na rasa gane wanann mentality na Sabeeha"Zuhra ta kare tana Jan hanci.

Dan shiru Mama tayi sanann tace "duk na ji na kuma fahimta kamar dai yanda na fada miki ne shedan ne a tsakanin ku shi daman yana bakin ciki da duk wani aikin Alkhairi,Allah ya ga niyar ki don haka ki yi hakuri ki bar kukan nan haka,ki nutsu hankalin ki ya kwanta itama nata ya kwanta sai kuyi magana na fahimtar juna,na tabbatar itama Sabeehar bacin rai ne amman sarai ta san ba za ki taba iya cutar da ita ba,tashi ki wanko idanun ki kar ki sanya damuwa a ran ki babu kawancen da ba a samun matsala ba ma kawance ba duk zama aka ce ai daman zo mu zauna watarana kuma mu sa'ba do kar ma ki sanya abun a ran ki kin ji ko"kai Zuhra ta gyada tare da mikewa don wanko idanun nata wanda har yanzu ran ta bace yake da maganganun da Sabeeha ta mata,yau ta dauka tana da wanann alfarman a gurin Sabeeha amman wai har ita take kira da Shashasha kawai don ta baiwa FIK number din ta,kai ta girgiza tare da iban ruwa a mo'da ta wanke fuskan nata sanann ta shige dakin ta don har ta ji kan ta ya fara Sara mata,jakar tsarabar da FIK ya kawo a baiwa Sabeehar ta gani aje alamun Sabeehar bata dauka ba ke nan,hakan ne ya sanya ta mike wa tare da sanya hijab ta dau jaka sanann ta fito,dakin Mama ta shiga

"Daga wanko idanu sai kuma na gan ki da Hijabi ina zuwa kuma?"Mama ta tambaya tana yar dariya, "Mama gidan su Sabeeha zan je yanzu in dawo tsarabar da ya kawo zan kai mata,kin ga ba nawa bane tsautsayi kar ya sa Abba ya shigo ya gani"

"Munafuka da Uwar ta uban me ake boye mun ni da gida na don iskanci wai kar a bari na gani"caraf suka jiyo maganar Abba a bayan su,daman Zuhra a sama take hakan ya sanya ta saurin bashi amsa don ta san in tayi shiru Mama ba iya tanka shi za ta yi ba.

"Abba lah ashe ka shigo to sannu da zuwa,kai Abba ba fa komai bane daman sako ne aka bani na baiwa Sabeeha to ta zo ta tafi ta manta da shi shine nace bari na kai mata kar ka gani kayi wa Anty Amarya sha'awar sa ka ga kuma abunda ba na wa ba balle marainiyar wayon nata Mama na balle ace za a kai mata"ta kare tana bude mishi kyakyawar paper bag din.

Idanu yayi saurin zaro wa sakamakon kayan dukiya da ya ci karo da su,wanda be taba ganin irin su ba,bakin shi har na rawa gurin fadin "Zuhra wanann din wai duk na wace ma kika ce?Ko naki ne kin fara yin abun arziki"ya kare yana washe baki tare da kokarin saka hannu don ciro wata kwali da ya gani wanda be san ta mecece ba amman ta tsole idanun shi.

Da sauri Zuhra ta rufe jakar tare da cewa "Ina Abba ina ni ina wanga kayan duniya ai Habeebeey bayi da kudin siya mun rabin wanann ma,ka tuna wanann mutanen da suka zo a mota suka yo kira na wancan ranar?"

Da sauri Abba ya ce "ni ko Uwa ta ina zan manta wanga rana ba shine har ya bani 50k ba yaron da na miki sha'awar Auran ki ko kya maida wanann uwar kashin wuyan irin ta Uwar ki"ya kare yana me daure fuska don har yau in ya tuna inda ya ga samu ya ga rashi sai ya ji kamar ya daura hannu a kai ya kwala ihu.

Dan dariya Zuhra ta sanya tare da jin dadin Mama bata sako baki a zancen na su ba hakan ne ya sanya ta cewa "Ai Abba na fada maka to shine yayi wanga duk siyayya wai duk ka nan din ga da ka gani kayan Sabeeha ne,gaba daya yace tsaraba ya kawo mata,kasan son ta yake kuma Auran ta ya ke son yayi"ta kare tana washe baki.

"Mtswwwwwwwweeeee amman kin yi asara Wlhy Zuhra Turrr!!!Albasa bata yo halin ruwa ba kin kuma bani kunya billahil azeem,ban taba sanin ke wawiya bace sai yau dan Bura uban ki Sabeehar da uwa ta fiki ko da uba da za ta na samun wanann tulin kayan duniyan?Shegiya ko goro babu uban da ya taba kawo miki balle ni na lashi arziki,shegiya saboda mutuwar zuciya zuciyar ki ta mutu irin ta uwar ki saboda hauka wai ke ce kike hada ta da me arziki har kike bin ta gida da kayan duniya sabida ke kin samu ya ishe ki ko?Wlhy Allah ya sauwaka da halin ki Zuhra da uwar me za ta nuna miki saidai hasken fata amman saboda mutuwar zuciya ita tana cikin daula ke kina nan kina fama da Malamin makaranta,na rantse in baki bace mun a gani ba sai na miki karaya takwas a hannu da kafa kuma Wlhy na ci kayan da ya kawo din ayi uban da za ayi"

Har ga Allah maganganun shi ba karamin dariya suka bai wa Zuhra ba inda ya rufe ido shi ala dole yana expressing din bakin cikin shi,sanin halin shi sarai zai iya kwace jakar ayi abun kunya ya sanya ta cewa

"Allah ya huci zuciyar ka,ni kam Mama sai na dawo"daga haka tayi saurin nufan zauran gidan, "Allah ya tsare Zuhra ki gaida Umman nata,in kin ga Faisal kofar gida ki ce ya zo ya je mun aika,ki kuma yi saurin dawowa kar ki zauna tunda Abban ku na gida tayu ya bukaci wani abun"

"Za ki mun shiru ko sai na taka wuyan ki,Wlhy ba laifin ko wace shegiya bace sai na ki,na tsani yarinyar nan Wlhy ita ke kara kashe wa Zuhra kasuwa amman saboda iyayi da munafurci irin na ku na mata kun gaza fahimtar hakan,Wlhy in baku sa wasa ba sai na yanke duk wani halaka da ke tsakani ta da Zuhra,saboda banda mutunci ina magana ita tayi ficewar ta ke kuma kin yi shigewar ki daki kin sauke labule,wato dan iskan nan ya ishe mu yayi ya gama sumbatun shi ya bamu guri ko?To Wlhy ku fita ido na zan ci muku mutunci in ba kuyi wasa ba"haka dai yayi ta sababi shi kadai ya kai ya kawo yayi tsaki yayi kwafa bakin ciki goma da ashirin sun hade masa ya rasa me daya ke masa dadi,ji yake da yana da dama ba abunda zai hana ya aurar da Zuhra wa FIK don gani yake ita ce ta dace da wanann daulan ba wata Sabeeha ba,sanann yana matukar jin haushin yanda Zuhra ke wani rawar kafa akan Sabeehar da wanann sabon yaron dan gidan masu kudi da haushi shima yake bashi,na akan me be so Zuhra ba sai Sabeeha?Haka dai yayi ta yi har ya gaji ya fita,Mama na daki tana jin shi kala bata ce da shi ba,don wani zubin daukan abubuwan na shi yake kamar mara lafiyar brain.

Ko da ta shigo gida har yanzu Umma na parlor tana kallo,sanar da ita ta dawo tayi sanann ta wuce dakin ta,inda ta tarar da missed calls din Faizan ya fi a irga,muguwar tsaki ta ja a bayyane ta furta "aikin banza aikin wofi,ko nayi maka kama da shashasha ne sai Allah da za ka yi tunanin zaka iya fooling dina da sauri haka"zama tayi a kan katifar ta tare da bude wayar inda ta bi shawarar zuciyar ta kan ta watsa number din shi a blacklist sai kuma ta tsaya don tunanin da tayi kila yana kira ne ya ce da ita ya aiko a kwashe masa kayan kallon shi,saida zuciyar ta ya dan buga domin bata san me za ta ce wa Umma ba in ta ga an zo kwashe kayan abinci da kayan kallo,ba Umma ka dai ba,su Hajiya Ladi an samu abun nema an kuma samu chapter din gulma ita da sauran matan gidan,saidai ta gwammaci suyi mata wanann dariyar da yaba maganar da ta bar ko da chokali ne na FIK.

Tana cikin wanann tunanin ne wani kiran na shi ya kuma shigowa,inda a zafafe ta dauka tare da sanya wayar a speaker,cikin rudu da muryan alamun mutum ya sha kuka ya gaji yace

"Hello Beeha,can you hear me?Pls hear me out don Allah I can explain Wlhy"saida ta sauke dan ajiyar zuciya jin ba aikowa yayi a karba masa kayan sa ba,har ga Allah bata son barin komai na shi amman tana tsoron tabuwar mutuncin su.

"Look na fada maka kuma zan kuma fada maka,babu abunda yayi saura da ya rage ni da kai ba mu tattauna ba,FIK leave me alone I don't want to
talk to you,ko ana dole ne?Daga kai har ita shugaba Master planner din bani son kuma magana da ku,tun dazu na ce da kai ka goge number na amman ka kiyi ko?To shike nan ni bari na taya ka goge wa"ta kare a zafafe kamar za ta buge shi

"Bebe pls I'm sorry have been crying tun dazu don Allah ki saurare ni 2 mints ma ya isa"kitt ta kashe wayar ta,inda aka bar shi da "Hello!!Hello can you hear me?"jin shiru ne ya sanya shi zare wayar tare da maka ta a kan gado

"Fuck!!!!yarinyar nan bata san da wa take yi ba,Wlhy tallahi duk wani abunda za ta mun tana kara wa kan ta punishment ne akan wanda na tanadar domin ta"ya kare yana Jan tsaki me kara sanann ya dauki wayar ya kuma danna number din ta,saida aka ce da shi user busy wanda hakan ya tabbatar da shi kan cewa tayi blocking din shi ne.

Dan dariyar takaici ya sake sanann ya mike akan doguwar kujerar da ke dakin sa,ya sanya hannun shi cikin gashin kan shi a hankali yana shafawa,shiru yayi tare da lumshe idanu be ma san me daya zai yi ba,can kamar wanda aka tsikara yayi saurin mikewa zaune

"Hell nooo ba zai yu ba saida na zo this far haba Bebe Ai Wlhy baki isa ba dole mu karasa abunda muka fara,ba zan taba barin ki ba sai na samu cikar buri na"ya kare yana dauko wayar shi tare da shiga WhatsApp din shi,chat din su ya shiga inda ya zauna ya shiga tura mata message na ban hakuri tare da rokon ta don Allah ta daure ta saurare shi suyi magana,shi ba da niyar cutar da ita yayi mata haka ba,ya rubuta mata messages sun fi 20 tare da crying emojis kafin ya kunna data ya tura ganin bata online ne ya sanya shi aje wayar tare da fadawa toilet don yin wanka ko zai ji dadi da sanyi a ran shi,dan tsaki ya kuma ja a hankali sanann furta "damn what a day,dole na bukaci shower Gaskiya.

Sallamar Zuhra ne ya fito da Umma daga parlor,tana mamakin Waye haka da gabanin Magrib din nan,ganin Zuhra tsaye ya sanya ta sakin fuska, "Ahh yau ni nake ga ikon Allah yaran zamani Zuhra lafiya kika biyo kawar taki,ince dududu ko 30 mints kun yi da rabuwa ne?"Umma ta kare tana yar dariya.

Dariyar dole Zuhran tayi sanann tace "Ina wuni Umma ya zafi zafi ya aiki?Mama tace na gaida ki", "kai Masha Allah lafiya kalau Zuhra Alhamdulilah ina amsa wa,to ki shiga tana daki tun rana na ga yanayin ta wani iri na tambaya tace da ni ba komai kila ki san me ke damun ta kila ta fada miki,don Sabeeha akwai ta da tsinannan zurfin cikin tsiya"Umma ta kare tana saka takalmin ta don dauko abu a daki.

Zuhra bata ce komai ba banda ja da tayi ta tsaya tunanin abun yi,inda Umma ta zo ta wuce ta ta shige daki har ta gama ta fito Zuhra na nan tsaye hakan ne ya sanya Umma ce wa "Zuhra ya baki shiga ba?Ko tana bandaki ne?"

Kai Zuhra ta girgiza a hankali sanann tace "Umma uhmmm daman gurin ki na zo don Allah"dan murmushin manya Umma tayi don tun dawowan Sabeeha ta fahimci akwai abinda ke faruwa zuwan Zuhra ya kuma tabbatar mata da zargin ta.

"Mu shiga parlor to Zuhra ba damuwa mu je can sai muyi maganar"ta kare tare da bude kofar parlor din,inda suka shiga Umma na gaba Zuhra na a bayan ta,saida Umma ta zauna kan kujera inda Zuhra ta nemi guri kusa da kafafuwan ta a kasa ta zauna tare da sauke kai kasa sai tayi shiru kuma.

"Ina jin ki Zuhra me ke faruwa?"dan numfashi Zuhra ta sauke sanann tace "actually Umma ba zan miki karya ba ko na boye miki,don Mahaifiyar mu ce ke,ni da Sabeeha ce daman muka samu matsala"dan kallon ta Umma tayi tana mamaki don tun tashin su babu wani matsalan da suka taba samu har ta kai ga sai an musu sulhu don ita a kan idon ta ba su taba fada ta gani ba,coz ba karamin hakuri da kawaici Zuhra ke wa Sabeeha ba,don har ita kan ta Umman kan fada,tunda yau Zuhra ta zo har gida to abun ya kai ta bango ba karya.

Ajiyar zuciya ta sauke sanann ta dan yi dariyar karfin hali kafin tace "to yau kuma ke da Saheebar taki za mu ji kan ku,me ya hadu ku?"shiru Zuhra ta dan yi kafin can kuma ta budi baki tace "Umma daman sai kuma tayi shiru sakamakon hawayen da ke zubo mata sai yanzu abinda Sabeeha tayi mata ya kara ci mata rai,kun san kuma akwai mutanan da in sun zo maida magana ya kan sanya su kuka to Zuhra ma na daya daga cikin su.

Umma bata ce da ita komai ba banda kallon ta da take yi,har ta gama kukan sanann tace "Za ki sha ruwa?"kai ta girgiza alamun aa, sanann Umma tace "ah yau kam ni da kaina zan zane Sabeeha a gidan nan tunda ta sanya Zuhra kuka,goge hawayen ki in ta fito ta ga kina kuka Ai sai ta raina ki"

Baki Zuhra ta turo sanann tace "Umma Allah abun yayi mun ciwo sosai ne wai har ni Goofy angel za ta ce za a hada baki da ni a cutar da ita?"zama Umma ta gyara sanann tace "fada mun abunda ya faru Zuhra"

Nan ko Zuhra bata boye wa Umma komai ba ta bata labarin tun daga farkon haduwar su da FIK zuwan da yayi gurin ta sanann nufin Alkhairin da yake da shi akan Sabeeha,nannauyan ajiyar zuciya Umma ta sauke sanann tace

"Ita Sabeehar ce ta miki haka?"kai Zuhra ta daga sanann tace "Umma Wlhy babu nufin cutar wa da nake nufan Sabeeha da shi,duk duniya bayan iyaye na babu wace nake so irin ta,Umma tun yarinta muke tare laifi ne don na so mata arziki?Wlhy Umma ba karamin so da kauna FAIZAAN yake wa Sabeeha ba,Umma in kin ga yanda ya ke roko na Wlhy sai ya baki tausayi,kuma Wlhy ni da zuciya daya na yi wanann abun don na ga yanda yake kauanar ta na tabbatar ba za ta sha wahala ko ta wulakan ta ba,amman maybe in ta nutsu tayi tunani za ta fahimci hakan,wanann jakar tsaraba ce a ciki da ya kawo domin ta amman bata tsaya ta karba ba shine ta biyo gida ya kawo mun kan na bata tare da yi mun makiyar don Allah na shawo masa kan ta,shine nace bari na kawo mata"ta kare tare da mike wa.

"Koma ki zauna Zuhra ina zuwa"Umma ta fada tare da mikewa tsaye fita tayi tare da shiga dakin Sabeeha ba dade wa suka dawo tare inda da ganin Zuhra Sabeeha ta sha jin jikin ta tare da tsuke fuska,da hannu Umma ta nuna mata kusa da Sabeeha sanann tace da ita ta zauna.

Nan ko ba musu ta zauna inda Umma ta rufe ta da fada kuwa,tas tayi mata domin har ga Allah bata ga a ina ne laifin Zuhra ya fito ba,ita da kyakyawar niyar tayi abun nan sannan miye na ci mata mutunci har haka,tayi mata fada sosai sanann ta shiga yi musu nasiha duk su biyun,kafin suka gode mata inda Zuhra tace za ta koma,kar dare yayi.

Murmushi Umma tayi tace "ba za ki tsaya kiyi Magrib ba tunda an fara kira?In ya so sai ki ci abinci?"kai ta girgiza sanann tace "aa Umma na gode zan tafi Mama kar tayi fada"nan ko tayi wa Umma sallama ko kallon inda Sabeeha take bata yi ba ta sa kai ta fice bayan ta aje jakar,Umma na ta sanya mata albarka.

Kallon Sabeeha Umma tayi sanann ta ce "ba za ki tashi ki raka ta ba?Wlhy Sabeeha ki fita ido na wanann dacin rai da zafin halin naki ya soma isa ta fa,saboda Allah miye laifin yarinyar nan a cikin maganar nan?Amman saboda kin ga kin fita baki shine za ki bita har gida ki fada mata maganar da kika so ko?Ki tashi ki bi bayan ta ki bata hakuri tun raina be gama baci da ke ba"

Jiki ba kwari Sabeeha ta mike tare da fitowa tana jin duk zuciyar ta a lalace wato Zuhra ita tayi mata laifin sanann ta kawo karar ta gida,Wlhy babu hakurin da za bata ta ma raina wa kan ta hankali,gunagunin da take tayi ke nan har ta iso kofar gidan amman ko kyallin Zuhra bata gani ba hakan ya tabbatar mata da cewa ta tafi ke nan,kafudu ta dake in I don't care din nan sanann a bayyane tace "kan ki ake ji"ta kare tare da jan tsaki sanann ta dawo gida.

"Kin bata hakurin?"shine abun da tayi Umma ta fada bayan shigowar ta gidan,dan Jim ta dan yi kafin a hankali tace "Umma na tarar ta tafi amman zan kira a waya sai na bata,ko kuma ai za mu hadu gobe a makaranta"

"Ni dai Sabeeha ina me kara Jan kunnen ki Wlhy ki rage wanann zafin ran naki,in za ki yi wa kowa wa ma Zuhra ta cancanci dagun kafa daga gurin ki,tare kuka taso na kuma san halin ku daga ke har ita,wlhh hakurin yarinyar nan da take yi da ke har ya baci duk yanda kike so ko bata so haka za ta bi wai duk don ku zauna lafiya,amman wai ita kike yi wa wanann irin rashin mutuncin Gaskiya ban ji dadi ba Wlhy,duk hakurin Zuhra ace saida kika kure ta,yaron da ake abun don shi ba fa ita ta bishi ta ce ya so ki ba fa,shi yake ta biyayyan ta akan ki,to in ma za ki ga laifin shi ita Zuhra nata a wanne?Gaskiya ban ji dadi ba sam Wlhy"ta kare tana mikewa

"Kiyi hakuri Umma cikin bacin rai ne amman hakan ba zai kuma faruwa ba in sha Allah"ta kare a raunane, "Allah ya kiyaye na gaba kar kina ba wa shedan dama da kofar bata muku zumuntar ku domin duk duniya bana jin za ki samu kawa irin Zuhra babu ita kuma ba za ki taba samu ba,don haka dole ki koyi hakuri ke ma,ga can jakar a parlor ta bar shi ki dauka don ke aka kawo,saannn kiyi alola kiyi sallah an kira"daga haka ta wuce dakin ta,sim sim Sabeeha ta wuce bandaki saida ta yi tsarki sanann tayi alola tare da shige wa daki.

Ko da ta ida kan sallaya ta kwanta tare da lumshe idanu,tana ma rasa me daya take ji,wani zuciyar nace da ita a kira Zuhra ta bata hakuri,inda dayar Bangare na zuciyar na ce da ita ta Kyalle ta Ai babu wani abunda ta mata da har za a bata hakuri ita ce ma tayi mata laifi ta kara da kawo karan ta gida,don haka ta Kyalle ta in ta neme ta shike nan,da wanann shawaran ta gamsu kuma ta zauna a kai,wanann dare FIK kusan kwana yayi yana kiran ta da layuka daban daban don duk wanda ya canza ya kira ta ji shine sai tayi blocking,yayi text na ban hakuri da rokon ta saurare shi saboda Allah amman sam bata kula shi ba,karshe ma kashe wayar tayi baki daya ko ta huta,da wuri tayi bacci wanann ranar don tana ida Isha'i nan kan sallaya ta kwanta ko abincin dare bata ci ba,Kyalle ta Umma tayi kan in tayi ta gama ta fito,a haka bacci ya dauke ta ko ta kan jakar da Zuhra ta kawo domin ta bata yi ba.

**********************3 days later

A kwanaki uku da suka wuce din nan Sabeeha ba karamin damuwa take ciki ba,domin yanda ta dauki abun da ya faru tsakanin su da Zuhra har ya wuce hakan,tunda suke ba su taba kwana guda ba suyi magana ba sai wanann lokacin don gaba daya Zuhra ta fice a harkan ta,ko a makaranta ma ta canza gurin zama,kallo wanann baya hada su da Sabeeha balle magana,abun ba karamin damun Sabeeha yayi ba inda ta ga Zuhra ta banzartar da lamuran ta abun takaicin kuwa duk makarantar babu wanda ta sani suke magana sai ta zamo very lonely inda Zuhra ko vibe take da yan matan da Hostel din su daya ba tare da damuwa da Sabeehar ba.

A gefe guda kuwa FIK ya sauko ta gaba domin layuka sun fi nawa yake kiran ta da shi tana kin dauka tayi blocking ba shi zai sanya ya hakura ya Kyalle ba haka zai kusan kwana yana kira yana turo sakon ni,abun da ya fi komai bata haushi be wuce in ta tuno akan shi suka samu matsala da Zuhra ba.

Kamar kullum an tashi a makaranta ta ga Zuhra na kokarin barin class din tare da wata yarinyar da ta ga kwana biyu tana yawan shige wa Zuhran wace bata ma san sunan yarinyar ba,rai a bace Sabeeha ta mike tare da nufan su inda kafin ta iso har sun fice daga class din so bayan su ta bi cikin sauri ta ga sun dauki hanyar hostel da dan karfi ta kwalo mata kira

"Keee Goofy angel!!"sarai Zuhran ta ji kiran amman sai ta ja hannun yarinyar tare da kara sauri,hakan ne ya sanya zuciyar Sabeeha yin sanyi,ganin abun har ya kai Zuhra na jin tana kiran ta tana kin amsawa,ashe Gaskiya ne da ake cewa babu kyau kure me hakuri domin be iya fushi ba,sai yanzu ta tabbatar da ashe Zuhra tayi hakuri da ita a baya sosai,me ya shige ta har ya sanya ta mata abunda tayi bayan duk irin so da kaunar da Zuhra take yi mata,da sauri ta maida hawayen nadamar da ke kokarin zubo mata tare da kara sauri itama don ba karamin missing din ta tayi ba sanann bata fatan ta koma gida yau ba su shirya ba,da ta sani da ta dauki shawarar Umma tun day one ta bata hakuri tunda ta san Zuhra bata da riko ba kamar ta ba,amman ta dauki zuciya ta daura wa kan ta gashi yanzu tana kokarin rasa aminiyar ta.

Ko da ta iso hostel din gadon Zuhra ta nufa inda ta tarar babu ita,tambaya tayi inda aka ce da ita tana dakin su Aneesa yanzu shigowar su,da haka ta fito tare da shiga dakin su Aneesar kan gado ta hango ta suna ta shan hira kamar wasu Aminan juna😂,take ran ta ya baci inda ta nufe su fuska a tsuke

"Goofy angel ke don wulakanci kina ji ina kwala miki kira shine kika yi tafiyar ki ko?"ta kare kamar za ta yi kuka,ba tare da ta dago ta kalle ta ba tace "Ban ji ki bane Sabeeha da na ji kin san Ai zan tsaya kila kin kira lokacin muna tsaka da hira ni da Aneesa ne"ta kare kamar bata son magana.

Dan shiru Sabeehar tayi don ganin yanda Zuhran ta amsa ta kamar bata son magana da ita,ba abinda ya sanya ta jin haushi da kunyan kan ta ma kamar ganin da tayi ta banzar tar da ita sun cigaba da hiran su da Aneesan.

Hannu ta mike mata sanann tace "tashi mu tafi magana nake son yi miki pls"ta kare kamar me tsoron magana,kai Zuhran ta girgiza sanann tace "ki fadi koma miye zaki fada a nan Sabeeha hira muke kuma kamar an ci fuskan ta ne ace muna tare ki zo kiyi kira na in tayi tunanin za muyi maganar ta fa?Sanann ita shashasha har ana maganar arziki ne da ita da har za a ja ta gefe?Ai koma miye a fada a nan kawai"ta kare tana kallon Aneesa.

Dan kallon ta Sabeeha tayi ganin yanda ta tsuke fuska ya sanya ta kuma shan jinin jikin ta,nan ta ja ta tsaya cak a kan su inda suka cigaba da hiran su tsakanin suna dariya,ganin fa tabbas Zuhra bata da niyar sake kallon ta balle ma har ta kula ta,ganin haka ne ya sanya Sabeeha mika hannu tare da kamo hannun Zuhra,sai a lokacin ta dago ta kalle ta

"Sabeeha miye haka?Sake mun hannu na kar ki ji mun ciwo"baki Sabeeha ta murguda mata sanann tace "Wlhy ba zan sake ba Ai da nace ki taso muyi magana ki kika yi,to Allah yayi mun karfi,ko ki fito ko na dauke ki cak kamar baby mu fita"

"Haba Sabeeha tunda tace bata son maganar ki Kyalle ta mana dole ne?"harara ta watsa mata sannan tace "to yar karere ko wa ya kasa da ke ma balle ki dauka har ki sa baki,ina ruwan ki da takanin mu?Bana son shishigi"ta kare tana kan hararan ta tare da finciko Zuhran "Ke kuma fito mu tafi Wlhy sai mun yi magana ko ki so ko kar ki so,har wata banza can tana da bakin da za ta saka a maganar mu"ta kare tana kan jin haushin Aneesa,ita dai Zuhra bata ce komai ba bin bayan Sabeehar take tana yaba karfin hali irin na Sabeeha.

Saida ta janyo ta dan nesa da mutane sanann Zuhra ta fincike hannun ta "Ke ni fa kina ta ja na wai ina zaki kaini ne?"kallon ta Sabeeha tayi idanun ta sun fara ci kowa da kwalla a hankali ta nuna kan ta

"Goofy angel ni kike fada wa haka?"kallon ta Zuhra tayi sannan ta dauke kai tace "Sabeeha yanzu kuma me nayi miki?Ni Zuhra uwar laifi,don na tambayi ina za ki kaini shine abun magana?"

Narai narai tayi da idanu sanann tace "gaske wai fushi kike da ni?Ni ce fa Sabeehar ki,Goofy angel din ki,Zuhra har ni kika share na 3 days akan dan karamin abu?Har kin mance ni kin yi sabin kawa ko?"ta kare hawaye na zubo mata.

"Don Allah Sabeeha ya kike son nayi miki?Gani nayi kina bukatar space ya sanya na baki,and jira na ke na gama hankali tunda ni shashasha ce sai na nemo ki,kin ga ai abota da shashasha babu riba"ta kare da iya kan gaskiyar ta.

"Goofy angel don na fadi haka shine kika fita Harka ta?ke baki san raina ne ya bacci a lokacin ba"katse ta tayi a sauri gurin fadin "bacin rai?Sabeeha bacin rai fa kika ce?Ni da kika fada mun son ran ki nawa ran be baci ba ko me?Wai upon all people ni Zuhra za ki kalla ki ce wai an hada baki da ni don a cutar da rayuwar ki,Wlhy ni babu abinda ya fi bani haushi a duk maganar ki irin wannnan,dauka nake by now kin san wace ni ko wani na gani zai cutar da ke sai yanda karfi na ya kare balle ace ni da kaina wai za a hada baki da ni a cutar da ke haba Sabeeha kin mun adalci saboda Allah,laifi na a nan ina be wuce daukan nunber din ki da nayi na bai wa FIK ba ince shine laifi na?To kiyi hakuri ni dai Allah ya ga niya ta be zo gare ni da nufin cutar da ke ba balle na mara mishi baya,amman nayi kuskure don da na san haka zai faru tun farko da ban ma fara ba"ta kare a raunane

Jikin ta Sabeeha ta fada tare da rungume ta kam "Goofy angel don Allah kiyi hakuri kar ki dauke maganganun da na fada miki har zuciya wlhh bana meaning duk wani abinda na fada miki,na sani nayi hauka na kuma yi shashanci don ni ce ma shashashar ba ke ba da na kasa fahimtar ki har na fada miki irin wanann maganganun amman don Allah kiyi hakuri forget and forgive me kin ji don Allah ki manta ki kuma yafe mun kin ji?"ta kare tana hawaye hararan ta Zuhra tayi sanann tace

"Ni dalla sake ni an ki ayi forget and forgive din,ai wlhh Sabeeha kin ban mamaki kuma kin mugun bani haushi,har na dau wa kaina alkwarin daga ranar nima babu ni babu ke zan Kyalle ki kiyi rayuwar ki ki samu wace ba za a hada baki da ita a cutar da ke ba"

"Naki din Allah Zuhra in baki yafe mun ba ba zan sake ki ba,you are my best best girl and ba zan taba samun kamar ki ba nima na sani,na biye wa shedan ne da fushi amman Zuhran ta na sani ko gashin kaina ba za ta iya harming ba balle ni karan kaina,na san ban kyauta ba amman don Allah kiyi hakuri,I'm ready na karbi duk wani punishment din da zaki bani in har zai sanya ki hakuri,ni dai kawai ki ce kin yafe mun and we are still best friends"ta kare tana me narai narai da

"Ni matsa ki Kyalle ni na dai ni ce kika wa haka ba,ai Wlhy ya nuna babu yarda a tsakanin mu,ni ce kawai na yarda da ke amman ke kam gani kike da zuciya dubu nake zaune da ke,ina amfanin Amintar da babu yarda a cikin ta?"da sauri ta rufe mata baki da hannu

"Goofy angel don Allah kiyi hakuri ki bar maganan nan Wlhy na gane kuskure na kuma ba zan kara ba,don Allah kiyi hakuri mu shirya kin ji,ko sai na tsunguna za ki yarda ki yafe mun?"ta kare tana hawayen gulma.

Dan kallon ta Zuhra tayi sanann ta girgiza kai "dallah ki goge hawayen nan kafin a dau dukan ki nayi,ki kuma sake ni kar a dauka Lesbo ne mu"ta kare tana dariya,ita ma dariyar Sabeeha ta sanya sanann tace "ina ruwa na kowa ya dauki abunda yayi masa ni da ke mun san ba hakan bane,ba fa zan sake ki ba sai kin ce kin yafe mun"

Hararan ta Zuhra tayi sanann tace "Mayya na ji na hakura rabi ki jira in na tuna punishment din ki kika yi sai na karasa yafe wa sake ni to", "kai Goofy angel this is cheating amman babu yanda na iya na yarda duk sanda kika shirya ki fada mun punishment din koma miye ne zan yi,we still friends right?"ta kare tana washe baki.

"Kind of ki wuce mu je na raka ki kar Umma ta neme ki", "kai Goofy angel don Allah miye wani kind of,ni dai Wlhy ko kin ki ko kin so ba za mu taba rabuwa ba,ni da ke mutu ka raba takalmin kaza,kuma Wlhy ki ce wa wancan siririyar yarinyar kar ta kuma kula ki in ba haka ba zan balla ta,don Goofy angel kawata ce nawa ni kadai kowa ya nemo kawar sa"ta kare tana hararan dakin su Aneesa,dariya kawai Zuhra tayi tare da janyo ta suka fito daga hostel din,inda tayi ta bata hakuri,tare da sanar da ita irin missing din ta da tayi,har suka iso bakin gate,da kan ta tsaida me adaidaita tare da yin ciniki sanann Sabeeha ta shiga,babu yanda Sabeeha bata so Zuhran ta raka ta gida ba don Umma ta ga sun shirya amman tace za ta zo akwai abinda za ta yi tukun na,ta dai kula da kan ta ta kuma gaida Umma za suyi waya,da haka suka rabu suna daga wa juna hannu,kun san ance sabo turken Wawa duk sai suka tsinci kawukan su cikin matsananciyar farin ciki,da annashuwa na shirya wan da suka yi,Sabeeha har ta iso gida tana sakin murmushi ita kadan ta,don ba karya tayi missing din Zuhran.

Kamar kullum gidan cike ana ta gulma ta daga kai kamar bata san da zaman kowa ba tayi hanyar sashin su,don tuni ta daina gaida ko wace shegiya da shege da ke gidan,a tsakar gida ta tarar da Umma ta shimfida taburma tana zaune inda a dan gefen ta wani matashi ke zaune saidai bata ga fuskan shi ba,don ya bata baya,saidai tana hango lallausan bakin gashin kan shi da yake kwance luf kamar na jinjiraye,

"Hajiya Umma iska ake sha kuma yau?"kallon ta Umma tayi sanann tace "Auta sai yanzu kika dawo?Ya makarantar?"tana takowa gurin Umman tace "Wlhy Umma na tsaya gurin Zuhra ne yau dai mun shirya da kyar kin ga fushin da Goofy angel tayi,ban taba dauka tana da irin fushin nan ba"

Dan dariya Umma tayi sanann tace "Ai da bata hakura ba,dauka kike ke kadai ce me fushi duk duniya ko?ai ya sanya aka ce ka guji fushin me hakuri,sannan kure mutum a musulince ma babu kyau,amman tunda kun shirya to barka ubangiji ya kare na gaba"

"Ameen thuma Ameen Umma bako kike yi ne?"ta tambaya tana kokarin wuce wa  dakin ta, "bakon ki ne Auta ba nawa ba zo ki zauna,tun dazu yake zaman jiran ki"mamaki fal fuskan ta tace "Umma ni kuma bako na?"kai Umman ta gyada mata alamun eh hakan ne ya sanya ta dawowa inda suke din

Zama tayi kusa da Umma tare da cewa "sannu ina yini"murmushi kwance kan fuskan shi ta juyo tare da zuba mata shanyayun idanun shin nan yace cikin sanyin murya "Sannun da dawowa"

Da sauri ta mike tare da zaro idanu "Whattttt!!!You?Me kake yi a gidan mu?Me ma ya kawo ka gidan mu?Ba na ce ka fita harka na ba ko bance da kai duk wani abunda ya shafe ni ka goge shi ba?"

Cikin murya me rauni yace "Umma kin ji abunda take fada mun ko?Umma why ta tsane ni har haka?Kowa na laifi kuma yana tuba na bata hakuri har ban san so nawa ba,taki daukan waya na,taki responding wa messages dina,bani da wani option da ya rage na zo gida gurin Umma don na san za ta fahimce ni,tunda Uwa ce ita,Wlhy I have learned my mistake,and I'm a change person now ba FAIZAAN din da kika sani a baya bane"ya kare yana sunkuyar da kai.

"Change person na ji ka ce?Ko ba kayi learning mistake din ka ba,wai FIK kana tunanin har akwai dadin baki ko yaudaran da za ka yi mun wanda zai sanya na yarda da kai never!!!you better get going ka fice mana daga gida tun muna mu biyu"ta kare a harzuke kamar za ta sa mai duka.

"Ke Sabeeha lafiyar ki kuwa?Wani irin abu ne haka"Umma ta fada da dan fada,da sauri yace "Aa Umma don't shout at her,tana da each right din da za ta yi fushi da ni,tunda abunda nayi nima tun farko nan kyauta ba amman Wlhy wancan FIK din da wanann new FAIZAAN din ba daya bane,na canza ki yarda da ni don Allah"

Kallo ta watsa mishi irin kallon sai kayi din nan sanann ta ja tsaki kasa kasa tare da yin wucewar ta daki,kunya ne yayi mugun kama Umma tare da mamakin wanann murdaddiyar hali irin na Sabeeha,yaron nan har kuka yayi a gaban ta be boye mata komai ba ya bata labari tare da nuna tsastan nadamar shi,sannan ya gwada wa Umma shi a shirye yake ya dauki komai za ta masa don da gaske son ta yake kuma Auran ta yake son yi,kallo daya Umma tayi mishi ya shiga ran ta don ba karamin nutsuwa da biyayya tare da yaba hanklain shi tayi ba,

Da kallo ya bi Sabeeha sanann yace "na sani Umma it will take time kafin ta sauko don tayi fushi sosai amman I will wait for her duk sanda ta sauko ba zan gaji ba,zan zo kullum na bata hakuri har sai ta hakura"ya kare yana murmushin dole

"Kayi hakuri da abinda tayi maka Sabeeha har yanzu da yarinta akan ta amman zan mata magana", "Haba Umma babu komai Wlhy kome tayi nayi deserving haka,don Allah Umma kar ayi mata fada don bana son ran ta ya kuma baci"dan dariya Umma tayi tare da girgiza kai don daga zuwan shi ta gano yana da barkwanci tare da dadin zama,sanann ko a jikin shi ba kunya ba komai ya sanar da Umma shi fa mutuwar kaunar Sabeeha yake har abun ya ba wa Umma mamaki tace oho yaran zamani sai Allah,nan ya durkusa har kasa tare da yi wa Umma sallama,sanann ya tafi zuciyar shi kal don ya tabbatar ya siye zuciyar Umman Sabeeha siye na Sabeeha zai zo masa da sauki.......

  A yi hakuri da Typing errors Keyboard dina ke bani matsala.

Kar a manta da comment da share saboda Allah.

Ina yi wa kowa fatan Alkhairi 🥰

Continue Reading

You'll Also Like

31.3K 5.2K 15
In the elite ranks of DRDO, Ardik Rajwasnhi, a young prodigy, is fueled by ambition to secure a coveted position among the legendary Team Phoenix. Ho...
128K 12.9K 32
Athulya Singhania has spent her entire life in solitude, yearning for the love of a family. Over the years, she mastered the art of concealing her em...
Khalifa By laiba

Mystery / Thriller

2.1M 118K 56
✵ featured ~ ❝Once upon a time in Baghdad, a street girl teaches the Khalifa of the kingdom why a king needs a queen.❞ ✵ Started: June 5, 2021. Comp...
50K 1.4K 81
"𝐻𝑎𝑛𝑠𝑒𝑜𝑘𝑎𝑎,𝑎 ℎ𝑒𝑎𝑟𝑡𝑙𝑒𝑠𝑠 𝑝𝑠𝑦𝑐ℎ𝑜𝑝𝑎𝑡ℎ 𝑙𝑖𝑘𝑒 𝑦𝑜𝑢 𝑑𝑜𝑒𝑠𝑛'𝑡 𝑑𝑒𝑠𝑒𝑟𝑣𝑒 𝑡𝑜 𝑓𝑒𝑒𝑙 𝑙𝑜𝑣𝑒 𝑤𝑖𝑡ℎ 𝑠𝑜𝑚𝑒𝑜𝑛�...