A SIMPLE DARE (WASA DA SO)

Von marteybee

434 7 16

Mehr

new book
Page 2
Page 3
Page 4
Page 5
Page 6
Page 7
Page 8
Page 9
Page ten
Page 11
Page 12
Page 14
Page 15
Page 16
Page 17
Page 18
Page 19
Page 20/21
Page22/23
Page 24/25

Page 13

16 1 5
Von marteybee

✨✨

SIMPLE

DARE

                              ✨✨

(WASA DA SO)

WRITTEN AND STORY
       BY
NERNAH MARYAM
(MEEMARH)

 
             Kofa a bude take ga duk me son yin joining group dina😌,Amman Hajiya don Allah in kin san ba yin comment ko karanta littafi na zai kawo ki ba I beg you in the name of Allah kiyi zaman ki ba sai kin shigo ba!!haka zalika wanann group din na mata ne zalla don Allah Maza should stay away from my group👏

       My What's app group link👇🏻

           https://chat.whatsapp.com/EUrVVaKJnIBDTlQsxurZv0

Bismillahi Rahmanin Raheem............

(    In the name of Allah the most beneficient,the most merciful)

 
  Kofa a bude ta ke ga duk wani me good quality product da ya ke son Advertising ɗin shi,as Kaya masu kyau,da inganci (TALLAH) should contact me via :
                              08100046388

Page 1️⃣3️⃣

TALLA!!TALLA!!TALLA!!!

       https://chat.whatsapp.com/ImtxMSS1tuSKqvBpPqc03P

Assalamu'alaikum sisters🤗
KAMSHI* mace Mai kima, mace Mai daraja, mace Mai izza, mace Mai aji itace tasan darajan kamshi, if your perfume is not unique hajiyata you're just using ordinary air freshener🤣, hajiyata ko nawa Zaki kashe indai a turare ne baki Fadi ba😘 matan da suka gane suka San yanda zasu kankaro da martabar su, suke amfani da turare, a *BAKHOOR BY FAIXY* Zaki Sami Main chic, Bachelor, Husband snatcher, Her royal sexiness, Mysterious girl, Pleasure, Boovilous, White khumra, Maroon khumra, Black khumra, Hair perfume, Turaren wanka, Turaren  wuta, Turaren tsuguno, Turaren mopping,Turaren carpet Shu'umat khumra,and more, yar uwa kar kibari abaki lbr, (wholesale and retail) WhatsApp 09067621681, siyan na gari Maida kudi gida🥳

Instagram @Bakhoor_by_faixy

******************************

Da sauri Zuhra tace "kina son ki ce mun FIK??"ta kare tana zaro idanu saida ta fada kuma tayi saurin rufe bakin ta da tafukan hannun ta deep down tana fadin "Oh shit wanann baki nawa wataran sai ya kai ni Prison"..........

Idanu Sabeeha ta zuba mata sanann tace "FIK🙄🙄Zuhra FIK kuma ke kullum baki da zance sai na wancan arrogant person din,me ya hada FIK da mutumin da nake baki labari?Ina miki tadin mutum me kirki me mutunci wanda ya san darajan yan Adam kya wani ce da ni FIK don wahala ke kullum baki da zance sai na shi" ta kare tana maka mata duka tare da watsa mata harara kamar idanun ta sa zubo kasa,abun ku da me manyan idanu.

Wata wawiyar ajiyar zuciya Zuhra ta sauke tare da murmuring "Alhamdulilah"kasa kasa sanann ta kalli Sabeeha kafin ta dan kwade kan ta,tana me godiya wa Allah da Sabeeha bata gano ta ba.

"Goofy angel kin san wani na gani me kama da shi ya wuce yanzun nan,shine na ke son nuna miki mutumin ki"ta kare tana dariya,tsaki Sabeeha ta ja kafin tace "wlhh Zuhra kina da abun kunya banda kayan raini ina ruwan ki da wani can wai FIK ko FUK??Ke dai kullum baki da zance sai na shi,to wai ko dai son shi kike bani da labari?"ta kare tana tsare ta da idanu wa.

"Subhhanalli!!!Sabeehatu!!!don Allah ki rufa mun asiri,ina ni ina FIK wace ni da shi?Wanann Ai sai ku manyan mu", "Wlhy Zuhra zan ci uban ki in baki bar hada ni da sakaran yaron nan ba kina hauka ne??Ina ruwan Biri da ga'da in banda shashanci irin naki?Haba ke baki da zance sai na shi,ni dai in son shi kike tun wuri mu san nayi,amman ni Sabeeha kam babu ni babu shi,and it's will be better for you to stay far away from him don ba mutumin kirki bane,tun wuri ki raba ni sanann ki raba kan ki da batun wani FIK in ba haka ba you go see shege"ta kare tana hade rai tare da hararan ta.

Dan dariya Zuhra ta danne sanann tace "dadi na da ke saurin fushi Sabeeha waya ce miki son FIK nake??Kawai dai ce miki nayi na ga me kama da shi ne ya wuce,so why all this long lecture??And ko kaffara ba zan yi ba in na rantse FIK is not that bad as you think kin ki ba wa kan ki daman fahimtan Waye shi ne,amman yana da kirki sosai wlhy"

"Excuse meeee!!!Goofy angel don't tell me is  true abunda nake tunani?Yaushe kika san shi har kike bada shedan kirki akan shi?"ta kare tana tsare ta da idanu.

"Ko na san shi ko ban san shi ba Sabeeha d'an Adam
ne shi,dole yana da good da bad halaye babu yanda za ayi ace Allah ya tara masa mugayen halaye ba tare da kyawawa ko da kadan ne ba,and a labari na ji yana da halin kyauta duk wani me kyauta kuma Ai kin ga alamun mutumin kirki ne,so pls don't just judge a book by it's cover and ki sassauta irin wanann tsanar da kike masa domin bayi da amfani sam,as far as zan iya tunawa mu muka masa laifi amamn shi ya zo yana neman shiri da mu,inda wani ne ko zai yi yawo tsirara kin san sai ya rama marin da kika yi mishi,amman rashin ramawa da be yi ba har yau shiru be kuma yi komai ba shows that he is actually a gentleman!!!!so pls no need of holding grudges anymore ki manta ke ma da abunda ya faru ko ma zauna lafiya mu fahimci juna duka"

"Ke dalla yi mun shiru!!!Sannu nace sannu Zuhra Wlhy abu daya da yake hada ni da ke rashin wayon ki,ko hauka nake ni ce zan zauna har na fahimci waye shi to akan me ma ??Akan wani dalili??Keee ni fa haka kawai yaron be mun ba ko kin manta abinda ya fara hada mu da shi ne???"ta kare tana tsare ta da idanu wa

"Ban manta ba Goofy angel ko da ace labari kika nan ya ci ace na haddace na kasa mantawa balle akan idanu na komai ya faru,I'm just saying kiyi kokarin kyautata masa zato tunda shima Musulmi ne dan uwan ki,yanda kike sallah shima haka yake yi,so why za ki zauna kina ta jin haushin shi tare da tsanar shi?"

Dan shiru Sabeeha tayi don ta ma rasa abun fada saida Zuhran ta riko hannun ta tare da damkewa cikin nata alamun kin ji pls sanann ta iya budan baki tace "can we stop talking about him pls???and can you hear me out pls?Labari nake baki kin katse ni kin shiga na wani can daban so kina iya saurara ta na karasa miki ko kuma nayi tafiya ta yau it's gonna be a busy day for me got a lot to do"ta kare tana hada kan jakar ta don bata ga amfanin zama da Zuhra yau tana mata tadin yaron da take ji duk duniya babu wanda ta tsana irin shi,and ko shakka babu ita ma ta san ya tsane ta,hauka ma ashe take ta saki Jiki da shi,yaron da tarbiyya ma be ishe shi ba,duk da itama har yau in ta tuna da ta mare shi bata bashi hakuri ba,sanann be yi mata komai don ramuwa ba banda haka ma sai taimakon ta da yayi ta yi don ma ta hana shi,jikin ta ya kan yi sanyi tare da jin tsoron ko yana planning something big ne??saisa kullum idanun ta bude suke tana jiran ta ga ta inda zai bullo don a yanda Zuhra take bata labarin su ta san ko ita kanwar uwar shi ce ta mare shi Wlhy sai ya rama,ta rasa me ya shiga kan kawar nata yau har take yabo tare da kare shi haka,banda ta san Zuhran ta mace wa Habeebeey Ai da sai tace son FIK din take yi.

"I'm sorry babe ni ba na fadi haka don na bata miki rai bane,just saying abunda nake gani kamar ya dace ne,ina jin ki"saida ta harare ta sanann tace "wa Ai na gama miki labarin bani karasawa kuma yar iya"ta kare tana hararan ta.

Rungumo ta Zuhra tayi tare da manna mata kiss a kumatu sanann tace "zo mu shirya kawata FIK din banza in dai maganar shi ne baki so am gama daga yau"ta kare tana narai narai da idanu,saida ta kuma maka mata harara sanann tace "Allah ya so ki yau ina cikin farin ciki yasin da nan gani nan bari ba zan karasa miki labarin ba haka zalika ba zan baki ko ficika a cikin kudi na ba eheee"

Dariya Zuhra ta kwashe da shi kafin tace "Ke kin isa!!yasin ba ki isa cin kwandala babu Zuhra ba ke ma kin san ni da ke hanta da blood ne in daya baya nan dayan ma babu shi,kar ki manta ke wata ni Zahra so ni da ke mutu karaba takalmin kaza,maza karasa mun labarin".

Saida ta dan kwade kan ta sannan tace "sai shegen dadin bakin tsiya,ki cigaba da mun iyayi da rawan kai in ina baki labari wataran sai na kama ki na tusa miki pepper a cikin bum bum din ki"

Dariya Zuhra ta kwashe da shi "Wlhy Sabeeha mugunta a gurin ki ya kare,hauka kike ki tusa mun yaji a duwawu??Wlhy Habeebey sai ya daure mun ke"ta kare tana hararan ta.

"Habeebeeyn banza Habeebeeyn hofi,ya isa ya kama ni ya ji da kan shi dallah", "aa Goofy angel duk abu na fada miki banda Habeebeey,Wlhy za a mugun jin mu da ke in kina zagin shi"ta kare tana hararan ta.

Saida itama ta rama hararan ita ma sannan ta gyara zama ta shiga bata labarin yanda suka yi da Mr I love you a daran jiya,ta kare tana fada mata kan yanzu in an tashi za su biya kasuwa suyi siyayya tare.

Dan ihu Zuhra ta saka tare da rungume Sabeeha kam kam "Goofy angel nayi murna wayyyo!!!Wlhh na ji dadi sosai Allah ya sa ya bude mana kofofin Alkhairi ke nan,Allah ya saka masa ya kara budi sanann ya sa ki zamo matar shi don da dukkan alamu kaunar ki yake yasin"ta kare tana daga mata gira daya tare da kashe mata ido daya.

"Zan ci uban ki,Zuhra zan zagi whole generation din ki,Bura uba ke fa dadi na da ke tabin hankali Wlhy,are you and or something???Daga ganin sarkin fawa sai miya ta yi zagi,waya ce miki so na yake har kina wani adduar zama matar shi"

"Kai Goofy angel Wlhy kina da mugun matsala,to wai don Allah in baki yi aure ba ni zan aure ki??ko kuma haka za ki koma ga Allah ba aure??"

Kai kawai ta girgiza sanann tace "Haihuwa Aure,Mutuwa duk lokaci ne,Goofy angel in lokaci yayi ko na so ko kar na so haka zan yi aure so chill okay"shiru kawai Zuhra tayi coz in tace za ta yi magana ma bata san abun fada ba,inda deep down ba karamin dadi ta ji da jin abunda Sabeeha ta gama fada mata ba,tayi murna sosai ta kuma yi farin ciki,don ko ba komai ta san za su huta ita da Umman ta na kwana biyu,saidai abu daya da ta fahimta shine Sabeeha bata gane FIK bane wanda hakan be wani ba ta mamaki ba don ya Riga ya fada mata bugun farko ba zai nuna mata kan shi ba,abun aikin a nan shine yanda ta ga Sabeeha ta mugun tsanar FIK ko maganar shi ma bata son ji,daman cikin dabara ta dan bugi cikin ta dazun amman ga dukkan alamu akwai aiki babba a gaban su gurin ganin ta watsar da tsanar da tayi masa tare da kokari gurin ganin sun jawo hankalin ta har Allah ya taimake su ta fada soyayyan shi,"in ko da haka zai faru da na fi kowa farin ciki wlhy,cute cute babies alert"ta kare tana murmushi.

Kallon ta Sabeeha tayi sanann tace "miye in ya faru za ki ji dadin??And cute cute babies alert din ta mecece wace tayi aure ko za ta yi??"ta kare tana kan kallon ta,dan kwade kan ta Zuhra tayi domin sam bata ma san taya zancen zucin ta ya fito fili ba.

"Ke tunanin Habeebey nake yi in mun yi aure zan fi kowa jin dadi,haka zalika yaran mu ba karamin kyau za su yi ba,har ina ganin su a idona"dariya Sabeeha ta kwashe da shi sanann tace "Amaryan Habeebey Zuhra in baki auri Mansoor ba ina jin sai kin sha fiya fiya ko zuciyar ki ta buga,Allah ya kyauta tashi ni kam mu tafi tunda an gama classes mu samu mu shiga kasuwa bana son shiga kasuwa da yamma Wlhy in ba haka ba sai ki ga kafin ka ankara Magrib tayi and babu kyau mace tana kai wa Magrib akan titi in ba da kwakwaran dalili ba"ta kare tana mike wa.

Tashi Zuhran ma tayi tare da gyara zaman dan kwalin ta sanann ta janyo Hijab ta saka sanann tace "Oya mu tafi rabin rai ta,yau ni da kaina zan yi miki baking cake din ma na hutar da ke"harara Sabeeha ta maka mata kan tace "dallah sai kace kin iya kwabin cake ma ba iya shi kika yi ba balle akai ga baking".

"Kina shirun ki goofy angel I will surprise you Ai ina ganin yanda kike yi,yanzu dai mu tafi kar mu bata lokaci and wani kasuwa za mu?"

"Ke dai dauko kayan da za ki bukata don kwana fa zaki yi,kasuwa kuma inda na saba siyayyan kayan snacks dina shagon Junior nan za mu je mana"daga haka kuwa suka hada kan komai sannan suka fito suna tafe suna hira har suka fito bakin gate babu abun hawa babu alamun shi.

Tsaki Sabeeha ta ja "Wlhy goofy angel na gaji da wanann tafiyar gaskiya, numfashi na har yana neman tsarkewa haba gaskiya ya kamata kiyi mana saurayi dan Napep da zai na dawainiyar kai mu school yana maido mu gida"

"Kut Goofy angel Wlhy kin ma raina mun wayo,in fitsari banza ce kaza ma tayi mana,why not ke kiyi mana saurayin in kina ga abu me sauki ne"ta kare tana murguda mata baki,dariya Sabeeha ta kwashe da shi sanann tace "chill baby girl Ai sarai kin san ni soyayya bata gaba na ne da yasin a ko ina sai nayi saurayi"

"Look who is talking don Allah,ke me ma kika sani game da soyayya shegen tsoro ya hana ki bude heart din ki ki sanya wani ciki,for Allah sake Sabeeha baki ganin kara girma muke kar muyi wa Allah butulci mana tunda Alhamdulilah ya hore miki manema na gani na fada just take a look at this secret admirer of yours bawan Allahn nan is doing all his possible best ya ga ya burge ki ya janyo attention din ki,ki ga irin kudaden da yake kashe miki,Sabeeha ga irin Abayoyin da yake aje miki kullum ga chocolates ga turaruka masu masifan kamshi da tsada,amman na rasa gane wa ko Zuma rock ne a cikin heart din ki da ke danne duk wani feelings da ya kamata ace mace ta ji,haba mutum kamar wanda Aljani ya aura,Ni dai ko dai Aljanu sun aure ki ne Sabeehatu muna zaune ba mu sani ba?"ta kare tana riko ta don kare mata kallo da kyau don lamarin Sabeehar sai Allah.

"Kin sake ni ko sai na miki rashin mutunci,Alajnnin lafiya in har ba ke ce Aljanar da kika aure ni ba to ni babu wani Aljanu a tattare da ni,Zuhra wlhy in baki bar ni da maganar soyayya aure soyayya aure din nan ba yasin zai miki wulakanci,soyayya mato ke kam ba kina jin dadin naki soyayyan ba to a cigaba da yi nima bari in right time ya zo zan yi,amman for now har yanzu ina kan baka ta babu soyayya a tsarin rayuwar Sabeeha"ta kare tana fauce hannun ta.

"Amman Goofy angel ke kan ki kin san baki taki Gaskiya ba dai ko??", "Zuhra!!!na roke ki ki Kyalle ni da maganar nan mu ji da uwar ranar nan da ake kwalawa yau kina gani dai wasa gaske mun rasa abun hawa gashi lokaci sai tafiya yake kafin ki ankara yanzu za a fara kiraye kirayen sallan La'asar amman kin tsaya kina ta surutu ko a jikin ki"ta kare tana make kafadan ta.

Ta bude baki da niyar yin magana sai suka ga wuce war wata wata Honda 2016 Silver color kai daga ganin motar ka san sabuwa kal ce,banda shinning babu abinda take yi,da sauri Sabeeha tace "Goofy angel babu abunda zai hana ni siyan motar nan in sha Allahu in nayi kudi,wlhy motar ba karamin kyau take mun ba"ta kare tana murmushi.

"Ke dai Goofy angel akwai ki da son mota da sutura da kamshi Wlhy,motar kuwa ba laifi tayi kyau,amman daga gani za ta yi kudi", "banda abun ki Ai cewa nayi nima sai nayi kudin,surura da kamshi duk macen da ta san kan ta take amsa sunan ta na mace to dole ta so sutura da kamshi"rufe bakin ta ke da wuya suka ga motar tayi parking a gaban su,wlhy ba su ma san lokacin da motar ta dawo baya ba,ganin haka ne ya sanya suka kalli juna Zuhra ce tayi murmushi sanann tace "God bless your beauty Goofy angel kin ga za a dauke mu kyauta kudin abun hawan mu ya huta,kila ma saurayi za kiyi"wata uwar harara Sabeeha ta maka mata sanann tace "Allah ubangiji ya shirya ki kin wuce mun tafi ko kuwa?"

Ganin suna kokarin wucewa ne ya sanya shi zuge glass din motar shi,dan leko wa yayi sanann ya sake musu kayatattciyar murmushin shi me tafiyar da zuciyar yan mata,sanann cikin sassanyar murya kamar ba tashi ba yace

"Hello"juyowa Zuhra tayi inda Sabeeha ta daga kai kamar bata san da su yake ba,nan take Zuhra ta saki murmushi tare da fadin "laaa Sabeeha kin ga FIK ne"

A zafaffe kasa kasa Sabeeha tace "FIK din kaniya Kanin Uban mu ne da za ki wani ce laaa ashe FIK ne to sai me?" "Ke dai Sabeeha Wlhy ba dai dacin hali ba"ta kare tana hararan ta.

Daidai lokacin FIK ya bude kofar motan tare da fitowa yana sanye cikin ash din trouser da milk shirt inda ba karamin kyau yayi ba gashin kan san nan sun kwanta sai kyalli suke gwanin ban sha'awa.

A gaban su ya ja ya tsaya sanann ya yi folding arms din shi as usual kafin a hankali yace "Assalamu Alaikum"ba tare da Sabeeha ta kalle shi ba ta amsa sallamar ciki ciki,saida ya dan kalle ta sanann ya kalli Zuhra da ido ya tambaye ta kan me ke damun kawar nata?Inda ta amsa mishi da itama bata sani ba,ganin yayi shiru ne ya sanya Sabeeha kallan Zuhra tace

"Can we get going pls kar time ya Kure na fada miki today is gonna be a busy day for us,kin kuma tsaya neman bata mana lokaci", "amman Goofy angel kya tsaya dai mu gaisa da shi ko tunda sarai kin san saboda mu ai ya tsaya"

"Saboda mu???Haka aka ce da ke to in ma saboda mu ne saidai ke domin ni ba sanin shi nayi ba,haka zalika shima be san ni ba,so ki wuce mu tafi tun raina be gama baci ba"ta kare a zaffafe don ta rasa wanann rawar jiki da Zuhra ke yi akan wanann mara ta idon yaron.

Cikin sanyin murya yace "Anty Goofy angel sorry na tsayar da ku ko,daman na tsaya ne mu gaisa ganin it's been long da muka hadu,where you guys are heading to?In baku damu ba ba sai na kai ku ba,don na ga alamun kaman babu abun hawa and akwai rana sosai yau"ya kare yana murza azurfan yatsar shi.

"Kasuwa za mu je daman,Wlhy kuwa yau abun hawa yayi wahala,mun ko gode sosai"Zuhra tace tana murmushi,da sauri Sabeeha ta juyo tare da galla mata wani banzan harara sanann ta damko hannun ta gam cikin nata kafin tace "kayi tafiyar ka mun gode na kira me abun hawa na yana hanyar zuwa daukan mu"

"But...." , "don Allah ba wani but ba yara bane mu we can handle kawukan mu so just take your leave mun gode sosai"ta kare tana jan hannun Zuhra da karfi suka bar shi tsaye a gurin

"Haba Sabeeha tsakani da Allah wai miye damuwar ki ne??Bawan Allahn nan tsanar wai ta me cece kike tayi masa ki duba saboda Allah ya ce zai kai mu amamn saboda bakin hali irin naki kin gwammace mu taka cikin ranar nan?"ta kare ran ta bace

"Kin san Allah Zuhra in baki raba kan ki da maganar yaron nan ba zan miki Bura uba,A ina kika san shi da za ki shiga motar shi??Ke saboda hauka irin naki yanda kike ganin zuciyar ki pure ne ba za ki iya cutar da kowa ba haka kike kallon na kowa??A ina kika san shi da har kika ji zaki iya yarda da shi?Nan ina kike bani labarin irin rashin mutuncin su ko kin mance Waye shi in tuna miki?FIK dai leader na Rocket gang wannan mara mutuncin yaron da baya mantuwa balle yafiya,amman na rasa gane wanann rawar jiki da kike in kin gan shi Zuhra ko dai kin kamu da soyayyar shi ne ni kam bani da labari?"ta kare tana tsare ta da idanu.

"Soyayya?Allah ya sauwaka taya ma za ki yi irin wanann tunanin miye riba na in na tsane shi,hasali mun masa laifi amamn shi ke kokarin ganin ya ba mu hakuri amamn kin kasa fahimta balle har ki bashi chance,Sabeeha wanann bakin zuciyar taki ba inda za ta kai ki fa,haba abu yau kwana nawa da faruwar shi ana neman fin wata amamn kin gaza mancewa,sanann me laifin don yace zai kai mu kasuwa a motar shi saboda Allah,ni dai Wlhy ban ga laifin shi ba"ta kare tana turo baki gaba.

"Kin san Allah Zuhra Zuhra Zuhra kin ga dai sau uku na kira ki ko?To Wlhy in kika ce za ki damen ko za ki ishe ni da maganar wanann yaro to ba shakka zan kira Mansoor na sanar da shi,ba zai yu ba Wlhy kin fara fin karfi na,kin ga kila shi in ya tambaye ki sai ki fada mishi me ke tsakanin ki da FIK din"ta kare tana yin gaba,harara Zuhra ta bi bayan ta da shi sanann kasa kasa tace "Wawa sai kace ba don ke nake komai ba,harda wani zaki kira Habeebey ki fada wa,to ki fada masa mana"ta kare tana Jan tsaki,juyowa Sabeeha tayi sanann tace "magana kike yi ne???"

"Maganar lafiya ni ban ce komai ba"dariya Sabeeha ta kwashe da shi sanann tace "in kin ga dama idanun ki su fado kasa kina harara na ko tongue din ki ya tsinke motar FIK dai ba za a shige tan ba,kin ga gama can Keke yana tahowa Allah ya sa ba kowa a ciki"

"Ba Ameen ba Allah sa cike yake da mutane kin ga sai ki ji dadi mu taka da kafafuwan mu har kasuwa"ta kare cikin bacin rai, dariya Sabeeha ta kuma
Sanya wa sanann tace "shike nan kuwa mun motsa jini mun kona kitse Wlhy na gwammaci mu taka da kafafuwan mu har kasuwa da mu shiga motar wancan mutumin da be san darajan yan Adam da mata ba"ta kare tana Jan tsaki,cikin saa kuwa sai ga me adaidaitan ya iso empty babu kowa ciki so hannu Sabeeha ta sanya tare da tsayar da shi,nan ta fada mishi inda zai kai su tare da yin ciniki sanann tace da Zuhra ta hau su je in tana da niya.

Har suka iso Zuhra bata kula ta saidai in tayi magana ta amsa ta da kai kawai,ita ala dole fushi take Sabeeha ta ki bari su shiga mota me AC,bayan sun sallami me adaidaitan ne suka biya gurin me POS inda Sabeeha ta cire kudin sai murmushi yake ita kadai,tare da jin dadi za su samu suyi chefane ko da na kwana biyu ne za su huta.

Shagon da ta saba siyayya ta nufa inda suna daga zaune aka hado musu duk wani abunda suke da bukata ta biya aka zuba musu a Leda sanann suka fito,Sabeeha na ta Jan Zuhra da hira amman ina Zuhra fa tayi fushi saida suka zo bakin titi ne sanann Sabeehar ta kalli Zuhran

"Goofy angel wai fushi kike da ni??To kiyi hakuri don Allah ki sake ki bar fushin nan kar mu isa gida Umma ta ga kina fushi Wlhy fada za ta yi mun,ni gani nayi ba mu san shi ba ya sanya nace kar mu shiga motar shi amman na ga kamar ran ki ya baci"harara Zuhra ta maka wa Sabeehar don in a duniya akwai abunda Sabeeha ta tsana to ta share ta ko ta nuna tana fushi da ita nan take duk hankalin ta zai bi ya tashi.

"Ni ba fushi nake ba Kawai dai Goofy angel yanda kike yi ne bana jin dadi,ba a ko wani lokaci ya kamata mutum yayi ta fushi da fada ba,tunda na ga ba da fada ya neme mu ba in ma ba za mu shiga motar na shi ba ba sai muyi rabuwar mutunci ba,wlhh be tafi ba saida ya ga mun samu abun hawa mun tafi kafin ya ja motar shi,just to make sure muna safe and sound I don't think yana nufin mu da mugun nufi ne,try ki ga good a jikin shi ba kullum kina masa kallon mara mutunci ba don Allah mu kyautata wa mutane zato"ta kare ta iya kan gaskiyan ta.

"To Goofy angel in sha Allah zan kiyaye yanzu dai ki ce kin hakura kin bar fushin"dan murmushi Zuhran tayi sanann tace "mu tafi kar yamma ya yi mana na hakura Goofy angel daman nima fushin karya ne amamn kin san ko ke kika mun ban isa yin zuciya ko fushi da ke ba,you are my world best best friend fa"Murmushi Sabeeha tayi sanann tace "and forever is the goal between us in sha Allah kawancan mu har yara da jikokin mu da yardar Allah yanzu dai taho ga abun hawa na tsaida mana"ta kare tana riko hannun ta yaro almajiri da ya dauko musu kayan su yana biye da su,saida suka yi ciniki sanann suka biya yaro almajiri tare da karban kayan sanann suka tafi suna tafe suna hira,har suka iso suka biya kudin me adaidaitan sanann suka kwashe kayan tare da shige wa cikin gida suna kan hira abun sha'awa,da mugun kallo Latifa ta bi bayan su sanann ta ja wani irin mugun tsaki in a duniya akwai wace ta tsana bayan Sabeeha to wanann shegiyar kawar nata ne Zuhra me kama da tsuntuswa.

Ba su ko kula da ita ba ma balle su tanka ta kai tsaye shashin su suka nufa,inda suka tarar da Umma da Shatu yar gidan kanin Mahaifin ta ne ba laifi ita kam suna mutunci da ita don yarinyar bata da matsala ko kadan.

"Ah hajiya Umma hira kuke ta sha abun ku ko sallamar mu ma baku ji ba"Sabeeha ta kare tana nufan inda Umman ke zaune,murmushi Shatu tayi sanann tace "Adda Sabeeha kun dawo tun dazu muke zaune jiran shigowar ku"ta kare tana mike wa tare da karban abubuwan hannun su,tare suka durkusa ita da Zuhra suna me gaida Umman inda ta amsa cike da sakun fuska sanann tace da su maza su tashi su watsa ruwa sun ibo rana sai tsami suke ta faman yi.

Cike da turo baki Sabeeha ta shige daki tana ihun "Umma yasin saidai Goofy angel ke tsamin amman ni kam har yanzu kamshi nake"ba tare da Umma ta kula ta ta ba ila mike wa tayi tare da shigewa kitchen don fara hada abubuwan bukata.

Saida suka yi wanka duka suka yi sallah tare da cin abinci sannan suka zo suka sanya hannu a aikin,wasa gaske ba su suka gama ba sai guraran bayan Magrib Sabeeha ta sanya Cake din da tayi baking kan sai zuwa gobe da safe sai tayi icing din shi,su Samosas din ma ba su Riga sun soya ba sun dai saka a fridge gudun lallacewa,shi kuma meat pie da Donut suka bar su kan duk sai goben za a tashi akai ganin an ci karfin aikin,don Donut free yafi dadin ci ya sanya inda aka yi order din Donut da Meat pie ba su cika yi ba sai washe gari in ba sassafe ake da bukata ba.

Saida duk suka kuma wanka sanann Sabeeha ta baiwa Shatu 7k kan ta karbo musu tsire na 5k da drinks na sauran canji,ba tare da bata lokaci ba kuwa ta dawo inda duk suka baje ana hira ana cin nama,banda murmushi da kallon Sabeeha ba abunda Umma ke yi,don ko ba a fada ba ta san yau yarinyar nata tana cikin tsanani farin ciki,ta san Sabeeha sarai da son nama kamar wata kura ya sanya bata wani ci da yawa ba ta tsame hannun ta tare da barin su tayi shigewar ta daki.

Wanann ranar sai guraran 12 Shatu ta wuce shashin su inda Sabeeha da Zuhra suka yi alolan bacci tare da yi wa Umma saida safe suka wuce daki,tunda Sabeeha ta sanya kanta a pillow ta ji idanun ta na lumshe wa da kyar ta samu tayi Azkars din bacci,sannan ta kalli Zuhra da ke ta faman kashe murya wa Habeebey,kai ta girgiza don wanann soyayya ta Zuhra sai dai a bar ta,kiss ta manna mata a kumatu sanann a hankali ta ce "Kar ki manta da adduar bacci in kin gama soyayyar Good night Goofy angel ki mika sakon gaisuwa ta wa Habeebey"daga haka ta ja blanket tare da lumshe idanun ta sai bacci.

Tunda suka yi Asuba ba su koma bacci ba aiki suka shiga,saida gari yayi haske sosai sannan Shatu ta shigo ta kama musu,Allah ma ya taimake sun yau Asabar babu sch ya sanya hankali kwance suke aikin su,gama decoration din birthday cake din inda tayi masa decoration din cartoon din Sophia the first inda ko ba karamin kyau yayi ba,waya ta dauko tana yi wa cake din hoto domin ita kan ta ya burge ta sanann ta sanya shi cikin carton ta rufe sanann ta maida fridge

"Goofy angel tsakani da Allah kan idanu na kika gama hada cake din ga duk soyayay ta da cake ko dan dan baki bani ba kin mun adalci ke nan"Zuhra ta kare kamar za tayi kuka duk ta bade jikin ta da flour ala dole ita tana kwabin Donut.

Dariya Sabeeha ta fashe da shi sanann tace "Umma fito ki ga Matar Habeebey na aiki,yanzu tsakani da Allah Goofy angel ga yanda kika yi budi budi da flour kuma wai a haka za a miki Auran??"

Hararan ta Zuhra tayi sanann tace "ina ruwan ki dadin abun ba ke za ki aurar da ni ba balle ki ce baki iya wa ni dai Wlhy in ban ci cake din nan ba da yawu na ya biya yasin sai kin biya ni a ranar gobe kiyama"ta kare tana cin Bomb

"Wlhy Adda Zuhra ina bayan ki ko nima ya biya raina,daga gani yasin ba karamin dadi zai yi ba,Gaskiya Adda Beeha ki sama na kar ki dauki hakkin mu"

"Shatu da ke da Zuhra ban san wanda ya fi wani kwadayi ba,gashi can na san za a yi haka ya sanya na cire muku tun jiya don a qashin wuya za ku tsaya mun in ban baku ba,kwadayayyu kawai"ta kare tana hararan su daidai lokacin wayan ta ya dau kara

Dauka tayi cikin sanyin murya tace "Assalamu Alaikum",shima daga can bankaran yace "Wa alaiki Asslam Habeebty"idanu ta dan zaro hakan ne ya sanya shi cewa "maida idanun mana sai kace wace ta hadiye kunama"

Dan gefen ta ta kalla sanann tace "wa ya ce da kai ina zare idanu?"dan dariya tayi sannan yace "jiki na be taba bani karya ba don haka jiki na ne ya bani,sorry my bad Good morning princess hope kin tashi lafiya?"

Dan zare wayan tayi tare da kallon time sanann tace "1 ake nema and kana cewa Morning?Ga duk kan alamu yanzu ka tashi daga bacci,ni kam na tashi tun Asuba ban koma ba har yanzu"

Cikin muryan tausayawa yace "I'm so sorry Angel ni na jawo miki wanann wahalan ko🥹Gaskiya ban kyauta ba"dan dariya ta sake sannan tace "See you waya ce maka in sha Allah by 3 order din ka zai zamo ready saidai fa bani da wanda zai yi maka delivery"

Da sauri yace "ba ga ni ba I can be your delivery boy in kika so,sai ki siya mun dan keke ko machine ko ma mota kina aika na ko ina ne zan je miki I won't mind"dariya ta dan yi sanann tace "you are so funny Wlhy"

Shima dan dariyan yayi sanann yace "yau baki kira suna na ba fa"ya kare kamar me shirin yin kuka,dan rolling eyes tayi sanann tace "na ki din haka kawai ka na wa mutane wayo ana ce da kai I love you a banza"

Saida ya dan yi dariya sanann yace "Ai ko kin fada yasin and I love you more baby girl yanzu dai text me your address zan turo driver na ya dauka by 3 kika ce you will be done right?"Ya kare yana sauko wa daga kan gado.

"Yeah 3 komai will be ready in sha Allah and yanzu zan ma texting din Address din mu thank you for choosing SABEE'S PASTRIES "ta kare tana murmushi,shima murmushi yayi sanann yace "it's my pleasure after all bari na bar ki haka kar na cika ki da surutu bye bye take care of yourself okay",kai kawai ta daga kamar yana ganin ta sanann tayi ending call din,ganin yanda Zuhra da Shatu suka zuba mata idanu ne ya sanya ta hade rai tare da cewa

"Shi dai munafurci da sa ido ba abun yi bane,Wlhy in yarinya bata bar kallo na ba sai na cire mata Retina ta rasa na gani ranar Auran ta eheee"dariya kawai suka yi ba tare da ce mata komai ba don in suka ce za su tanka ta to masifa za ta cika su da shi.

Nan fa kafin 2:30 sun kammala komai tare da yin packaging din su,inda Sabeeha har dan Cookies tayi different sizes and shapes masu kyau da dadi pieces 20 da kuma alawar madara shima haka,ta sa su a package daban sanann ta sanya cikin kayan nasu,inda tace wa Zuhra tayi musu ne kyauta don yanda ya faranta mata ta ji dadi ita ma ta san za su ji dadin shi.

Kamar yanda yace da ita kuwa 3 dot sai ga driver din FIK a kofar gidan su Sabeeha inda ya kira ya sanar mata ya iso cikin jin dadi,suka kwashi komai tare da taimakon shi aka sanya a mota sanann yayi musu sallama tare da wucewar shi.

Wani irin tsalle Sabeeha ta saka tare da rungume Zuhra da Shatu cike da tsantsan jin dadi,tana me adduar Allah ya sa ya bude kofa ke nan daga yau ta fara receiving manya manyan orders irin haka,nan suka koma suka tarar da Umma tana tattara gurin da aka bata hannu suka sanya mata kafin kace me gida ya dau seti,nan duk suka yi wanka sanann Shatu tace za ta tafi 5k Umma ta dauko tare da mika mata sanann aka kula mata abubuwan da ya yi saura,godiya sosai tayi wa Umma inda Umman ta yi ta sanya mata Albaraka,sanann ta koma gida.

Zuhra kam tare suka yi girkin rana inda shinkafa da Miyar kaza suka yi,saida suka ci suka yi dam sannan suka hau hira,sai yamma liss sanann itama tace za ta koma gida,duk da ba yanda Sabeeha bata yi kan ta kara kwana ba amman taki, 10k Umma ta bata itama tare da kula mata nata sanann Sabeeha ta rako ta bakin titi tana ta godiya don haka ta wuni bata da ko sisi.

Kallon ta Sabeeha tayi sanann tace "Mataar Habeebeey na gode sosai da dawainiya Allah ya saka da Alkhairi ya kuma baki Habeebeey in Alkhairi"

"Ameen thuma Ameen Sabeehatuwa ta Allah ya cika miki burin ki na bude babban Restaurant a cikin garin nan,ya kuma nuna mun randa za ki ce Zuhra nayi saurayi fa"

Dariya Sabeeha ta fashe da shi sanann tace "Ai ke kam Wlhy ko baru nan ya gan ki ya bar ki indai akan soyayya ne Allah ya shirya mun ke,maza ga abun hawa na tare ki shiga Allah ya kiyaye hanya sai mun yi waya"

"Ai ko baki kira ba ni zan kira ki na ji yanda za ku kare da Mr I love you din nan naki,don jiki nan yana bani ba rabuwar ku ke nan ba yau zai kira ki"harara ta maka mata sanann tace "shegen iyayi kamar uwar miji wuce ku tafi kar na finciko ki baki kamar Mr I love you,Mal ka tafi mun da ita a hankali Hilisss kawata take care,I love you okay"hannun Zuhran ta daga mata sanann tace "a huta gajiya Goofy angel dita I love you moree,na gode sosai Allah bar zumunci"daga haka me adaidaita ya ja tare da barin gurin Zuhra na kara jin kaunar Sabeeha a ran ta,domin bata taba ganin mutum me zuciya me kyau irin nata ba,bata da shi amamn kullum burin ta be wuce ta ga ta taimaka tare da cire Zuhran cikin damuwa da kunci ba,ya Sanya aka ce duk wanda ya kasance me hannun bayarwa to baya taba rasa wa Alkwarin Allah ne.

Gida Sabeeha ta koma inda ta wuce daki kai tsaye tare da gabatar da sallan Magrib sanann ta fito ta shiga dakin Umma,saida ta tsamo nama a tukunya sanann ta zauna a hankali ta fara ci ganin Umma bata idar da addua ba.

"Allah ya shirya mun ke Uwa ta yanzu haka za ayi Auran kina tsamen nama a tukunyar miji?Ni kam yaushe ne za ki girma ehyee Auta?"baki ta dan cuno sanann tace "Umma ba ma sai nayi auran ba ma,na ga Ai tukunya ta ne ba na wani gardi ba balle ki ce haka"

Baki Umma ta rike don wani zubin takan ga girman Sabeeha ne amamn hankalin ashe da saura,saida ta gama cinye wa sanann ta goge hannu tare da fadawa jikin Umman, cikin shagwaba tace "Allah kara lafiya da nisan kwana Umman Sabeeha Zuhra tace ace miki ta gode sosai Allah kara budi me Albaraka"kan ta Umma ta shafa sanann tace

"Ameen thuma Ameen sannun ku da aiki Allah yayi muku albarka duka,yau dai da wuri za mu kwanta kin ga tun safe kike tsaye,ya kamata ma ki balla PCM ki sha da pain reliever don ki samu bacci me dadi,in ya so gobe sai ki mika wa Hajiya 10 kudin wuta da ruwan da take ta magana a kai,sai a dan sai sweet a raba wa yaran gidan suma su ci arziki ko?"

Mikewa zaune Sabeeha tayi sannan tace "yasin Umma babu wani sweet din da za a bawa ko wnai yaro ko yarinya su in sun samu na su kudin ko goro suna ba mu ne,ita dai da ya zama dole kudin ruwa da wutan duk da ma cutar mu ake amamn don a zauna lafiya za a bata amman bayan haka Umma sisi babu me ci,kayan chefane zan siyo mana gobe in sha Allah tunda kin ga ma babu school so sai na je da wuri na dawo"Kai kawai Umma ta daga alaman to,don saurin Zuciyar Sabeeha har tsoro yake bata,gudun kar ma Umman ta zaga ta tayi siya musu ya sanya cikin daran suka gama list din abubuwan da za su siya snanan ta karbi kudaden kan gwara ya kwana a gurin ta kawai zai fi.

Saida ta yi alolan bacci sanann ta shigo daki,Azkars ta gama yi sannan ta cire hijab din ta tare da janyo blanket tare da daura kan ta kan pillow sannan a hankali ta lumshe idanu,don ba karamin gajiya bane a jikin ta,don ma ta sha magani a gurin Umma,kai ta girgiza tare da dan yin murmushi sanann a bayyane tace

"Wani abu saidai a bar Zuhra in Banda hauka irin na Goofy angel me zai kara kira yace mun??Ita dai bata da zance da ya wuce soyayya soyayay Allah ya shirya mun Zuhra"daga haka ta sanya kanta Ayya hannun dama sanann ta kuma lumshe idanun ta a hankali bacci ya fara daukan ta,kamar cin mafarki ta fara jiyo vibrating din wayan ta dake kasan pillow,har ga Allah da farko ta dauka cikin bacci ne saida ta ji kiran yaki daina wa ne ya sanya a hankali ta mika hannu tare da janyo wayar ba tare da ta kalli sunan me kira ba ma kawai tayi picking tare da manna wa a kunnan ta,cikin muryan bacci tace "Assalamu Alaikum......"


Kar a manta da Sharing da commenting saboda Allah🥹🥹ayi hakuri da typing errors hilissss ban Riga nayi editing ba.

Ina yi wa kowa fatan Alkhairi.

Weiterlesen

Das wird dir gefallen

627K 9.6K 48
Lost, Lose (Loose Trilogy #1) She's a girl of hope, Lisianthus Yvonne Vezina. A teen-year-old girl who focused on her goal... to strive. But everyth...
180K 4.1K 13
❝ fate. a word meaning destiny. fate. a word meaning doom. ❞ [ a f4 thailand fanfic ] [ thyme paramaa x fem!oc ] [ currently being rewritten ] © 𝐬𝐭...
31.4K 5.2K 15
In the elite ranks of DRDO, Ardik Rajwasnhi, a young prodigy, is fueled by ambition to secure a coveted position among the legendary Team Phoenix. Ho...
24.5K 3.7K 36
مــن نــەم زانـیـبـوو ئـەو پـیـس تـریـن و گـەورەتـریـن مـافـیـای سـەر ئـاسـتـی ئـاسـیـایـە.... "دووبارە ھەوڵی ڕاکردن لەم ماڵە بدەیت ھەڵبژاردن لەنێوان...