WANI GARI

By KhadeejaCandy

10.4K 566 36

A wani gari, da al'ummarsa basa hada jini da mutanen wajen garin, akwai wata yarinya da alkalamin kaddara yay... More

WG-01
WG-02
WG-03
WG-04
00
WG-05
WG_06
07
08
09
11
12
13
14
15

WG-10

401 28 1
By KhadeejaCandy

Namra ta matsa kusa da ita ta karbi wayar ta duba hoton, sai gata suna kallon kallo ita da Nimra, sai a yanzu Namra take tuna ta sha ganinsa a media amman how come ta ganshi a fili bata gane shi ba. Nimra ta yi baya ta zauna saman kujera ba tare da tace komai ba, Namra shiru ta yi gudun kar ta furta abun da zai saka jefa yar'uwarta cikin matsala, domin idan Ummi ko Abiey suka san cewar ta bashi motarta za su yi mata fada sosai.
Ummi da wani abu mai kama da kashi ya tsoki kahon zuciyarta saboda ambatar sunan Ameer da na mahaifinsa da Mahmood yayi ya saka ta kasa zama ta kuma kasa motsawa zuciyar sai ciwo take mata.

“Ummi”

Namra ta kira sunanta ganin yadda ta tsaya kamar hoto, da sauri ta kalli Namra irin kallon kamar bata cikin hayyacinta, wani abu take ji mai kamar kuka kuma ba kukan ba, ba zata iya kiran da damuwa ba, haka kuma ba almara ba ce, wata kila mamaki take na sunan da ya zo daya, wata kila kuma wani bangare na zuciyarta gaskiya yake fada mata cewar Ameer dinta ne. Ko shiyasa Abiey yace a bar magana sun yi solving matsalar da mahaifinsa.? Daker ta iya tara yawun bakinta ta jika makoshinta sannan ta juya ta cira kafarta da take jin kamar ta shekara bata taka ta ba, ta fara tafiya.

“Ummi lafiya”

Mahmood ya tambaya domin hankalinsa yana gurinta, Nimra kam nata hankalin yana can gurin wani tunanin na dabam.

“Na'am”

Ummi ta amsa sannan ta juyo ta kalleshi gaba daya a rikece take irin rikicewar abun da kake tsammani ko tsoron ya faru, irin rikicewar wanda hankalinsa ke daf da gushewa, ba kuka take ba sai dai kana kallon fuskarsa kasan akwai tashin hankali a zuciyarta da fargaba.

“Lafiya”

Ya sake tambaya hakan ya hanyo hankalin Namra gareta, Hajiya Zahra ta kasa cewa komai kallonsa kawai take amman hankalinta da tunaninta suna wata duniyar ta dabam, ba tare da ta sake ce masa komai ba ta juya ta fara takawa suka bita da kallo har ta haye sama ta shige dakinta. Sai ta maida kofa ta rufe ta nufi gadonta ta zauna kwakwalwarta na tuna mata da abubuwan da suka faru a baya, yayin zuciyarta take soyuwa da kuskuren da ta aikata. A hankali Namra ta turo kofar dakin ta shigo rike da jakar Hajiya Zahra da wayarta da ta bari a falo.

“Ummi ga wayarki da jaka”

Wannan karon tana dagowa sai hawaye suka sauko mata, a sanyaye Namra ta ake jakar saman gadon ta zauna kusa da ita.

“Ummi lafiya?”

Sai ta yi saurin share hawayenta.

“Tsoro nake kar..... Kar.... Kar... Yaron ya sake yi ma Maleek wani abu....”

Ta fada ba dan komai ba sai dan ta kawar da tunanin Namra akan hawayenta.

“In shaa Allah ba zai sake ba, ko da ba a hukunta shi ba ai ya tsorata da yadda aka dauki abun da muhimmanci kuma kin ji har mahaifinsa ya kore shi”

Ummi ta juyo wasu hawayen na taruwa a fuskarta ta rike hannun Namra.

“Toh idan ya fada wani halin fa, nuna min hotonshi Namra”

“To koma minene ai shi ya jawa kansa, kuma hukuncin da mahaifinsa yayi zai saka dole ya kiyaye gaba”

Ta fada tana daukar wayar Ummi ta shiga google ta kama hotonsa ta nuna Hajiya Zahra. Hannu biyu Hajiya Zahra ta saka ta karba kamar wanda aka bawa sakada, gabanta na wani irin bugawa da ya wuce kima kanta har sarawa yake, hotuna ne da yawa a zube ko wane da kalar style dinsa, hannunta na rawa ta saka yatsanta ta taba daya sai ya bude a babban hoto, zaune yake akan kujera ya saka kananan kaya wando da riga ya dan karkata fuskarsa kadan ya kalli wani wajen dabam. Kamanin Deen ta gani zube a fuskarsa ciki har da hade rai da haske.

“Da gaske sunansa Ameer? Kuma dan Mr Bashir ne?”

Ta tambaya.

“Ummi gashi ma kina gani a rubuce”

Namra ta amsa mata tana kallonta, sai ta daga kai ta sake girgizawa. Tun tana kallon hoton da kyau har ta koma bata ganin komai sai duhu hannu ta saka ta fara shafa wayar.

“Namra Hoton ya bata, dawo min da shi na sake gani”

“Ummi ai kin jika wayar da hawayenki ba zaki iya gani ba”

Sai a lokacin ta san hawaye ne ya rufe mata ido take ganin duhun. Hannu ta saka ta share amman suka ki tsayawa tana kokarin ganin bata yi kuka a gaban Namra ba amman abun ya ci tura har sai da ta fashe da kuka mai karfi, ta saki wayar hannunta ta saka hannayenta ta rufe fuskarta.

“Subhanallahi Ummi lafiya?”

A take hankalin Namra yayi matukar tashi, sai ta rumgume mahaifiyarta tana rarrashinta, can kuma ta sake ta mike tsaye ta fice daga dakin da sauri, bata dade ba ta dawo dakin tare da mahaifinta Nimra da Mahmood suka shigo daga baya Maleek ya shigo dakin ya tsaya jikin kofa ya rumgume hannayensa, yana kallon Namra dake fadawa Abiey abun da ya faru.

“Ummi ta cika daukar komai da girma, ko karamin abu ne sai ta dauka ta saka a ranta”

Maleek ya fada, duk a tunaninsu saboda abun da ya faru ne take kuka ban da Abiey da ya san dalilin kukanta.

“Ku fita waje bari na yi magana da ita”

Fita suka yi daga dakin cikin damuwa, ko a tsakaninsu wani ya shiga damuwa damuwa suke da Matsalarsa balle kuma uwa kamar Ummi. Sai da suka fice sannan ya zauna kusa da ita ta kalleta da duba na tsanaki  da natsuwa ya ce.

“Wannan kukan duk na minene? Na fada miki an yi solving matsalar nan komai ya wuce, kuma na miki alkawari iri haka ba zai sake faruwa ba”

Sai a lokacin ta samu damar dago kai ta kalleshi da jajayen idanuwanta.

“Abiey ka san yaron nan?”

“Ni ban taba ganinsa ba”

“Amman kasan mahaifinsa?”

“Aa na dai yi magana da step mother dinsa”

Ta hade kuka daker.

“Mahmood.... Mood.... Ya ce dan Mr Bashir ne kuma yan Kano ne”

“Eh haka ne, mun yi magana da ita kuma ta tabbatar mana cewar ba zai sake ba”

Ta kai hannu ta dauki wayarta ta bude ta nuna masa hoton Ameer, karba yayi ya duba.

“Oh shi ne wannan yaron kamar mai natsuwa, Allah ya shirya na fadawa Maleek kar na sake ganinsu tare”

“Ranka ya dade Ameer ne, Ameer..... Ameer...”

“Wane Ameer kuma?”

Gangan yayi mata haka saboda ya kawar mata da tunanin da take.

“Dana Ameer...”

Wani irin deep breath Abiey yayi taking sannan ya ce.

“Kina da wani ďa bayan Maleek da Mahood?”

Hajiya Zahra ta kalleshi da duba na irin wanda yake son yayi wasa da hankalinta ya juya tunaninta.

“Ameer ďana na farko da na fara haihuwa, ďan da na haifa da Deen, ka kalli fuskarsa sunansa da sunan mahaifinsa”

Wani irin kallo Abiey yake mata mai kama da harara zuciyarsa ta hau bugawa da mugun karfi.

“Wata kila ba ki gane ba ne”

“Na gane shi Ameer ne Wallahi, ta ya zan auri ubansa na haife, na kwana da shi a raina na tashi da shi har yau tunanin Ameer be bar raina ba kuma ka fada min cewar ban gane ba, wannan ďana ne Abiey jinina ne, ka daina canja min tunani Abiey mu ba yara ba ne”

Mikewa yayi tsaye ya daka mata tsawa da sai da ta zabura.

“Kin gane shi saboda har yanzu kina rike da shi da ubansa a ranki, na dade da sanin cewar Mr Bashir yana garin nan tare da Iyakinsa sai dai ban san akwai alaka tsakanin ďansa da Maleek ba, da ban bari abun ya kawo haka ba, ni da ke mun dade da rufe babin Deen da duk wani abu da ya shafe shi, ďa dai kin riga kin siyar yana da rayuwarsa da iyayensa a yanzu, yana da dangi da yan'uwa, ba san ki ba be san da labarinki ba, so this should be the last time da zaki sake yin maganar Ameer a gidan nan, kar son zuciya ya saka ki rusa rayuwarsa da ta wanda kika bawa, karki ruguza farincikin Mr Bashir da shi kanshi Ameer din, and mafi muhimmanci yarana ba su san da wannan maganar ba, ba su san ma kin taba auren wani kamin ni ba, karki kawo mana wani bakon al'amari a gida, na fi son yayana fiye da kowa karki tashi hankalin yayana...!”

Yana kaiwa nan ya kabe rigarsa ya fice daga dakin a fusace har yana sakin kofar da karfi.  Kalaman da yayi mata a yanzu sun kara tabbatar mata da cewar Ameer din ta ne, sai dai ya shata mata layin da bata isa ta tsallaka ba, kamar yadda ta yi ma kanta kataga tsakaninta da shi da bata isa ta rusata a yanzu ba. Ba tayi mamakin kalaman mijinta ba domin ta san ba shi da makiyi kamar Deen, hakan ya saka a duk lokacin da ta nuna damuwa akan Ameer sai ransa ya bace ya ce saboda yana ďan Deen ne, a kullum ikirarinsa bata son Maleek saboda jininsa ne sai Ameer da yake ďan makiyinsa.

‘Gaskiya ne, Ameer ba ďana ba ne a yanzu, ďan wasu ne, yana da family da iyaye yana da rayuwarsa ta dabam’

Da zuciyarta take magana tana kokarin ganin ta kawar da tunaninsa a ranta ta cire shi daga zuciyarta, ko ba komai yanzu dai ta san yana a guri mai kyau kamar yadda take buri, ta san Mr Bashir ya ba shi gata da kulawa kamar yadda yayi mata alkawari tun da har ya hana police su kama shi saboda abun da ya aikatawa ďanta Maleek, ya girma a yanzu ya zama babban Saurayi rayuwar baya ba ita ce a yanzu ba, ya kamata ta manta da komai. Hakan ya saka ta tashi ta shiga bandaki ta wanke fuskarta ta fito ta zauna bakin gadonta dafe da zuciyarta, har yanzu bata daina jin wannan mashin da ya tsoki kahon zuciyarta ba, a yanzu kam ta yarda ta rasa Ameer har a bada, sai dai idan ta tuna bata bashi kulawa yadda ya kamata ba, sai ta ji wani iri a ranta, ga cutarwa da ta yi ma iyayen Deen na raba su da ďan Deen tilo da zai iya zame musu sanyin ido.

“Hakki ba zai bar ni ba, na cutar da yaron nan na cutar da kananinsa na cutar da kaina, miyasa ban yarda na karbi hukunci tun a wacan lokacin ba?”

Ta fashe da kuka sosai tana tsananin nadamar abun da ta aikata, ina ma ace da halin gyara da ta gyara komai a yanzu, yanzu ta kara tabbatar da hakkin ne yake bibiyarta shiyasa Maleek baya kaunar matsowa kusa da ita, kuma baya son ko muryar mata ya ji, ita kuma ta kasa manta abun da ta aikata hakan ya hana ta farinciki. Mikewa ta yi tsaye ta dauki wayarta ta yi clearly din searching din da Namra ta yi mata na Ameer, a kokarin na engaged din kanta da wani abu ya saka ya canja tufafin jikinta zuwa wasu marar nauyi ta sauko falo, Mahmood kawai ta samu zaune yana lasa wayarsa, dagowa yayi yana kallonta har lokacin idonta be cire kumburi ba.

“Abiey yace mana Bachi kike”

“Yanzu na farka”

Ta fada tana kokarin ta yi murmushi amman ta kasa, haka ta wuce Kitchen suna da masu aiki, sai dai ta sabawa kanta ita take girkawa mijinta abun da zai ci da kanta, hakan ya saka ta fara shirye shiryen girka masa abin da ya fi kauna saboda ta san ransa ya bace, sai dai me tana kai hannu ta bude fridge sai ta fashe da kuka.

AMEER POV.

Be isa Katsina ba sai 11pm na dare sai da ya fara tsara dajikan garin ya fara tunanin me ma zai kawo shi garin? Miyasa ya zo nan?

“To ina zan je idan ba nan ba?”

Ta tambayi kansa domin ya san barin kasar a yanzu ba abu ne mai sauki a gare shi ba, idan ma ya bar kasar duk inda zai je zai samu kansa cikin bacin rai ne da damuwa. Ya cika bakinsa da iska ya busar tare da kai hannu ya dauki wayar Nimra da sakonta na uku ya shigo domin jin lafiyarsa tsoron kiransa take kar ransa ya kara baci wata kila be huce ba har yanzu.
Kai tsaye ya aika mata da kira ringing daya ta daga kamar daman can jiran kiransa ake, sai dai yayi mamakin jin wata muryar wacce ta girmi ta Nimra ta daga wayar tare da sallama, da gangan yaki amsa sallamar domin ya san ba Nimra ba ce, kuma shi tun da ba wanda yake son waya da ita ce ta daga ba be ga amfanin yin magana ba, sai kawai ya kashe wayar. After like 3 minutes Nimra ta kira shi sai ya daga ya saka ta a speaker.

“Ka kira na je na daukowa Ummi abu, ka isa Lafiya?”

Yayi shiru kamar ba zai amsa mata ba.

“Ina na je?”

“Ban sani ba, amman ina fatar kana wani guri mai aminci”

Ya faka motar gefen titi ya sauke gilashin Motar yana kallon titi.

“Ina KT in the middle of the road i think”

Nimra dake zaune a dakinta ta mike tsaye cike da damuwa.

“I know be kamata ma saka kaina a cikin matsalarka ba, Amman da zaka yi hakuri ka dawo gida ina tunanin zai fi domin a yanzu zaka jefa kanka a cikin wata matsalar ne kawai kuma..”

Sai kuma ta yi shiru..

“Mahaifinka yana bukatar ka Ameer”

Ya juyo ya kalli wayar kamar ance masa ita ce a gabansa.

“How do you know my father? Taya kika san shi?”

“Abiey mu yayi magana da step mother dinka”

“Ke ki fito fili ki yi min magana yadda zan fahimta, what do you know about me?”

Bata son ta fada masa cewar ita din kanwar abokin hamayyarsa ne duk kuwa da ta san dole zai sani, sai dai tana ganin kamar be dace ta yi hakan a yanzu ba.

“I'm talking to you”

Ya daka mata tsawa kamar tana gabansa, a dole ta fada masa abun da ya faru da yadda aka yi ta gane cewar shi din ne ciki har da hotonsa da Mahmood ya nuna musu.

“Wow... So Maleek duk shi yayi planning wannan? Shiyasa kike ba ni shawarar yadda zan yi masa? Shi yake fada miki ko?”

Ta girgiza kai da sauri.

“No no no  Wallahi ba shi yayi ba, ba shi ya saka ni ba, taya zan baka shawarar yadda zaka yi masa haka? Wallahi ban san akwai alaka tsakaninku ba sai dazun ka yarda da ni Ameer”

“Idan na yarda dake duniyarki zata gyaru ne? I don't trust you karki sake kirana, and mark my words ke ma sai na koya miki darasi kamar yadda zan koyawa ďan'uwanki”

Rasa ta yi ta inda zata kamo zaren balle har ta fara sakar yadda za 'ayi ya yarda da ita.

“Mahaifinka yana bukatarka Ameer He's Unconscious, Step Mother dinka tace be ma san an kai shi Asibiti ba”

Yanke watar yayi ya bude motar ya fito yana jin wani bakinciki na karuwa a ransa, Ameer wani irin murdaden mutum ne da bashi da fahimta cikin sauki, abu kadan ya bata masa rai. Ji yake gaba daya Maleek ya gama da shi.

_Da gaske mahaifinka na asibiti Ameer ba karya nake maka ba, kuma ka yarda da ni ban yi komai saboda na bata maka ba, dan'uwana ma be san muna da alaka ba_

Ta aiko masa da sako, yana gama karanta sakon ya koma cikin motar ya danna a wata hanyar da ke gefen inda ya faka motar, daman can be san tsoro ba tun yana karami baya shakkar kows bata shakkar komai, musamman idan ransa ya bace babu abun da ba zai iya aikata ba, Ameer irin mutanen nan ne da idan ran su ya bace hankalinsu ke gushewa su aikata komai sai dai daga baya ayi nadama, tun yana karami haka ya tashi ko mutuwa aka aje sai ya taba ta sai dai ya mutu, idan kuma aka ce idan yaje can zai mutu ko wani abun ya same shi to sai yaje sai dai komai zai faru ya faru.
Ba ma kamar yau da yake jin kamar ya kashe kansa, miyasa ya yarda da yarinyar da be sani ba, why ya kulla alaka da kanwar makiyinsa? Duk wannan plan din Maleek ne haka zuciyarsa ke raya masa, be taba sani shi din wawa ba ne dai yau. Gudu yake sosai cikin jar kasar da babu titi sai kura da turda dake tashi saboda gudun da yake komai ya ci karo da shi bugewa yake babu ruwansa da bata motar da zai yi ko kuma ya jiwa wani ciwo, yo a gari ma Ameer ai gudu yake da mota yana kade mutane balle kuma a wannan dajin na Allah da babu kowa a hanyar. Karshe gudu ya kai motar har sai da ya kai karshen hanyar sai ya tsara ta inda ransa yayi masa dadi domin ba hanya da ke bullewa cikin gari ba, da gangan yayi ta buga motar a jikin wasu manyan duwatsu da ya samu daker da wahala motar ta karaso gurin, sai da ya tabbatar ya lalata gaban motar sannan ya bude ya fito ya jefar da wayar a cikin daji. He rather die here da ya sake amfani da wani abun da ya shafi Maleek.

Hudun yayi masa yawa domin ya lalata na Motar kuma ya jefar da wayar a inda be saka ran ganinta ko da ya duba, tsaye a gurin yana kara jin tsanar Maleek a ransa musamman idan ya tuna shi yana can kwance a guri mai kyau tare da iyayensa shi kuma ya hada shi da nasa iyayen kuma ya bashi da inda ya fi jindadin kwanciya. Ya dade yana tunanin yadda zai yi ya rama abun da Maleek yayi masa kamin ya bude motar ya dauko Carpet dinsa da ya siya ya saka hannu aljihu ya ciro ATM din Nimra ya karya shi, ya cire kudin data bashi ya saka a motar ya rufe motar. Da taimakon farin wata dake haska dajin mai kama da tarkon mutuwa ya karasa gurin fakon dake gabansa mai kamar an share ya shinfida ya kwanta a gurin ba Aljannu ba ko Uban gidan aljannu ne a gurin sai ya kwanta ko ma kashe shi suka yi shi daman mutuwar yake nema, yadda ka san wani dan shaye shaye haka yake zama idan ransa ya bace.
  Kasa bachi yayi hakan ya saka shi tashi ya zaune idan ya gaji da zaman yayi tsaye, ba bacin ran abun da Maleek yayi masa ne kadai damuwarsa a yanzu ba, har da ta mahaifinsa da aka fada masa baya cikin hayyacinsa, sai dai duk da hakan Maleek yake dorawa laifin. Sai da sanyin  Asuba ya fara sauka sannan ya fara jin bachi na son daukarsa daukar Carpet din yayi ya nufi wata hanyar da be san inda ta nufa ya fara tafiya kamar ana kiransa. 
Gaban manyan duwatsu sai ya tsaya nesa da su kadan ya shimfida Carpet din ya kwanta, wata kila ya fi jin natsuwa a nan fiye da inda ya zauna a dazun, rairai ya kwanta ya yayi matashin kai da hannayensa ya hade kafafuwansa guri daya yana kallon sama ya runtse idonsa, sai dai babu abun da yake gani sai mahaifinsa ko ba komai ya san shi kadai ya rage masa tun da mahaifiyarsa ta rasu tun yana jariri kamar yadda Daddynsa ya fada masa, idan kuma ya rasa Daddy ya rasa komai kenan.

‘Wait... Da gaske take ma ko kuma wani sabon plan din ne?’

Da wannan tunanin bachi yayi gaba da shi.



WAIRA POV.

Gudu take sosai ba dan ta san inda zata je ba, sai dan ta tsira da rayuwarta domin ta san tabbasa za a biyo sawunta ko da kowa be biyo ba Eid zai yi kokarin yin haka, a zuwa yanzu ta san laifinta ya karu a gurin Sarki hukunci da za a mata wata kila sai yafi na mutuwa kai tsaye, a tunaninta sai an azabtar da ita sannan a kashe ta ranta kila na wulakanci.
  Tana jin ta taka abu amman bata damu ta tsaya ta duba kafarta ba, tana jin zafi sosai amman tsoro ya hana ta tsaya ta yi tafiyar tsanaki balle har ta duba abun da ta taka a kafarta, tana kokarin tsallaka wasu duwatsu bata ankara ba wani dutsen ya tadeta ta fadi bakinta ya bugu da dutsin dake gabanta a take jini ya balle, a rikice ta tashi zaune tana kuka ta koma bayan duwatsun ta boya ta rumgume hannayenta tana tausayawa kanta, domin bata san inda zata je ba kuma ba zata iya komawa garin da suka shar'anta mata doka ta karya ba. Sosai ta lafe jikin duwatsun ta yi zamanta a gurin da baka jin motsin komai sai ruwa dake gudana babu komai a gurin sai ciyayi, duk yunwa da kishin ruwan da ta ji bata yarda ta fito daga gurin ba ganin take idan ta fito za a iya ganinta, tsoro da rikicewar da ta yi ya saka ta manta cewar suna da tsananin tsafin da za su gani ko sanin inda take, a gurin ta wuni har dare yunwa ta hana ta bachi sai da dare ya raba sosai sannan ta samu yin bachi shi ma daker domin yunwa take ji sosai, saboda bata saba zama da yunwa ba, idan ma bata da abun da zata ci a gida taje take zuwa ta hau itacece ta ci yayan itatuwa sai ta koshi sannan ta dawo wani lokacin har sai ta yi guzuri...

Continue Reading

You'll Also Like

Saved By Madison:)

General Fiction

835K 16.5K 33
Isabella Rose Romano A 13 year old to which love is something very unfamiliar to her. Having grown up in the foster system, it didn't come very often...
246K 37.7K 109
Maran and Maya, two independent individuals hate each other out of their family background but destiny has some other plans by bringing them together...
110K 2K 17
System bl အပြာ လိုးစာ MC တစ်ယောက် ကမ္ဘာ တွေပြောင်းပြီး သူ့ကိုမုန်းတဲ့သူတွေကို ဘယ်လိုခြွေပစ် မလဲဆို ဖတ်ရမှာပါ။ ‼️မှတ်ချက်။ ဤစာသည် boy အချင်းချင်း ကာမဆ...
180K 6.6K 82
Not many people understood 12 year old Jessica, as a person and an individual. That doesn't include, however, her older sister, who Jessica adores w...