WANI GARI

Da KhadeejaCandy

10.4K 566 36

A wani gari, da al'ummarsa basa hada jini da mutanen wajen garin, akwai wata yarinya da alkalamin kaddara yay... Altro

WG-01
WG-02
WG-03
WG-04
00
WG-05
WG_06
07
09
WG-10
11
12
13
14
15

08

444 25 2
Da KhadeejaCandy

Fitowa yayi bakin gate din gidansu, ya mike hanyar fita daga road din, ko sau daya be juyo ya kalli gidansu ba, not just gidansu even mahaifinsa ya fice masa a rai a yanzu tufafin dake jikinsa ma ji yake kamar ya cire su ya jefar saboda ya same su ne silar mahaifinsa da ya gama yi masa gori ya kwace komai nasa a yanzu.
Ya daukarwa kansa alkawari ko ba zai taba amfani da Atm dinsa ko mota da duk wani abin da ya san ta hanyar mahaifinsa ya same shi ba. Bacin ransa ya ninku akan Maleek zuciyarsa na raya masa komai akan Maleek akai masa, bayan shiga tsakaninsa da friends dinsa yanzu kuma ya shiga tsakaninsa da mahaifinsa.

“Sai na kashe yaron nan”

Ya furta yana jin kamar ace yana gabansa ya saka bindiga ya halshe kansa. Be taba jin tsanar Maleek irin wannan time din ba, duk wani abun dake shiga tsakaninsu be taba kaiwa kololuwa har haka ba sai tsakanin kwanakin nan ba ma kamar yau, da gangan ya daga tsaddadiyar wayar hannunsa kirar Samsung ya buga a kasa ya bita da kafarsa ta ya taka ya rika gurza ta akan titi ba domin komai ba sai dan ya siyata silar mahaifinsa, yana ayyana cewar sai mahaifinsa ya neme shi tun da har ya wulakanta shi har haka, he can't remember when last yayi tafiyar kafa mai nisa irin wannan har ya kai karshen road din be samu abun hawa ba, gashi ya fasa wayar balle ya kira wani daga cikin abokansa su zo su dauke shi duk da yana kallon haka a matsayin wani abun kunya. Unguwace da karamar mota ma abu ne mai wahala ka gani balle kuma napep ko taxi, shi kanshi ya san ya dauko ruwan dafa kanshi, domin tafiya ce zai ci cibi cibi, gashi be san inda zai je ba, garin zai bari? Ko kasar? Ko kuma wani hotel zai kama ya zauna domin vaya son rabar duk wani abu da mahaifinsa ya mallaka balle ya tafi daya daga cikin gidajen mahaifinsa, ko nasa ko ma kamfaninsa, kuma baya son kusantar yan'uwan mahaifinsa gudun kar a kira mahaifinsa a bashi hakuri.

“Hajiya Jamila...”

Ya furta a ransa, he's father Ex-wife, tana matukar nuna masa kauna a duk lokacin da ya rabe ta ko kuma ita ta rabe shi, wannan ya saka duk girman kansa idan yaje Kano sai yaje inda take, kamar yadda take yawan shigowa Abuja ta duba shi.... Sai dai zuciyarsa na raya masa idan yaje can din ma zata iya kiran mahaifinsa ta yi masa magana ko da ya hana ta, shi a yanzu yana son ya tafi inda be san kowa ba kowa be san shi ba, sai dai ya zai yi ya tafi? Ba tare da ya taba kudin da ya same su ta hanyar mahaifinsa ba? Shi ne abun da ya fi tsaya masa a rai, domin tufafin jikinsa ma ya matsu ya cire su balle kuma har ya sake taba wani abun.

Idonsa na akan titi da gidaje amman hankalinsa da tunaninsa ya tafi wata duniyar, sam be ga motar da ta tsaya a gabansa daman hausawa sun ce hankali ke gani ba ido ba, har Nimra ta kusa karaso kusa da shi jikinsa be bashi akwai mai kallonsa, sai dai kamshin turarenta ya dawo da shi daga duniyar da ya tafi ba dan ya tantance mai kalar kamshi ba sai dan turare ya zama wani bangare na rayuwarsa domin shi ne weak point dinsa no matter what happen.

“Hi Buddy”

Ya kalleta with Angry face kamar ita din ce ta yi masa laifi, a take murmushin daya fadada fuskarta ya bace bat kamar walkiya, cike da nuna damuwa ta lake fuskarsa, gushewar murmushinta ya saka shi jin wani iri domin ta zo gurinsa da farincikinta da gwarin guiwa, this is the first time da yaji yana damuwa akan abun da be takama ya damu da shi ba, kuma yana sakewa da abun da be hadade da haduwa da shi ba.

“Miya faru?”

Ya dan sake fuska sai dai ya kasa boye fushinsa, kuma ya kasa kallonta da idonsa dake bayyana bacin ransa karara.

“Alot”

“Zamu iya yin magana akansu?”

Tunani ya tsaya yi, sai ya ji ba zai iya yi mata garda ma ba, ji yake kamar ya dade tare da ita, kamar wata close friend dinsa haka yake jinta.

“Wait ina motarka ya kake tafiya kasa”

“Na bawa Daddy duk wani abu da na mallaka na shi”

Ta saki baki tana masa kallon mamaki.

“Da gani akwai babbar matsala, ina tare da sister if you won't mind ina son ka shiga motar mu tafi gida zai mu yi maganar”

For the first time ya daga ido yayi mata kallo mai kyau, kallon da kawai yayi mata ta fahimci ba zai yarda ya bita gidansu ba, ba ma lallai ne ya shiga motar ba. But bata da yadda zata yi domin tana jin ta damu da shi da rayuwarsa kamar wani wanda ta saba da shi, yanayin yadda kaddara take ta kara hada su ma wani abun ne da ba tsarinta su ba.

“Alfarma zaka min ka shiga motar nan, na san ba ajinka ba ne, kuma ka fi karfin haka but please do this for me”

“Ni zan yi driving...”

Ya fada kai tsaye daman ba shi da wani hope bayan wannan ba shi da wata mafita ko dabara a yanzu sai wannan.

“Fine”

Ta fada tana murmushi tare da daga hannayenta sama, sannan ta daga masa yatsanta daya sama.

“One minute”

Ta nufi da wani irin zumudin da ita ma kanta bata san na minene ba, murna take Ameer zai shiga motarta sai kace wani celebrity. Driver side ta tsaya ta yi knocking Namra ta sauke gilashin, yadda take watsa mata wani kallo sai ka rantse da Allah bata san inda yar'uwarsa Nimra ta fito ba, ba kuma ta yi da gangan ba ne, sai dan ya zama mata hali, ta nan suka banbanta da yar'uwarta, domin Nimra irin yan matan nan da babu ruwansu da girman kai ko nuna isa balle wulakanta wani, tsabanin Namra da take ji da kanta kamar ita kadai ce yar mai kudi a garin Abuja.

“Sauko ki koma baya”

“Ban gane ba”

“Na ce ki sauko ki koma back seat”

“Fine daman ba son driving nake ba, amman zan cen na zauna baya ba zan zauna ba, zan dai zauna a front seat”

“Idan ba zaki zauna a baya ba, then get out of my car, ni zan zauna a front seat”

“And who's going to drive?”

“Him”

Nimra ta nuna Ameer da ya kasaro gurin cike da izza yana zuba hannayensa aljihu.

“We just drop Mom tun a can nake ba fada miki ba hanyar nan ya kamata mu biyo ba, ashe kin san da wanda zaki hadu shiyasa kika yi haka, and now kina fada min na zauna a baya or na baki motarki”

“Yes that's the rules”

Ameer ya kalleta ya kalli Namra da kamar su ta yi yayawa ya sake duban Nimra.

“Are you guys twins?”

“No we're triplets”

Namra ta amsa tana bude motar ta sauko tare watsa masa harara. Ameer ya kalleta yana murmushin gefen baki daman ya kware a babin bakar magana.

“And you're the ugliest one”

Har kasan zuciyarta ta ji zafin maganarsa, hakan ya saka ba ta yi attempting sake fada masa wata maganar ba.

“Da kin shiga na sauke ki gida”

“Ba zan shiga ba my friend will come and pick me up, and this is the last time da zan shiga motarki”

Namra ta amsawa Nimra a fusace, Nimra ta daga mafadunsa tana rufewa Ameer kofar.

“What ever... ”

Wannan karo na biyu da Nimra ta kara burge shi, domin yana son ya ga an nunuwa mutane shi din wani na mai muhimmanci, a wulakanta wani saboda shi abu ne da ke matukar faranta masa rai. Da karfi ya fisgi motar bayan Nimra ya rufe front door din.

“Da gaske ku twins ne”

“As you can see, ita ce Namra ni kuma Nimra, kuma kama sosai sai dai mun banbanta a hallaya”

Be sake ce mata komai ba, tukin kawai yake ba tare da ya san inda zai je ba. Shiru abun da ya shiga tsakaninsu har ya samu wani gurin can kusa da Galadimawa ya faka motarsa, the place is so quiet nesa da mutane ne sai ka yi ta bawa idanuwanka abinci, ba tare da ya kashe motar ba ya bude ya fito ya jingina jikin motar ya rumgume hannayensa yana kallon wasu gidajen dake gefensu. Ganin hakan ya saka Nimra ma ta bude motar ta fito ta zagayo gafensa ta tsaya juyowa yayi ya kalleta sai ta ji wani irin faduwar gaba da bata taba jin irinsa ba, ba faduwar gaba irin mai tsoro ko fargaba ba, ba faduwar gaba ka kyaun da ta gani a fuskarsa ba, ba kuma ba damuwar dake bayyane a idonsa ba, faduwar gaba ne da ita ma kanta bata san dalilin hakan ba, kuma hakan be taba samuwarta ba sai a yau, wata kila kwarjini yayi mata, wata kila wani abun ne zai faru duk kuwa da kasancewar jikinta be raya mata haka ba, domin ba faduwar gaba ne irin wanda ake neman tsari da shi ba, wani irin faduwar gaba ne mai kama da na dadin da bata san na minene ba. Can cikin wani yanayi mai kama da tunani ta jiyo sautin muryarsa.

“Karki tambaye mi yasa na yi fada da Daddy, don't ask me anything i feel like ba zan iya miki karya ba, kuma i don't want to talk about it now, i just want to go somewhere nesa da nan”

A take ta ji babu dadi, domin tana kokarin juye damuwarsa ta zama nata ne.

“Why”

“Just wani gurin nake son zuwa inda ban san kowa ba, kowa kuma be san ni ba”

“Zaka iya zuwa gidanmu, Ummi bata da matsala yanzu muka sauketa da tare zaka gan mu ma har ka gaisa da ita, Abiey din mu ma haka we're like family to you”

“No Abujar bake son bari gaba daya”

“Ka rika hakuri, karka yi saurin yanke hukunci a cikin fushi idan ma baka son gidanmu zan sama maka wani wajen da zaka zauna”

“Ina da hakuri sosai, da ace ba ni ne Daddy yayi ma haka ba, da yanzu wani labarin ake dabam ba wannan ba, amman ni na san ina da hakuri sosai shiyasa nake son na yi nisa da nan”

Shiru ta yi tana tunanin kalaman da zata hada ta gamsar da shi ya janye kudinrinsa na fasa tafiya.

“Miye wannan”

Ya tambaya tana kallon Box din dake hannunsa. Ya kalli Box din ya fara shafawa da dayan hannunsa.

“Sarewace a ciki wanda nake busa”

Kusan a tare suka kalli wayar hannunta da ta yi kara.

“Ummi ce”

Ta fada sannan ta matsa nesa da shi ta yi picking call din, binta yayi da ido kamin ya dauke ya mai da gurin wata honda da ta faka nesa da su kadan, wata yarinya ce ta fito cikin motar sakale da jakarta ta goyo irin ta teddy da yan mata suke yayi wacce ake saka littafai a ciki. Kallonta ya sake yi da kyau fuskar yarinyar da ta tare shi a office tana rokon ya bata dama ta yi koyi aiki a ma'aikatarsu na dan lokaci ya gani shimfide a fuskarta, idonsa baya masa karya dan haka ya tabbatar da ita din ce. Ita ma kallonsa ta yi cike da fahimtar shi ne mutumen da ya fada mata ba su bukatar irinta a gurin, ta dauke idonta daga barin kallonsa a lokacin da Nimra ta dawo daga wayar da take ta kalli yarinyar ganin idon Ameer yana kanta ita kuma kallonsa take.

“Kasan ta ne?”

Sai a lokacin ya sauke idonsa sai dai be ce amsa mata da eh ko aa ba.

“Kun yi kama kamar yar'uwarka”

‘God forbid’

Ya fada a ransa a fili kuma yawu ya tofar ya yamutsa fuska alamar maganar bata masa dadi ba. Hakan ya saka Nimra jin babu dadi domin ko be fada mata ba ta san ransa ya bace ita kuma a dan lokacin idan akwai abun da ya tsana to bacin ransa ne.

“Ya kamata ka sauke ni gida, Ummi ta kira tana nemana”

Be ce mata komai ba, ya bude motar ya shiga sai ta zagaya ita ma ta shiga, har suka koma cikin birnin Abuja be kalli inda take ba balle ya furta wani abu, sai dai ita ta kan kalleshi lokaci zuwa lokaci.

“Ina zan sauke ki?”

“Kofar gidan mu”

Ta fada cike da fatar idan suka isa ya yarda ya shiga gidan domin bata son tafiyar da zai yi, kamar yadda bata isa ta hana shi aiwatar da kudinsa ba.

“Duba nake yi da zan san gidanku ba tare da kin fada min ba”

“Wuse zone 2”

Yanayin yadda ta yi magana ya saka ya juyo ya kalleta sai ya ga shi take kallo, cike da takama ya kawar da idonsa ya cigaba da tukin, tana fada masa inda zai bi har suka isa gaban wani farin Gate, da shi kan shi ya san masu gidan sun amsa sunan su na masu arziki. Pen ta dauka a motar ta zari tissue ta rubuta masa number ta, ta aje a gurin da jakarta take aje.

“Ka kira ni please, karka bar ni da tunanin halin da kake ciki”

“Na fasa wayar”

Na fada ba tare da ya kalleta ba, kallonsa take da mamaki tana tunanin wane kalar zuciya ne a jikinsa da baya iya controlling dinta, sannan ta maida idonta a gurin jakarta ta bude ta dauko ATM dinta ta aje a saman tissue din da ta yi rubutu akai.

“Maybe zaka bukaci yin wani abu, akwai enough kudi a ciki, kuma zan sake saka wasu a account din just for you”

Ya mika masa dayan wayar dake aje a cikin motar.

“Akwai Sim a ciki, zaka iya kira da ita take care of yourself”

Kallon wayar kawai yayi isa da takama ta hana shi mika kallo ya karba, ko ba komai dai wayar ta masa karama domin baya rika kananan wayoyi, iPhone 14 ce while wayar dake dayan hannunta is iPhone 14pro max duka wayoyin yana jin ba ajinsa ba ne, ko ba komai shi baya son abun da kowa zai rika yayi, ya fi son nasa ya zama dabam ace kalilan ke da abun hakan kan banbanta da sauran mutane.

“1742 is my ATM Password, wayar kuma ba password”

Ganin ba zai karba ba ya saka ta aje wayar a muhalinta dake cikin motar, ta sake bude jakarta ta dauko dollars ta aje a gurin.

“Ko da bukatar cash ta kama ka”

Ta bude motar zata fita.

“Miyasa kike min duk wannan?”

“Because I care for you, i don't want why i don't how, kawai ina jin na damu da kai, don't hurt yourself please”

Wannan karon ta yi sa'a ya daga mata kai, sannan ta sake dubansa ta fice daga motar ta rufe masa kofar, tsaye ta yi har sai da ta daina hango shi sannan ta shigo cikin gidan da masu gadi suka dade da bude mata gate.


WAIRA POV.

Har cikin dakinta Eid ya kawota, a nan wani babin nishadi ya sake bude sabon shafi, sai dai wannan karon hira yake mata irin na wanda ya saba mata lokaci zuwa lokaci, na wasu mutanen da suka banbanta da su ta bangaren abinci, al'ada da kuma addini da ma rayuwar kacokam.

“Ai akwai zafi sosai”

Ta fada a lokacin da yake mata bayanin yadda matansu suke rufe jiki, domin ita duka tufafinta guntaye ne, rigar da zata iya kiranta da doguwar riga bata rufe mata kafafuwa ba, da kadan ta wuce quiwarta, wani lokacin kuma zata saka riga da skirt na fata ko na saki irin na mutane da da ake yi da kaďa rigar iya cibiya skirt din iya guiwa ko ya wuce kadan, ba al'adarta bace saka talkami komai zafin rana da ake, komau hadarin guri haka take shiga da kafafuwanta babu ruwanta da saka talkami balle kuma wanke kafar.
Ta mika hannu beran dake lalen kwanon da take cin abinci ya hau hannunta ta saka shi a tsakankanin kafafuwanta tana shafa shi.

“Akwai wanda na san idan ya shigo dakin nan sai ya mutu ko ya suma saboda tsananin tsabtarsa”

Ta juya ta kalli dakinta da yake ya mutse, ita kam sam bata ga wani abun kyama ko Allah wadai a dakin ba, ita dai yadda take rayuwarta a haka tana jin dadin rayuwarta sosai.

“At takfr hur verrr gulta jaget”

_Yayi tsabtarka?_

“Ya fi ni sau dubu”

Ya fada yana kallonta, sai ta ya mutsa fuska domin Eid ma ganinsa take mai tsananin tsabta da idan zai ci abu sai ya wanke ga wanka a kullum idan kuma aka ce akwai wanda ya fi shi ai abun be burge ba.

“Bana son irin wadanan mutanen sam, amman fatar jikinsa ba irin wannan bace ko? Saboda tsabta”

Yayi murmushi mai sauti, ya kama hannunta ya dora saman goshinsa ya yana kallon kyakkyawar fuskarta dake dauke da datti, so yake kawai ta ga yadda suka yi rayuwa da mutumen na dan lokaci kadan domin ya san tana da wannan tsafin da idan ta dafa kan mutum tana iya ganin da jin abun da ya faru a rayuwarsa ta baya. Runtse ido ta yi sai ta fara arba da karar wani abu mai da bata taba jin irinsa ba, karar ta girmin kunnuwanta, hayaniyar da take ji ta yi yawa, dishe dishe ta fara ganin wani abu bata taba gani ba yana gudu wasu kalar na binsa a baya karar karfe da karfe suna gaduwa kamar za su tashi kwakwalwarta, da sauri ta dauke hannunta ta bude ido domin karar da take ji ta girmi kunnuwanta.

“Kara sosai”

“Abun da nake baki labari kenan Mota, ita suke hawa a madadin dabobin mu”

“Outar.... ota...”

Ta maimaita tana mamakin wace irin rayuwa ce wannan. A gurinta ya wuni har dare sannan ya kunna mata wutar tsafi ta haska mata dakin na adadin awawanin da zai yi kamin ya kwanta a daidai lokacin da wutar zata mutu.

Continua a leggere

Ti piacerĂ  anche

Cecilia Da Anastasia

Narrativa generale

32.3K 756 27
Cecilia's father, a well-known and successful lawyer, was tired of her problems. Tired of the issues she had been causing for the family and it's nam...
316K 23K 28
Avantika Aadish Rajawat Aadi, with his fiery nature, adds intensity and excitement to their relationship, igniting a spark in Avni. Avni, like the ca...
92.6K 3.4K 33
Salvatore Smith meets a woman with whom he shared few nights after loosing his wife. It was 12 years ago, she was way younger than him, from a diffe...
624K 20.7K 169
The young lady from the Xue family was talented and beautiful, and married the dream husband at the age of 16. They had a loving and harmonious relat...