UNAISA

By Shatuuu095

3.1K 443 33

A yanzun maza da yawa suna shunning daga responsibilities dinsu, kamar yadda mahaifina ya auri mahaifiyata ya... More

A
C
D
E
F
G
H
I
J
TSINTUWA

B

261 42 1
By Shatuuu095

🧕 UNAISA 🧕

*B*

✍️ Ayshatuuu

Mijin Anty Aisha yazo, aka Kuma sanar da Governor se gasu an aiko daga fadar shi, aka dauki gawar da taimakon masu zaman jinya harda staff din da securities, sannan aka rike hannuna muka fita, na jingina kaina da headboard din kujera motar Ina jin wani irin abu na bin jikina, I was scared, I was hoping ya tashi yace min April fool! Wasa yake Babu abinda ya sameshi, how I wish a movies ne ace ya shiga cardiac arrest ne! But wannan da gaske ne na rasa shi, shi din ya mutu. Wayar shi Dake hannuna ta fara Kara se Naga " Daughter" nasan Aseey ce hakan yasa na dauka na Kara a kunnena, cikin kuka take fadin

" Unaisa a wani asibitin kuke zamu taho?"

Hawaye ya cigaba da gangaro min nace cikin dashewar murya Dan ta riga da ta Jima da dashewar saboda kuka nace

" Ya rasu!!"

Seda tayi shiru na kusan mintina daya, either she's in shock ko Kuma kokarin digesting abinda na fada take, se kuwa ta saki kuka tana fadin

" That can't be Unaisa! Ki duba carotid artery din shi. He can't die just like that"

Allah sarki ita ta fini sakin layi, Jin bance komai ba se ta Kara sautin kukan Wanda ya Kara dagula min lissafi na jiyo ta tana fadin

" Mamaaa wallahi Abiey ya rasu! Unaisa tace ya rasu. Innanlillahi wa inna ilaihil rajiun!!"

Na kashe wayar Ina Kara sakin kukan rashin sanin halin da nake ciki, rashin sanin madafa. Kafin wani lokaci Kira ya dinga shigowa Amma bazan iya dauka ba, se Kuma Wanda suke da number ta Suka ta Kira na Amma na mutum daya na dauka wato mahaifiya ta

" Unaisa me ya faru da me gidan ki?"

" Ya rasu!"

Na fada Mata a hankali, ban Kuma Jin me tace ba, na rutse idanuna se Kuma ga Kiran Dada, uwata wadda ta kasance tare dani a dukkan halin da nake ciki, na dauka Amma banyi magana ba se sheshekar kuka da nake, hakan yasa ta saki salati tana fadin

" Yallabai da gaske ya rasu, ku Kira zuhra mu tafi"

Anty Aisha ta karbe wayoyin a hannuna, duk Wanda ya Kira se ta dauka ta bada amsa, a wañnan halin muka karaso Kano. Allah yasa nasan gidan shi Haka na kwatanta muka Isa, an taru sosae abinka da Dan siyasa da yake akan mulki. Aka shiga Dani ciki shima Haka gawar tashi. A makeken parlon kasa Mata ne a zazzaune kowanne da carbi a hannunsa, I began to think Ina Suka samu ko dama sunsan zai mutu ne, already Dada da Zuhra da Badi'a har da Yaya khulthum sun karaso, Zuhra na ganina ta mike ta nufo ni ta rungume ni, Haka kukan mu ya tsananta, seda Dada ta janye ni ta rungume ni tana buga bayana a kunnena tana fadin

" Sabr Unaisa"

Na kankame ta inajin kamar zuciyata zatai bindiga Dan abinda nakeji yafi gaban misali. zaunar Dani tayi aka dakko min hijab na yaye mayafin Dake jikina, Allah kadai yasan tururin da zuciayata take. Babu jimawa har an Gama shirya shi, aka shigo dashi akan muyi masa addua, kafata har sarkewa takeyi saboda jiri da nake ji. Na tsugunna gefen shi, ga Mamaa wato First Lady, Asiya, Muhammad da Kuma Ahmad se ni, mune ahalin nashi. Banda kuka Babu abinda nake Yi seda Mamaa ta dubeni tace

" Kiyi Masa addua Unaisa ita yake bukata"

Na kalleta, she sure is a strong woman, na saukar da kaina Kan gawar shi Sannan na fara nema Masa gafara, ina saka ran zai huta a kabarin shi saboda shi din mutumin kirki ne. Muna kallo Haka aka fita dashi zuwa makwanci, na saka kaina cikin hijab kamar Raina zai fita, ban taba sanin Haka zafin ka rasa wani yake ba, ko lokacin da mahaifina ya rasu naji Babu dadi nayi kuka Amma Bai Kai ko kwatan abinda nake ji yanzun ba. Ana Kiran sallar maghrib Anna ta karaso hankali a tashe, suka shigo Muna hada idanu da ita na Kara sakin kuka, ta janyo ni jikinta tana fadin

" Kiyi hakuri! Ki Masa addua"

Seda nayi shiru sannan ta matsa gefen Mamaa suka yiwa juna gaisuwa, Suka gaisa da Asiya sannan Dada da sauran Yan uwan shi Suma, a hakan se kallon banza ake wurga Mata. Se bayan ishai aka sarara, ya rage bamu da yawa. Dada tasa aka kawo Mana abinci, Amma Babu yadda batayi ba naki naci, se kuka kawai nake na rashin madafa da Kuma tausayin kaina. Wannan yasa Mamaa rike hannuna ta fara kuka itama, tunda nazo Naga tana hawaye daga baya se ta daina, she's trying so hard to be strong for us. Asiya ma se ta biye mu, Haka Muhammad da shigowar shi da abokan shi zasu Mana gaisuwa. Dada ta dinga Mana nasiha da matan gurin, Sega wata dattijuwa me Kama dashi tasa mu da fada tana fadin

" Idan bakuyi hakuri ba ya zakuyi? Kowa yaji mutuwar nan Amma kukan ya Isa Haka, ke Hajiya Talatu idan kina kuka Unaisa da Asiya su mutu kenan? Dan Allah kuyi hakuri"

Aka taru ana bamu Baki se kukan ya lafa, Anna ta mike tace zata tafi gobe zata dawo, Dada da Mamaa suka ce basu San magana ba, Dole ta zauna dan a wañnan lokacin Ina bukatar support, Dole Anna ta zauna ga Anty Aisha, se kannena Mata su biyu Nuzla da Hunainah, Dan Dada tace ma Badi'a ta tafi gidan ta tunda Yaya Man yazo tafiya da ita. Acan bangaren muka koma, duka Suka fara Shirin kwanciya Amma Ina zaune saman carpet nayi shiru tare da tsirawa guri daya idanu, Anna ta zauna gefena itada Zuhra ba tareda tace komai ba, wannan Daren guangyadi kawai nayi. Da safe labari ya bazu sosae cikin kawayena da Yan uwan Kai kasar Baki daya, ko Ina ka duba hoton mu ne na ranar daurin aure, Yana sanye da bugaggiyar shadda blue wadda akai riga da Yar ciki, se katuwar babbar riga ta farar shadda, ni Kuma Ina sanye da dandatsetsen lace Blue irin shaddar shi, nayi kyau har na gaji, fuskar mu dauke da madaukakin annuri, Wanda ganin shi kawai se ya saka murmushi, hoton ma iya soft copy ne ya karaso Dan hardcopy Bai zo ba, "he died after three days of wedlock" shi ne caption din.

Tun asuba nake kuka bayan nayi sallah, Anna ta dinga bani Baki da Anty Aisha, yayinda Hunainah da Zuhra ke tayani kukan. Anty A'isha tasa nayi wanka Amma Babu ma kayan da zan saka, se kawai na maida Wanda na cire Dada ta shigo lokacin Ina saka socks a kafata saboda bana son iska a kafar, ta zauna gefena na gaishe ta cikin dasashiyar murya

" Ya hakurin mu? Allah ya jikan honorable"

Ta fada na amsa da Amin Nima na Mata gaisuwa, ta dubi su Anna Suka gaisa sannan aka shigo da abinci, tea ta hada min me kaurin gaske tace na daure nasha, se na fara hawaye Amma yadda take min bazan iya Mata musu ba, Haka na kafa Kai na Sha baifi rabi ba na aje, ba Wanda ya sani se na karasa Suka barni sannan ta kamo hannuna muka dawo can parlon Dan karban gaisuwa. Haka har seda akai kwana uku sannan Anty Aisha ta tafi, Anna da sisters Dina ma Suka tafi tunda Zuhra na nan, Dada Kuma na zuwa. ya rage daga mu se shakikan shi, nawa dangin da kawayena sun min Kara nasha waya kowa na min taaziyya, wasu ma nasan Basu Gama warware gajiyar bikina ba.

Da yamma Ina zaune a daki ni da Zuhra, a Rana na hudu, Asiya na parlor zaune tana waya Mamaa ta fito daga daki tana fadin

" Ku saka hijab zaa shigo"

Nikam dama da hijabina a jikina Dan Haka Asiya kadai ta zura nata, Anty Uwa ta dubeni tace

" Unaisa Banga Hajiya ba?"

Na dube ta nace

" Ai ta tafi tun dare Baku hadu ba?"

Tace

" Ina can Ina magana, Amma ai da ta zauna dake"

Bance komai ba na cigaba da Jan carbina kawai. Babu jimawa Ahmad ya shigo shi tunda akai rasuwar Bayan ankai shi banma Kara ganin shi ba, ya rame ya to duhu na kalleshi shima ni yake kallo, ya karaso ciki ya zauna Dan nesa Dani muka gaisa muka yiwa juna gaisuwa sannan yace

" Ina Mamaa? Bakin zasu shigo"

Kafin na amsa shi se gata ta fito da carpet na Mike, na karba na shimfida sannan Ahmad ya fita se gasu sun shigo,mutum daya na sani Abba, ya zauna da mutanen da suke tare muka gaisa sannan Suka Mana gaisuwa. Sannan Abba yace

" A ganina Babu amfanin a zauna ana Jan magana, lawyer company din shi yazo Hajiya talatu zamuyi proceeding da compiling dukkan dukiyar shi a Raba gado"

Haka fa abun yake, ka Tara dukiya kana rasuwar zancen gado zaa fara, Babu Wanda ya damu da Kai se na kusa da Kai, hawaye suka gangaro min. Nasan Mamaa lawyer ce Kuma ya fada min dukkan takardun shi a hannun ta suke. Ta mike ta dakko katon file ta aje sannan tace

" Amma hanzari ba gudu ba, Baku ganin a Dan Kara lokaci Koda zai kasance Unaisa nada ciki!"

Anty Uwa Dake gefe tace

" Ciki Kuma? Auren kwana ukun haba ke kuwa Hajiya Ladidi"

Abba ya dubeni nidai kaina a kasa yace

" It's very possible, ni tunanin hakan Bai ma zo minba. Ahmad how early ake iya detecting ciki?"

Ya dubeni sannan yace a kalla  da komai na mallakin dukiyar shi, tun ana lissafi Ina ganewa har kaina ya daina dauka, addua kawai nake Masa Allah ya gafarta masa. Anan aka ware abubuwan da ya riga ya mallaka Mana, ce Kar a raba gado dasu. Malamin dake zaune ya kissima yaga eh Bai Shiga yadda musulinci yace kada ayi considering ba. Gidan da ya saka ni ya mallaka min babu a gado,akwai wani gida na Mamaa ne, se wannan gidan ya barwa yaranshi kada a raba dashi.


Unaisa is not free, pay N300 to 3091721807 Aisha kwalam Hassan first Bank of Nigeria, send evidence of payment to 09063467258.

Continue Reading

You'll Also Like

1.3M 56.9K 27
အပျော်သဘောဖြင့် ရေးထားခြင်း ဖြစ်ပါသည်။
429K 82.5K 130
🍁 සුදුපාට පාසල් ඇඳුමේ තරුණ සුවඳ එක්ක කාකි ඇඳුමේ සුවඳ මුහු කරන් තේ දල්ලක කහට සුවඳ එක්ක එක යායට පෙනෙන රබර් යායවල්, ඇළ දොල වල සීතල දරාගෙන හිතුවක්කාර ය...
50.1K 3.8K 23
အခုခေတ်ရဲ့ B@d@ssက နှောင်းပိုင်းခေတ်ကို ရောက်သွားတဲ့အခါ...