✨MIJIN AMMINA NE SILA(COMPLET...

By NoorEemaan

8.8K 350 5

labari mai matukar ban tausayi, son zuciya, soyaaya mai zafi da shiga rai, hadi da nadama..... More

1
2
3
4
5
6
7
8
9
10
11
12
13
15
16
17
18
19
20
21
22
23
24
25
26
27
28
29
30
31
32
33
34
35
36

14

211 8 0
By NoorEemaan

🍇🍇MIJIN AMMINA NE SILA🍓🍓

written by noor Eemaan
wattpad:NoorEemaan

page27-28

cikin sauri ma'aikatan suna shiga duba ko wani lungu da tsakon gidan, shima alhaji shettima ba'a barshi abaya ba har da shi ake neman nata, bayan sun duba ko ina basu ganta ba suka sanar da alhaji cewa bafa ta cikin gidan, cikin wani tashin hankali yafara tunanin ina taje? can sai ya kalli mai gadi babu alamun wasa yace
"kodai ka bude mata gate ne?
murya na rawa mai gadi yace "wallahi tallahi alhaji ban bude mata gate ba" domin shi kam be shirya rasa aikinsa ba...
"Toh acikin ku waye yaji fitar ta?"
shiru duk sukayi sai daya daga ciki yace

"ni dai alhaji ina kwance adaki naji an diro kasa, amma ban leka ba"

Cikin takaici alhaji shettima yace kwada masa mari yace"shashashan banzan da wofi meyasa baka lekan ba?" domin alhaji shettima ya fahimci cewa lada ta hau ta dira kasa, tunda me gadi be bude mata ba domin babu wata hanyar agidan, adaran nan yasa dukkansu banda megadi baza nemanta, shima mota ya hau ya bar gidan...

Duk inda suke tunanin zasu ganta sun duba amma ko alamarta babu, har karfen bakwai din safe suke nemanta, dasuka gaji kawai ya kira su kwaro yace duk inda suka ga abrar su kawo masa ita tunda sun santa ya kuma yimusu alkwarin basu kyauta me tsako, domin shi be shirya  asirinsa ya tonu ba, domin ana ganin mutuncinsa agarin na abuja sosai,  da wanda ya nufi gida...

Bangaren ammi kuwa gaba daya ta fita a hayyacinta kuka take sosai, kukan nadama akurarren lokaci, "wani hali abrar take yanzu?" shine tambayar dake kai kawo aranta, gashi tana rufe balle tasamu ta fita ko Allah ze sa tayi dacen ganin yarta, tana cikin wanna tunanin taji an dan bude kofar hadi da tura mata plate din abinci kafin ta taso an rufe kofar...

"Waye nan? wanene dan Allah abude min inje neman yata"...

dariyar alhaji shettima taji yace "hajiyata ki kwantar da hankali, ana kan nema miki yarki, sai dai kisani idan an ganta wani gidan daban zan kaita in cigaba da lasar zumanta domin bazan iya barinta ba,  za kuma ki cigaba da zama anan dakin har a ga abrar, karki damu zan dinga turo miki abinci kullum"...

cikin kuka ammi tace "Allah ya isa tsakanina da kai, sai ka wulakanta aduniya, idan ka isa ka sake ni na bar maka gidan ka, domin gidanan tamkar kuzurmin daji haka nake ganinta"

"hhhh hajiyata kenan ina raga miki ne saboda son hadi da sha'awar da nake wa abrar daba haka ba... sai ya ja kwafa hadi da barin wurin.

da misalin karfe hudun yamma zaune suke a babban falon gidansu su duka ukun yayinda mummy ta kalli hanan dake faman danna waya rai abace tace "ke kam hanan me damuwarki ne"
"tambayeta mummy ta damu mutane da tsaki" amal ta fada tana harararta.
turo baki tayi tace "mummy ki raba  ni da anty amal"
"ke ni ba wanna na tambayeki ba, meke damunki?"
"number amminsu abrar nake ta kira baya shiga, gashi inason zuwa gidan".

mummy na shirin bata amsa suka ji wani razananan ihu da sautin sa ya karade duk ila'irin mainson din nasu, kallon kallo aka shiga yi tsakanin mummy, hanan, amal, yayinda suka mike atare suka nufi bangaren aaban domin tabass ta nan wanna ihun ke tashi, suna kokarin hawa matattakala sai suka ji dariyarta na tashi sosai can kuma sai kuka  gaba daya suka rugo aguje suka dawo falon har da mummy kuwa😅 kukan ne ya shi gaba da tashi yayinda suka zauna jugum cikin rashin sanin abunyi, dadinta daya yau aaban da wuri ze dawo, take ciwon abrar ya fadowa hanan, domin irin ciwon abrar ne wanna patient din ya aaban keyi amma nata be kai wanna ba, sun kai awa daya awanna halin kana suka ji tsayuwar motar aaban ajiyar zuciya suka sauke, yana sallama yabi su da kallon mamaki se dai be tambaya ba, be kuma nuna afuska ba, "yawwa son welcome home, ga patient dinka can tana kuka  hadi da dariya kaje ka duba awani hali take ciki"..

jinjina kai yayi alamun "toh" duk da yayi mamakin abunda tace toh kenan meye matsalarta? ya aiyana aransa yana nufan side din nashi, sai duk suka bara masa baya, suna zuwa kofar dakin suka tsaya domin har yanzu dariyar hadi da kukan na tashi.

ko dar be jiba ya shige dakin, hannu yasa ya rike kugunsa, ganin yanda gaba daya ta sanja masa kamanin daki, tamkar dakin mahaukata, kallonta yayi yaga gaba daya gashinta ya kara hargitsewa ya dawo gaban fuskarta duka wanda hakan yasake rufe face dinta.

cikin tafiyar sa ta burgewa yakarasa wajenta hadi da karbe wani kwalben turarensa  data fasa, g jini ahannunta da alama ta caka wa kanta, tana jin ya karbe ta fasa wani ihu hadi da bubbuga hanunsa sai ta dau pillow ta shiga dukkansa dashi, hannunta ya damko kana cikin husky voice dinsa yace "will keep the hell out shout"
kamar kuwa taji tayi shiru din, sai kuma ta fara kyakyale dariya har da kifewa kan gadonsa, wasu allurori ya hada mata  yayimata babu jimawa kuwa  bacci yadauketa, take ya fahimci matsalarta, duk da shi karatunsa ba bangaren kwakwalwa yayi taba, zai yiwa abokinsa musaddiq magana ya zo duba aihinin matsalan domin ya tabattar...

kallonsu mummy yayi yayinda ya hango tausayinta a idanunsu, domin kwantar musu da hankali yace "kada ku damu mum nayimata allura xata dau lokaci bata farka ba"
"toh son, bazaka ci abincin ba?"
"no mum sai dare"
"ok ka kula da kanka please, ko hanan ta gyara maka dakin, tunda bakason masu aiki suyi maka"
"noo mum, i will do it my self tnx" yafadi haka yana bata peck (sumbata) a kumatu.
murmushi tayi kana suka bar wajen

bayan ya cire rigar suit dinsa, ta cikin data kasance fari ya tattare hannun, nan ya shiga aiki, komai data hargitse ya mayar da ita muhallinsa yayinda wadanda suka fashe ya zubar a waste bin( kwandon shara) kana ya share dakin ya goge take dakin ya dawo hayyacinsa, wanka ya shiga bayan ya gama yasa kananun kaya marasa nauyi ya dawo kan sofa, sai kuma ya mike ya bude wardrobe dinsa ya ciro rigar abrar dinnan data yayyage, ya kwanta kan sofa ya bar rigar kan fuskarshi yayinda yake shakan natural body scent dinta dake sa masa nutsuwa, tunaninta yake as usually yayinda kaunar ta ke karuwa aransa, kiran sallah magriba ne ya katse masa tunaninsa...

washegari yana off hakan yasa shi kiran doctor musaddiq abokinsa, wanda ya masa alkawarin zuwa da rana tunda yana half day ne, kamar yadda ya alkawaranta sai gashi da rana da kayan dazai mata gwaji domin daman aaban yayi masa bayanin yanayin ciwon nata, bayan ya gama duba ta, suka dawo falon kasa, nan ya shiga yi musu bayanin ciwonta tamkar dai yanda likitan nan a cyprus yayiwa hanan sai dai bambamcinsu shine, wanna karon ciwon ya sake ninka na baya... sun yi matukar tausaya mata, ga hanan datake wani tunanin na daban, domin irin  ciwon patient din ya aaban shi abrar ke fama dashi
"ya Allah kasa abrar na cikin kwaciyar hankali" tafada cikin kaunar kawarta...

"bayan sati daya"
alhaji abdur-rauf ya diro kasar nigeria domin yayi hutun daya dauka tsayin wata biyu da iyalansa domin ba karamin kewarsu yayi ba. gaba daya gidan ya kacame da murna daga masu gidan har yan aiki, domin daddy shi kowa nasa ne, har dare baki na zuwa yimasa sannu da zuwa, hakan yasa be zauna sun tattauna da iyalansa ba,...

sai washe gari daya kasance sunday suna zaune dukkansu suna hira, abun birgewa  daddy ya zauna cikin iyalansa suna ta raha da nishadi, wanda su mummy sunyi missing wanna kyakyawan halin nasa, hajiya mummy baki yaki rufuwa daddy ya dawo lolz😜
"mummynsu jiya kin fara min magana akan abokina, (aaban, domin da haka yake kiranshi tun yarinta) tukunna ma yana ina?  wai har yanzu baya shiga jama'a? anya bake ya yayo ba kuwa?" yafada cikin zolaya yana kallon mum, dariya sukayi kana mummy tace "ai daddy wanna abokin naka Allah kadai yasan inda yasamo wanna halin nashi, sanna zan so yana nan sai mu hadu muyi maganar gaba daya alright bari na kira shi"  daddy ya fada.

bangaren aaban kuwa yana zaune idanunsa a lumshe yana tunanin decent one dinshi, jin motsi yasa shi ware idanunsa abrar ya gani zaune tana  kokarin   tashi, kara rufe idanunsa  yayi yana tunanin kai ta asibitin kwakwalwa domin aduba ta duk da besan ya kalar fuskarta yake har yanzu ba, amma yaji yana da niyyar taimaka mata.

sake ware idanunsa yayi adalilin ringing din da wayarsa keyi, karawa yayi akunne bayan ya daga yaji ance "abokina kazo falo muna jiran ka yanzu"
"ok dad" ya amsa ataikace

yana zuwa ya zauna akusa da daddy yayi shiru idanunsa alumse, murmushi mai sauti daddy yayi kana yace
"mummynsu ina jinki?"
"daddy daman akan maganar auren aaban ne, yasamu matar aure, shine nakeso anema masa auranta, yarinyar dai kawar hanan ce, duk da bamu gama sanin address din su ba, amma na na yaba da hankalinta kwarai... hanan na shirin tambayar wacce kawar tata, suka ji dariya hadi da kuka na tunkarosu yayinda cikin sauri take taka benen domin saukowa gaba daya suka juyo suna kallonta banda aaban da idanunsa ke alumshe, daddy da fuskarsa ya nuna mamaki domin besan da zamanta cikin gidan ba,,, "wacece wannan" daddy ya tambaya.
nan mummy ta shiga bashi labarin komai da komai... cikin tausayawa yace "Allah ya bata lafiya, sai ya kalli abaan yace abokina da an kaita asibiti ayi aikin ko za'a dace ko?"
"eh dad abinda nake shirin yi kenan"
"toh masha Allah" daddy ya fada.
daddy yace "wacce unguwa suke, indai an san unguwar, toh sanin gidan da sauki ai, mummy zata yi magana suka ga abrar da ta yi zaman yan bori akasa ta mike hadi da  daura hannunta kan gwiwowinta kamar dai ruku'u, sai tasake dago kanta wanda hakan yasa gashinta mai uban yawa yin baya take fuskarta ya nuna, nan ta shiga bin ko wannesu da kallo sai kuma tafara zallan kuka mai ban tausayi, sai lokacin aaban ya bude idanunsa yasauke su kan beautiful face dinta kara murza idanunsa yayi domin tabbatarwa,  cikin sauri ya mike kana ya tunkareta hadi da cewa
"decent one" yayinda hanan tace " bestie abrar kallon mamaki hanan da aaban suka yiwa juna, yayinda suka jefa su mummy cikin duhu...

share pls✔
comment✔
vote✔
edit❌

gaskiya comment dinku yana kadan, idan baku kara ba zan rage typing, domin baku bani karfin guiwan typing, tunda bazai yu in dinga typing domin faranta muku ace kuma kalillan ne zasu na comment ba

noor Eemaan✍

https://chat.whatsapp.com/FEfWeTiufpk96my8yNBeaM

Continue Reading

You'll Also Like

11.7K 870 31
"You were magnificent, Satoru Gojo. I will never forget you for as long as I live." Satoru Gojo laid there, bisected in half, as if the universe itse...
68.3K 7K 53
A life of a strict father who is a soldier raising his 2 kids along with his duties.
375K 39K 21
انا العاصفة الحمراء ألتي تراهن وتربح انا القوة العظيمة الذي سوف تنهك كُل الارواح الجنون والتلاعب بحد ذاته هنا أستطيع ان اتلاعب بعقلك حَد الجنون امر...
256K 4.3K 61
This is an unofficial fan-made English translation of We are...คือเรารักกัน (We are... we are in love). Please do not re-translate to any other langu...