✨MIJIN AMMINA NE SILA(COMPLET...

By NoorEemaan

7.6K 310 5

labari mai matukar ban tausayi, son zuciya, soyaaya mai zafi da shiga rai, hadi da nadama..... More

1
2
3
4
5
6
7
8
9
11
12
13
14
15
16
17
18
19
20
21
22
23
24
25
26
27
28
29
30
31
32
33
34
35
36

10

208 5 0
By NoorEemaan

🍇🍇MIJIN AMMINA NE SILA🍓🍓

written by noor Eemaan
wattpad@NoorEemaan

page 19-20

sai da ta tabattar da tayi nesa daga gidan da alhaji shettima ya kaita kana ta tsaya jikin wata bushiya tana sauke numfashi, kuka takeso take har ta sauka kan guiwowinta domin jitayi kafafunta sun gaza daukarta ta kai kusan mintuna ashirin awanna halin...
hanan ce ta taho tana waige waige ko zata ga abrar, ai kuwa tun daga nesa ta hangota da gudu ta karosa wajenta hadi da dafata afirgice abrar ta dago kanta ganin hanan ce yasa ta rungumeta cikin hanan kukan tasa, kukan tausayin abrar sun dau tsahon lokaci kana suka tsagaita
"abrar waye ya dauke ki? ya miki wani abu?" cikin damuwa hanan ta jera mata wandanan tambayoyin.
"hanan so yake yaga bana numfashi adoron duniya sannan hankalinsa zai kwanta harnan cyprus ya biyo niiiiii" ta ja karshen maganar cikin kuka...
"what! kina nufin mijin ammi?"
"eh shine "
"innalillahi wa inna ilahi raju'un, amma babu abunda yamiki ko?" hanan ta tambaya cikin damuwa
jinjina kai tayi alamun "eh" ajiyar zuciya hanan ta sauke tace "thank God"
ganin nisan dake tsakanin wajen da cikin hostel din ba nisa yasa suka karasa akafa...

bangaren alhaji shettima kuwa ya kai kusan awa daya yana rike da maransa domin ba karamin buguwa yayi ba bayan ya dan ji dama dama ya koma hotel din daya sauka, washegari ya koma nigeria cikin rashin jin dadi domin sosai yaso yasake lasar zumanta amma duk da haka zai biyo mata ta wata hanyar....

tun daga ranar da abunan ya faru abrar ta sake shiga damuwa fiyeda na baya, ta sake ramewa sakamakon tsoro da firgici gani take alhaji shettima zai sake zuwa har hostel dinsu, bata da aiki sai kuka- kuka tun hanan na lallashi har tayi shiru ta zuba mata ido, wata rana cikin dare suna bacci, abrar ta fara kyakyata dariya sosai dayayi sanadiyar farkawan hanan da linda, gaba daya ta hargitsa dakin ta sanja masa kamanin komai hannuta ya taba sai da buga shi da kasa, in mai fashewa ne yafashe, linda kuwa makurewa tayi can karshen gadonta tana zaro idanuwa (kun san turawa ajebo's ne basu son ganin tashin hankali😂) cikin sauri hanan ta nufe ta shiga jijigata "abrar what are you doing to your self? ki daina dan Allah!" dif dariyanta ya dauke kurawa abrar ido tayi na tsawon mintuna sai kuma ta fashe da kuka mai tsuma zuciya..
"hanan kisan me?
"a'a" hanan ta amsa cikin tausayinta
"idan mun kamalla karatun mu na zama lawyer, sai na maka shettima mijin ammina akotu, kuma idan alkali bai yanke masa hukunci daidai da zalunci daya yi mun ba sai na yanke masa da hannuna ta fada cikin fitar hayyaci hadi da kallon hannun nata, addu'oi hanan ta tofa mata babu jimawa kuwa bacci ya dauketa ajiyar zuciya hanan ta sauke hadi da rufe ta da bedsheet, sai lokacin ta lura da linda dake takura da bata cikin damuwa babu abunda zai ta yin dariya
" linda she's fine now, you can now go back to sleep"
"are you sure?" linda ta fada atsorace
"yeah sure" hanan ta amsa tana haye gadonta, tunani ta shiga yi fatan ta kada abunda take zargi ne ke damun abrar, dole gobe ta kaita hospital adubata gashi daman gobe basu da lecture duk da cewa babu wasu kudi a acct dinta amma zata kira ya aaban ya turo mata da wanna tunanin ta kwanta bacci...

washegari hanan tace abrar ta shirya zasu asibiti ba musu ba tambaya ta shiga shiryawa domin yanzu ba bakomai dake tambaya akansa ba saboda tsananin damuwan dake ranta, itama hanan shiryawa tayi sai a sannan ta fara dialing number aaban...

yana dakin gymming dinsa yayinda yake daga karfe cikin kwarewa gaba daya ya hada gumi ringing din wayarsa daya shine ya sa shi ajiye karfen ahankali hadi da mikewa, latsa kore yayi kana yayi sallama cikin muryansa mai dadin amo, amsawa abrar tayi hadi da gaishe shi, sannan ta fara cewa "uhmmm hmm ya aaban ina wanna kawata ta school bata da lafiya inaso...... you know banason dogon bayani just go straight to the point" jinjina kai tayi kana tace "i want money" kit ya kashe wayar bayan kamar minti taji alert ya shigo zaro ido tayi lokacin data ga yawan kudin daya turo duk da cewa tasan yayanta bai iya bada karamin kyauta ba amma tayi mamakin yawan kudi, sake dialing numbers shi tayi tana ji ya daga tace"yaa aaban nagode sosai, sai kawai yaji muryan abrar ta cikin wayar ta ratsa ta kunnuwansa tace"hanan let's go"
jiyayi wani yanayi na shigarsa haka kawai yakeson sanin mallakiyar mai zazzakar murya nan don haka yace "hanan who is that?"
"my best friend" bai kara cewa komai ya kashe wayar... da kallon mamaki tabi numbers yayinda take murmushi "wai yau ya aaban da kansa ya tambayi wata mace?"
"mummy most hear this" tafada tana murmushi, suna hanyar zuwa asibiti hanan ta fesa wa mummy cikin murna da mamaki mummy tace wacece? dariya hanan tayi ganin yanda mummy tayi maganar cikin zumudi "mummy abraer ce fa" ta fada tana kallon data fada duniyar tunani bayan sun gama wayar mummy ta jima tana mamaki domin ada tayi tunanin danta bashida cikakken lafiya, sai kuma tayi masa sha'awar auren abrar din domin tana son yarinyar hakan nan duk da bata taba ganin ta ba, hanan na yawan fadin kyawawan hallayenta, amma hakan baya nufin zata yi masa dole, duk da cewa shi din mai yi mata biyayya ne...

(tofah readers kuna ganin cewa mummy zata amince danta ya auri abrar idan taji kaddaran daya fada maka? ku dai cigaba da bin alkalamin noor dan jin yanda zata kaya a book din Mijin ammina ne sila).

bayan sun isa asibitin doctor hanan tayi masa bayanin yanda abrar keyi kwanan na nan yace sai sun zo da iyayensu zasu iya dubata, nan hanan ta nuna masa cewa iyayensa basa wanna kasar da kuma amincewarsu suka zo, ganin yanda anan tayi kallan tausayi yasa shi amincewa, amma ya gaya mata cewa za'a caje su kudi masu yawa ta nuna masa cewa basu da matsalan kudi...
bayan duk sun tanadi kayan aikinsu aka shigar da abrar wani daki yan gwaje gwajensu sukayi hadi da daukan hoton kwakwalwarta, bayan awa daya da rabi doctor ya fito yace anan ta bishi office dinsa...

Bayan ta shiga ya bata umarnin zama kallonta yayi na few seconds yace"you said the other girl is your sister right?"
Jinjina kai hanan tayi alamun "eh"
"ok sorry to ask are your parents still alives?" cikin mamaki tambayoyinsa hanan tace "of course yes!"
"You mean iyayenku na raye suka barta cikin wanna dangerous condition din. Doctor'n ya fada cikin mamaki
"Doctor please just go straight to the point" hanan ta fada cikin damuwa gyara medicated glass din idon shi yayi kana yafara magana cikin harshen turanci

"Asakamakon gwagwajen da muka yi mata mun tabattar da cewa tadauke da hawan jini, sannan kwakwalwarta yafara samun matsala domin idan aka cigaba ahaka ma'ana bata bawa kwakwalwarta hutu toh zata iya samun tabin hankali gashi ta dauko hanya, nayi matukar mamakin ganin wanna karamar yarinya cikin wannna mummunan halin domin ban taba jin karo da hakan ba duk da akwai wandanda ake haifa da irin wanna cuta amma bincike ya nuna damuwa, rashin hutu, firgice, hadi da rashin bacci sune suka haddasa nata wanda abubuwa da dama zai iya kawo shi kamar ko mutum ya ga abunda ya yi matukar firgita shi, kuma ace ya cigaba da gani ko wacce aka wa fyade ta karfi da yaji da dai sauran su ".

"innalillahi wa innah ila'ihi raju'un" hanan ta fada kamar zata saki kuka.
"amma bazata iya warkewa ba kenan doctor"?

"zata iya warkewa idan aka mata aiki amma, ba yin aiki bane solution, babban solution shine sai ta samu kwanciyar hali da bawa kanta cikakken hutu sannan aikin zai tafi yanda akeso domin bazai yu ayi aiki amma ta cigaba da dasa damuwa aranta tofah baza'a samu abunda akeso ba, dole sai tasamu mai debe mata kewa ta daina tunani dasa damuwa aranta, any way ga wasu magunguna zan rubuta miki zasu taimaka mata da yardan Allah" bayan ya gama ya mika mata takardan hadi da takardun aka dau hoton brain dinta, asanyaye hanan ta fito bayan ta siyi maganin ta biya kudin komai da komai dan kudin daya rage saura kadan domin asibitin suna da chajin kudi sosai...

tana juyowa ta ga abrar ta fito daga dakin da aka kaita, tun daga nesa hanan ke mata kallon tausayi "yanzu ace abrar mai kananun shekaru ke dauke da irin wanna cutan ita daya?" ta aiyana aranta...
bayan abrar ta karaso tace
"hey malama kallon fa" ta fada tana murguda dan mitsisin bakinta, dariya mai tafe da hawaye hanan tayi sai kuma ta riko hannunta suka fito daga asibitin

"wai hanan meyasa kika kawoni asibiti? nifa lafiya ta kalau"

hararan wasa hanan ta zabga tace"ban saniba yar rainin sense sai yanzu kika ga daman tambaya na"

dariya abrar ta yi tace" wallahi hanan har jikokin ki sun shiga uku da masifarki"
murmushi jinjina hanan tayi ko ba komai taji dadin yanda abrar tadan yi magana, hannunta takamo zuwa wajen wasu bayan dutsina gwanin sha'awa tamkar kujerar ta zama bayan sun zauna hanan tace

"jokes apart abrar mekikeso ki ja wa kanki? i know abunda ya faru dake yana da matukar ciwo amma ba yana nufin zaki cigaba da sa damuwa aranki ba, abrar damuwa bata gyara komai naji matukar tsoro lokacin da doctor ya fadi abunda yake damunki dan Allah ki kwantar da hankali wallahi bazan iya jure rasa kawa mai kyawun dabi'u kamar ki ba please ki taimaka ki rage damuwa akwai masu bukatar rayuwarki da yawa domin tana da muhimmanci agaresu, kalli result dinki cikin sauri abrar ta amshi takardun bayan ta gama karantawa sai ta kwashe da wani irin dariya ta dau wasu mintuna tana dariyan kana tayi shiru sai kuma ta fashe da kuka mai ban tausayi tace " hanan ko daya banajin ciwon abunda doctor yace yana damuna kamar yadda nake kan jin ciwon rasa budurcina, abu mafi daraja da kowacce mace mai mutunci ke alfahari dashi matukar ta kaishi gidan mijinta, hanan ki gayamin ina abunda zan kai gidan mijin? shin wazai aure ni ahaka wazai auri ragowar mijin ammina abrar ta fada tana jijjiga hanan sannan tace ki gayamun hanan bana jin zan iya daina damuwa hanan ba laifina bane i can't just control it"

"toh zan gayawa ammi, zan gaya mata matukar zaki cigaba a haka" hanan ta tace cikin fada fada
cikin sauri abrar ta riko hannunta tace "hanan kada ki gaya mata komai dan Allah, ammina na cikin kwanciyar hankali tana matukar son mijinta, ta yarda da shi fiyeda ni shiyasa ta kasa amicewa da abunda na fada mata, ba bukatata ammi tasan abunda doctor yace yana damuna ba a'a bukatata ammi ta amincewa da cewa gaskiya na fada mata komai dadewa koda bana raye aduniyan, duk da haka ina matukar son ammina domin ita ce halitta mafi soyuwa agareni banason abunda zai daga mata hankali kimin alkawari bazaki gaya mata ba pleaseeeee" ta ja karshen maganar cikin kuka mai ban tausayi....

cikin kuka hanan tace " bazan gaya mata ba i promise you this, rungume hanan abrar tayi tace nagode miki sosai bestie hanan nagode da kaunar da kike nuna min since from the very first day we met, ina sonki fisabilillah ina kuma fatan Allah ya hada mun har a aljanna madaukakiyya"
"ameen abrar nima sonki"sun dau tsahon lokaci suna kuka kana suka koma hostel...

"welcome home aaban" mummy ta fada
"tnx mom" aaban ya amsa yana bata peck agoshi murmushi mummy tayi
tace "aaban my son na girka maka favorite dinka da hannuna, am sure you will love it"
murmushin da iyakarsa lebe yayi domin shi ba ma'abocin son abunci bane sosai, yafi ganewa su coffe, black tea, soft drink da snacks haka amma yaji dadi sosai musamman da mummy ce ta girka masa da kanta "thank you, mummy bari nayi wanka"
"ok son you re welcome"...

ya dau kusan mintuna arba'in kana ya fito sanye da ash 3quarter hadi da black jersey armless sosai kirarsa ta karfafa yasake fitowa sumar nan a kwance luf luf aaban ba dai haduwa ba, tun daga nesa mummy ke kallon shi cikin alfahari da godiya ga Allah daya bata shi, serving dinsa tayi da pounded yam hadi da egusi da ya sha su kifi banda, naman rago, gwanda, stock fish, ugu, da dai sauransu babu abunda ke tashi sai kamshi (ko ni dana leka miyar sai da na hadiyi yawu😜)
yana kai loma daya bakinsa yace "yummy you re always a good cook mom" murmushin jin dadi mummy tayi (kusan ba wanda baya so a yabe shi) da kyar dai ya cinye malmala daya saboda farinciki mummynsa kana ya dawo falo ya zauna, ayanda yake zaka yi tunanin ba shi da ko digon damuwa amma azuciya shi kadai yasan abunda ke damunshi, gyaran murya mummy tayi kana tace "son inaso muyi magana it's hightime ace yanzu ka ajiye iyali shin kana da wacce kakeso ne? idan babu nayi maka sha'awar kawar hanan abrar domin na yaba da hankalinta, jiyayi gabansa ya bada dam! adalilin sunan abrar daya ji....

kuyi hakuri dan Allah wallahi nayi typing mai yawa ya goge😰 manage this pls...

noor Eemaan✍

SHARE PLS✔
VOTE✔
COMMENT✔
EDIT❌

https://chat.whatsapp.com/FEfWeTiufpk96my8yNBeaM

Continue Reading

You'll Also Like

1.7M 55.6K 75
Alexander, James and Skye were triplets. They were stolen from their family at the age of 4. The family searched for them day and night never giving...
310K 22.5K 27
Avantika Aadish Rajawat Aadi, with his fiery nature, adds intensity and excitement to their relationship, igniting a spark in Avni. Avni, like the ca...
502K 10.9K 51
Two girls are exchanged at birth and are given to the wrong mothers and after 13 years the truth comes out Rosabella Rossi is different from her sist...
276K 17.7K 48
The feeling of being abandoned by one's own family was not unknown to Aadhira. She hates her family for abandoning her when she was only a newborn, l...