2

1.3K 71 0
                                    

_*NAYI DACE*_

Maryam💕
Wattpad@mamsuhaimerh

II

      GASHI KU DANDANA ZUWA BAYAN SALLAH INSHA ALLAH😘😘

Kaina naji ya fara sarawa na rufe littafin na ajiye,lokacin hutawa yayi kenan Kar Kuma naje na rubuta rubbish

Wattpad na bud'e na duba littafin da nake karantawa nayi cigaba da karantawa,a half har bacci ya debeni

Washegari cikin doki na nufi makaranta, confidence sosai nakeji akan jarrabawar yau kuma alhamdulillah,na sameta yanda na shirya Mata

Mun Gama exams lafiya na Kuma ci gaba da jigilar yiwa su Yaya girki,har yanzu Saleh kunyata yakeji tun allurar da na Masa ni Kuma bana nuna masa wani Abu dukda Yana bani dariya idan na ganshi

A Dan hutun da muke na nemi makaranta ta bani takarda Domin na ziyarci wani asbitin na Karo ilmi kafin mu koma,a take aka bani approval,asbitin sharad'a na shiga na Basu takardar suka Kuma amince zan dinga zuwa Ina practicing acan

Ina da matukar son karatu sannan ina kaunar field Dina,na samu matsala a shekara ta biyu wadda ta janyomin maimaita dukka shekarar,hakan ne ya karamin karfi gwiwar da na zage dantse da karatuna

Tare da su Yaya muka fita suka ajiyeni a asbitin, bangaren haihuwa aka kaini Wanda nafi tsoronsa akan kowane bangare

Labour room muka fara zuwa babbar nurse din na ordering Dina nayi abubuwa,zuciyata ta karaya ganin yanda Mata ke Shan wuya tun kafin ma haihuwar tazo

Tsayawa mukayi Kan wata Mata dake jijjiga,hankalina ya tashi sosai da kyar na zama calm na tsaya a wurin

Matar ta galabaita sosai,bleeding take Wanda har nurse din saida ya Bata tsoro

Tun safiyarnan ake fama da wannan baiwar Allah sai biyar ta haihu,zuwa yanzu Kam na Gama karaya Dan naga iya ganina,Mata suna Shan bakar wahala wajen haihuwa

Kallo d'aya matarnan ta yiwa jaririnta tace

"Allah yayi maka albarka"

Kalmarta ta karshe kenan wadda ta fito sarari Bata sake cewa komai ba,a gaban idona yau mutum ya mutu,mace ta mutu bayan haihuwa

Fita nayi cike da tsoro,hawaye ke zuba daga idona Ina hango matarnan a cikin kwakwalwata

Yaya na Kira Ina Kuka nace yazo ya d'aukeni,Ina shiga motar na fara musu sambatu

"Yaya ta mutu,sanadin ta kawo Rai wannan duniyar ta rasa nata,Yaya yaronnan zai tashi maraya,a gaban idona ta mutu bayan Tasha wahala,Yaya...."

Katseni yaya yayi hankalinsa na Kan tu'kinsa yace

"Bilki,idan fa mutuwa ce kinyi sallama.da ita kenan,Babu abinda Zaki iya kiyi ha'kuri kawai shine,Allah da ya kawo jaririnnan duniya shi yasan yanda zaiyi dashi,kedai Baki kashe ta ba,Kuma tunda bazaki iya kasheta ki Raya ta ba mene na damuwa?muje na siya Miki shawarma kinji?"

Takaici ne ya sake isata,maimakon naji sassauci sai naji zuciyata ta sake karaya,cigaba nayi da Kuka Saleh yace

"Haba man,wannan wani irin rarrashi ne?mace ce fa Dole taji daban a ranta,kuma wannan rarrashin naka ai kaman kace ta sake yin Kuka ne,tsaya ka gani"

Bude gaban motar Saleh yayi ya dawo baya inda nake,saukar da muryarsa yayi yace

"Kiyi ha'kuri kinji kanwarmu, addu'a Zaki Mata da jaririn nata,Kinga ita fa tayi shahada aljanna straight zata tafi,Kuma Allah bazai bar abinda ta Bari ya wulakanta ko yasha wahala ba,ki zama mai juriya tunda haka yanayin aikinki yake,idan kina d'aga hankalinki bazaki dinga bawa marasa lafiya kulawar da suke bukata ba,nasan Zaki damu Amma ki takaita damuwarki"

NAYI DACE.Where stories live. Discover now