"Ƙarya kike yi ki ce min kina so na kuma kiyi zaton zan yarda ahh me zaki yi da saura second hand sauran khadijah wanda bai da kyau wanda bai da ajin da zaki saurara wanda bai kai matsayin wanda zaki kalla ki nuna a matsayin wanda kike tare da shi har ki kira shi da saurayin ki ta ya kike tsammanin waɗannan yaudararun kalamai na ki zasu yaudare ni for the second time kuma never"!!! Ya ida yana girgiza kan shi nima girgiza kan nake yi ina kuka kamar rai na

"I take them back ka min uziri dan girman Allah those words were out of anger ba a cikin hayyaci na na furta su ba believe me ba da gaske na ke ba faɗa kawai na yi amma bai kai zuciya ta ba"!!..

Wani irin kallo ya min wanda ya saka ni a ruɗu dan na kasa fassara ma'anar kallon bai ce min uffan ba ya ce

"Hmmm Ms Murad kenan me ya sa kika iya yaudara ne wai haka kin kware a iya poisoning mutum gabaɗaya i can't trust you anymore"... Waɗannan kalamai nasa kamar saukar dalma na ji su ya zan fahimtar da shi ya gane cewa ko a da ɗin ba da gaske na furta kalaman da na masa ba duk ni na janyowa kaina

Sai da ya ga da gasken kukan da nake yi ba crocodile tears ke fitowa ba sai ya tausasa muryar shi

  "Aisha ki gaya min gaskiya ke ma turo ki aka yi dan in saba da ke in faɗa tarkon son ki sannan ki bayar da ni ga waɗanda suka turo ki"?? Subhanallah iya abin da nake ta nanatawa a zuciya ta kenan ba dai kallon rashin yarda yake min ba in ko haka ne toh na yi wa kaina a yadda ya taso cikin wata bahaguwar rayuwa ta rashin yarda har karshen rayuwar mu ba zai taɓa yarda da ni ba me zan yi dan in gyara wanna rift ɗin a brain ɗin shi kawai nuna mai so da kauna zaki na yi a ko da yaushe cewar ɗayar zuciya ta dan haka na haɗa dukka zantukar da zan gaya mai domin wanke mummunar taɓon da yake zuciyar shi a kai na..

"Abdulrahman kalle ni"kallon na wa yayi cikin ido sai da na tabbatar da mun sami good eye contact kuma mun yi maintaining ɗin shi dan ta haka kawai nake ganin zai fi yarda ya ba wa magana ta muhimmanci

"Abdulrahman ka yarda da ni ban taɓa zalintar ka ba ko daidai da second ɗaya ban taɓa yarda wani abin cin zarafi ko wulaƙantuwa ya same ka ba ban taɓa kuskuren yarda a yi amfani da ni dan a cin ma wani manufa ba ka yarda da ni Abdulrahman tun ranar da na maka waɗannan kalamai ban kuma samin isashiyar bacci ba dan da zarar na kwanta bacci ya fara dauka ta sai in tashi sabpda ban da natsuwar zuci hankali na kullum a tashe yake tun ranar har yau aunty mama ba ta sake min bata bani kulawar da ya kamata saboda fushi ta ke da ni duk a kan ka office na daina zuwa tun ranar da abin nan ya faru alakata da khadijah has fade away duk saboda kai Abdulrahman zuwa na nan na biyu kenan ina zuwa in zauna in yi kuka in yi danasanin abin da na gaya maka baka gani ba duk na chanza daga yadda nake zuwa wata iri na fita a kamannina na koma wata iri na rame kullum cikin tunani da nadama nake na gama rurufe kofofin alkhairai na ban taɓa tunanin zan buɗewa wani ɗa namiji zuciya ta ba tun yanzu saboda abin da ya faru da ni na ɗauka daga kan shi shikenan na dai na soyayya saboda shi ya nuna min *Soyayya Mai Garɗi* shi ya koya min komai daga baya na rasa shi tun daga kan shi ban kuma gigin yarda da wani ɗa namiji ba dan haka lokacin da ka zo min da wannan maganar a banbarakwai ya riske ni ban mai fahimtar fasali ba duba da cewa kai ɗin husband to be ne na aminiyata khadijah ba zan iya cin amanar ta ba shi yasa na ƙi yarda da kudirin ka amma bayan doguwar lokaci da na dauka ina tunani sai na gano ba a ranar na fara son ka ba Abdulrahman na daɗe da kaunar ka a raina tun ban san kaina ba amma ban taɓa ganin shi a matsayin so ba na fi dangana hakan da son da nake yi wa zane zanen ka wanda shi ya janyo min so da kaunar ka mai tsanani a rai na ka duba fah sunan kamfanina _'M MOTIVES'_ ka san wannan suna ya samo asali ne ta dalilin ka saboda kai ne ainihin motive ɗin na wa kuma kai ne motivator ɗin na wa shi ya sa na sanar da mahaifi na har ya min bazata ta saka sunan a matsayin sunan kamfanina,sai da na ga an juya min baya ta ko wani bangare sannan na farka daga baccin da nake ti dan i always put others first kafin kai na amma sai ya zama kuma ni ce a receiving end din dan duk halin kirkin da na ke yi bai saka ni na tsira daga kaidin jama'a ba ciki har da na kusa da ni kana gani mutani mafi kusanci a rayuwata aka nemi salwantar da rayuwar su saboda na nuna damuwa ta a kan ka ta ya kake tsammanin da zuwan ka da wannan maganar farat ɗaya zan amince da bukatar ba bayan abubuwan da suka gudana a tsakanin mu ban yi wani tunani ba na furta maka waɗannan kalamai saboda ba a cikin hayyaci na nake ba ni na yi hakan ne dan in gujewa faɗawa a wani halin daga ni har kai ban taɓa tsammanin abin zai zame min damuwa sai da na rasa ka a kusa da ni na tsawon wata guda a sannan na gane cewa son ka da kaunar ka sun yi overshadowing di na ba zan iya daukar rashin ka ba ko na kira ka baya shiga in na tura maka messages ta email baka responding hakan ya daɗa rikitani na rasa yadda zan yi biki ake yi a gidan mu amma hankali na baya tare da ni tun da na ji muryar ka a wayata na rinƙa neman ka ban gan ka ba na koma ciki aka ce min ka zo ka tafi hankali na ya daɗa tashi na ji gidan ya min tsanani da duhu kasa controlling kaina na yi shi yasa na zo nan ɗin ko zan sami sauƙin radaɗin da ke dami na a zuciya ta.. Abdulrahman kana gani bayan duk waɗannan abubuwa zan yarda a hada baki da ni in cutar da kai kai ɗin da ka zame min haske a rayuwata tun ina yarinya ta, kai ɗin da ta dalilin ka na zamo abin da nake preswntly,kai ɗin da na girma da sonka a jinin jiki na, ba zan taɓa cutar da kai ba na san duk halin da kake nuna min ni na janyo shi laifi nane ba ka da laifi ko kaɗan dan ka nuna min rashin yarda da ni ƙarara ba zan yi fushi ba dan son da nake maka yana da girma a zuciya ta kuma ina mutunta ka ina ganin ƙimar ka ta yadda ko ma me ka min bana jin zan iya fushi da kai Abdulrahman dan haka in har bayan waɗannam bayanai da na maka bai gamsar da kai ba kana ji a ran ka kamar ni ba mai son ka tsakani da Allah bane kana iya goge ni a zuciyar ka a kwakwalwar ka a rayuwar ka ma gabadaya Abdulrahman amma ka sani ni ɗin mai son ka ce har abada"!!! Kaiwa nan na juya da sauri dan wani irin kukan rabuwa da shi ne ya taso min ba sauƙi a nashi bangaren kuwa ƙamewa yayi sakamakon jin irin wannan bayanai da na mai bai yi zaton jin haka daga gare ni ba kenan dama na dade ina son shi ne?amma ne yasa ban sanar da shi ba tuntuni?  ashe ina matukar kokarin kare shi ne daga shiga wani tarkon miyagu amma ni nake takura kaina and still abin da ya saka min da shi kenan how could he be so heartless by playing with my feelings har ya nisance ni da shi tsawon wata har guda bai min adalci ba dan haka ya yanke hukuncin comforting ɗi na

🍒🍒SOYAYYA MAI GARƊI🍒🍒Waar verhalen tot leven komen. Ontdek het nu