ZAMANIN MU A YAU 1

503 24 5
                                    

*🫧ZAMANIN MU A YAU🫧*

   NA

JEEDDAH ALIYU
          &
NANA DISO

_____

*001*

  Tsaye yake gaban madubi, agogon dake hannunsa yaƙe cirewa. Alamun buɗewar ƙofa ce tasa shi ƙara gyara tsayuwar sa, idan bai manta ba tsawan minti 30 kenan da ya ƙiranta a waya amma sai yanzu  tazo, wani zazzafan numfashi yaja kana ya fesar, tura ƙofar kai tsaye tayi batare da sallama ko wata magana ba, ƙarar rufewar ƙofar ce tasa shi jiyowa gaba ɗayansa ya zuba mata idanuwanshi, cikakkiyar macce ce wacce ba zata gaza shekara 40 ba fara ce sol amma kuma gajeriya ce, manyan idanuwa ta zuba masa a hankali tace  "Yallabai lafiya naji ƙiranka?" Cikin muryarsa mai amo yace "Banida darajar da zan dawo daga aiki naga matata tana jirana ne? Kokuma banida ƴancin ƙiranki aloƙacin da nakeso?" Taɓe baki tayi gami da galla masa harara ƙasa ƙasa batare da tace komai ba ta samu guri ta zauna cike da gadara take faɗin "yallabai when zaka waye? Yaushe ne? Please free world muke banson taƙura kai ba kada aiki sai tattaɓa mace gaskiya ni ba zan iya ba na gaji, idan kuma yunwa ka ke ji ga abincinka can ƴan aiki suna jera maka aƙan dinning idan wanka za kayi kuma sai na kira ɗaya daga cikin masu aikin ta hada maka ruwa dan ni dai ba baiwar kowa bace ba.
Tafada muryarta na rawa. Manyan idanuwanshi ya zuba mata, tare da wata muguwar harara da ya sakar mata, tsigar jikinsa tana mimmiƙewa, baice mata ƙomai ba ya juya tare da bismillah yana cire shaddar dake jikinsa, jiyo da idanuwanta tayi dan aduniya babu abunda takeso sama da wannan mazantaƙar halittar tasa miƙewa tayi tafara nufarsa, bai ankara yaji ta rungumeshi ta baya.Tsigar jikinsa ce taƙara mimmikewa a hankali ya ambaci sunan ALLAH sannan yace " Maryama inason haihuwa inason naga yarana suna..." " Please stop yallabai nace maka na gama haihuwa yarona shekarar sa 20 yanzu aduniya ya isheni, ko so ka ke yi na zama kaza kamar Babarka? banson..." wata irin zabura yayi ya jiyo, ya ɗaga hannunsa yayi ya sauke a fuskarta. Cikin mamaki ta ɗago idanuwanta da suka cika da hawaye tace "Dan na faɗi gaskiya shine zaka mareni? Bazan kara haihuwa ba na gama haihuwa.
Ta ƙarashe magana tare da samu guri ta zauna tana kuka ahankali.  gaba ɗaya hankalin sa tashi yayi to wai shi wacce iri mace Allah ya basa? Wannan wacce Irin akida ce? Ilimin bokon hauka ne? A hankali ya furta "Ya Allah" manyan idanuwanshi ya sauke akanta sannan yace " Wannan shi ne mugun harafinki na ƙarshe akan mahaifiyata naga wayewar taki tana sakawa kina tunanin mun zama ɗaya? To ki sani har abada gaba nake dake sannan ƙarkashina kike, maganar haihuwa ko kina so ko bakyaso sai kin haihuwa shekaru daya har ashirin ba wasa bane ba na gayamiki, kada ki ɓatamin rai maryama kada kisani cikin wani hali ina ragamiki ne saboda anty da darajarta da nake gani ba wai dan ba zan iya wulaƙantaki ba.
Miƙewa tayi ta kallesa gaba ɗaya illahirin jikinta rawa yake yi yayin da tsigar jikinta ta shiga miƙewa a dalili yadda ta ganshi ta ɗaure towel ga yanayin gashin jikinsa ya mimmike saboda bacin rai, ƙallonsa ta koma yi sannan ta kau da kanta zuciyarta na ayyana mata, she is not that cheap da zata kai kanta gurin namiji. Saukewar ajiyar zuciyarsa yasata yin murmushi tace " Am not going to say it again, Ahmad Shema kasani ni maryama Ado na daɗe da cire mahaifata, nagama haihuwa! Banida ra'ayin haihuwa kamar kaza, idan har.... bata karasa ba ya shige banɗaki yana rufowa da ƙarfi saboda ɓacin ran da yake ciki, sunan Allah ya shiga ambata a cikin ranshi a hankali ya kunna shower ta fara sauka akansa gaba daya ransa ya gama ɓaci, a gaggauce yayi wanka sannan ya fito ya shirya ciķin wani lafiyayyen yadin filtex yunwar da yaji yana ji ne yasa shi fitowa daga ɗakinsa ya nufi palour, mamakin ganin karamar ƙanwarsa Fati yayi tare da ƙaninsa farouk sai matarsa maryama dake waya a gefen kujera da alama da mahaukatan ƙawayenta ne take waya dan yaga yadda taƙe faman babbaka murmushi. "Barka da fitowa Abah". suka faɗa a tare murmushin nan nasa mai sanyayya zuciya yayi musu sannan ya fara taƙawa zuwa dinning  cikin kasalalliyar murya  yace " Maryama zoki zubamin abinci. Ta ɗan  saukar da wayar gefe tace "waya nake yi ka zubawa kanka.
Sannan ta ƙarasa fita daga part din. Wani mugun takaicine ya ziyarci fati, farouk kuwa kasa cewa komai ya yi. Fati da taga alamar yayan nata na ƙoƙarin zubawa tayi saurin miƙewa ta nufi wurin shi tana fad'in "Abah kawo in zuba maka please.  Ƙoƙarin boye damuwarsa yayi kafin ya bata cokalin ta zuba masa, kallon ta yayi yaji sanyi cikin ransa dan shi mutum ne mai son ƴan uwansa, duk da zafi da hali irin na mahaifiyarsu ta basu tarbiyya mai kyau tun daga girmama na gaba dasu da kuma mutuntawa, cikin sanyin murya da sunan da yake kiranta dashi yace "Batoul zuba muku keda farouk" ya faɗa yana fara cin abincin, cikin girmama ta zuba musu har suka gama cin abincin sannan yace  "Meke tafe daku?" Farouk ne yace "Abah zan je makaranta ne dan ALLAH kayi haƙuri in-sha-Allahu zan mai da hankali, na gayawa Alhaji yace tsakaninmu babu ruwansa.  "Batoul ke kuma fa?
"Abu nifa banason aure kuma hajiya ta ɗage sai nayi ni kuma karatu na keso dan ALLAH talk to her.
Murmushi yayi gami da cewa "na ji zaku iya tafiya.

ZAMANIN MU A YAUWhere stories live. Discover now