AUREN WUCIN GADI

由 zahraaliabdullahi5

19.5K 1.7K 78

labarin wani matashi daya auri wata yarinya na wucin gadi saboda wani dalilin sa. 更多

1
2
3
4
5
6
7
8
9
10
11
12
13
14
15
16
17
18
19
20
21
22
23
24
25
26
27
28
29
30
31
32
33
34
35
36
37
38
39
40
41
42
43
44
45
46
47
48
49
50
51
52
53
54
55
56
57
58
59
60
61
62
63
64
65
66
68
67
69
70
71
72
73
74
75
76
77
78
79
80
81
82
83
84
85
87
88
89
90
92
91
94
93
95
96
97
98
99
END

86

250 22 3
由 zahraaliabdullahi5

💕 *AUREN WUCIN GADI* 💕

✨ *GORGEOUS WRITTERS FORUM* ✨

          ✨ *G.W.F* ✨

CHAPTER 86

  Shiru tamasa ta basar dashi fuskanta yana nuna kaman bataji daɗin zuwan nasa ba amma cikin zuciyar ji take kaman taje ta rungumesa dan murna.

Tunda Alhaji mai gidan nan ɗazu da yazo yabita da wani kallo da shu'umin murmushi ta rasa nutsuwarta idan ta tuna yace idan bezo yau ba ze iya kaiwa gobe ko jibi sai taji jinin jikinta yana tsinƙewa gashi dare na karayi.

"Kode ba'ayi farin ciki da zuwan nawa bane na koma inda nafito?saurin ɗagowa tayi tana kallon sa da jin tambaya daya mata kaman tace masa a'a karka tafi ka barni ta riƙe hannun sa tasakar masa kuka ko zeji tausayin ta yafasa tafiya amma saboda jan aji irin ta ɗiya mace mai kamun kai da sanin darajan kanta ta dauke kanta tayi daga barin kallon nasa tana sake tsuke fuska kaman bata ji mai yake cewa ba.

Takowa yayi yashigo cikin takun sa dake nuni shiɗin jarumin namiji ne ya iso gareta bata ankara ba saijin ƙamshin turaren sa daya cika mata hanci tayi kusa gareta ɗagowan da zatayi saura ƙiris yarage ƙirjin su ya haɗu dana juna,ja baya tasoyi cikin zafin nama ya damƙo ƙugunta da duka hannun sa biyu yana dawo da ita kusa dashi yana haɗe ƙirjinsu waje ɗaya.

A fusge ta furta"a'auzu billahi"karki sake mun uziyya yafaɗa cikin yin ƙasa da murya yana ɗalle mata baki da yatsa"auchh ta furta cikin rawar murya idonta na cikowa da hawaye.

"Shiiii yace da ita yana daura yatsan sa saman bakin sa banson kukan gulma idan kukan kike sha'awa yanzu saina sakiyi mai dalili.

"Hajiya nifa ban yarda da yaron nan ba cewar Alhaji bayan fitan Ahmad daga falon"wane yaro kuma Alhaji?Mami ta tamvaya tana gyara zaman ta.

"Ahmad mana bayan shi akwai wani yaron ne"me yasa kace haka?ko yayi ma wani abunne?"beyi ba saide ina tunanin yana shirin yi idan ko hasashena yazama gaskiya wallahi kinde ji narantsa miki zan ajiye duk wata sanayya dake tsakanina da Uban sa in masa rashin mutunci ne.

Ni yaron nan yake neman yaudara  yakomawa aikin sa amma yake yin abu kaman wanda bamusan abunda yakeyi ba,ai duk wani motsin sa akan idon mu yake ko yaɗauka shi kaɗaine wanda ya iya taku,yakare maganan sa yana ta kumfar baki.

"Nifa Alhaji bangane akan me kake wannan kumfar bakin ba ko zakamun dalla dalla ta yanda zan gane ka ganar dani,ta kare fadin hakan cike da zakuwa dan son jin meya fusata shi har haka.

Ruwa mai sanyi ta daukata mika masa ya amsa yasha cikin glass cup sannan ya dire cup din saman center table dake gaban su ya shiga sauke ta gwayen ajiyar zuci yajin jina bayan sa da kushun dayake zaune akai yace wato Hajia ina tunanin yaron nan Ahmad yakoma aikin sa na yaƙi da fasa ƙauri idan ko bincike na ya cimmasa saide Uwar sa ta haifi wani wannan karon bazan bari ya tarwatsa ni kaman yanda yayi galaba akan mu shekarun baya.

"Amma Alhaji kasan Fauza tanason sa kana ganin zaka iya hafa rayuwar ƴarka cikin halin ƙunci kawai dan wani dalili naka ko burina ka?

Da dariya ya fashe kaman ta bosawa saida ya tsagaita da dariyan sannan ya kalli Mami yana cewa"kuɗi maganin wulakanci kuɗi maida tsohu yaro kuɗi masu gidan rana kuɗi mai maida yaro babba idan basu rayuwa sai tagayyara"saboda kuɗi kenan zaka iya rusa farin cikin ƴarka?ta katse shi da tambaya"eh mana to mai aciki shima yabata amsa kansa tsaye.

Ya daura dacewa ko kinsan yanzu haka mahaifin sa yana hannu ana zarginsa da kissa bayan fyaɗe"na shiga uku tafaɗa tana dafe da kirginta yanzu abunda yake faruwa kenan amma baka faɗamun ba tuntuni,takare maganarta tana ta salallami.

Shiko Alhaji na Allah yasamu abunda yake so dan haka ya cigaba daurata yana cewa"hatta da lasisin sa an sauke dan naji kaman anacewa yana amfani da ilimin sa yana safarar hodan iblis"na shiga uku cocaine fa kenan?me yasa badamasi zeyi haka dan Allah"sabida kuɗi mana ya amsa mata a ba abunda mutum ba zeyi ba saboda yasa kuɗi dan shine burin kowani mahaluƙi yatara yabarwa ƴaƴa da jikoki.

Hakade yayi ta ɗaura ta keken ɓera,amma fa duk da haka baji a zuciyar cewan zata hakura da haɗa Ahmad da ɗiyarta Fauza aure ba,wannan burin da ɗeɗɗen burine dake dankare cikin ranta.

****
Da ɗaya hannun yana riƙe da ƙugunta ɗaya kuma yana shafan fuskanta a hankali ya sauƙe babban yatsan sa yana zagaye tattausan lip's ɗinta dashi,lumsh idonta tayi sai hawaye dake sauka saman kyakkyawar fuskanta masu ɗumi yana sauka saman hannun sa.

Lumshe idon sa yayi yana kai bakin sa a hankali kunnen ta lip ɗinsa masu taushi ya gogi fatan kunneta haɗe da numfashin sa mai ɗumi daya sata rintse idonta da karfi"kina bukata na baki ko in karɓa da kaina?tsigan da yayi maganan dashi kaman bashi ba,batasan sanda ta bude idon tarrr ,bata sauke kallon ta ko ina ba sai a saman fuskan sa,kallon cikin idon sa tayi abunda ta gani ɗin yasa tayi sauri tana ɗauke idon ta daga barin kallon sa,sake kai bakin sa yayi saitin kunnenta yasake cewa"yanzu zaki bani ko sai anjima kode ni zankarɓi abata anjima?

Jikin tane ya ɗauki rawa karkarkar ai batasan sanda wani karfine yazo mata ba,bata kuma san sanda ta ture shi tayi gaba da ɗan gudun ta ba,saide ba inda taje ya cabkota yana sake haɗe ta da jikin sa yayi mata kyakkyawan masauki saman faffaɗan kirjinsa ya sake kai bakin sa yayi kunneta ya furta"saurin me kike ai basai ta kaimu ga zuwa can ɗin ba?ai ko anan kika bani zankaɓa,amaryata ta wucin gadi ya kare maganan cikin zolaya.

Kicin kicin din kwatan kanta ta fara yaƙi bata daman haka saima wasu abubuwa da yafara mata wanda taji kaman ƙafafunta baxasu iya ɗaukan ta ba,jin sabon yanayi data sinci kanta ciki shi kansa jinsa yake wani irin kasancewa dukkan su su biyun daga shidin har ita sabin shigane.

"turesa tayi cikin kuka ta xame ta zauna a waje tasaki wani irin marayan kuka tasake,jikinta yana wani irin tsuma,komawa yayi ya zauna saman kugera yana daidaita nutsuwar sa,saida yaji sa ya koma daidai ya bude bakin sa ahankali yana cewa"ashe dama ke matsoraciya ce haka ban sani ba,tsiwa fal cikin ki amma ɗan wannan abun da bekai ya kawo ba,kin wani zube kina ɓarnatarmun da hawayenki masu tsada amma dakin adanasu zasuyi miki amfani zuwa ranan da zan karɓa idan kin bani ko baki bani ba idan na buƙata zan karɓane.

Jin irin maganganu dake fita daga bakin sa,wanda tayi imanin sun girmi tunanin ta dama shekarunta baki ɗaya ai batasan sanda kukan ta yatsaya cak ba,tana murguɗa masa baki ta miƙe ta faɗa ɗakin da gudu tana maida ƙofan tana rufewa harda murza key,murmushin gefen baki yayi yana cewa lalle akwai aiki jaa a gabana gata da tsuwa da tsoro hmmm.

Yana nan zaune sai ga kiran Faisal saida yayi koƙari dan ganin ya daidaita yanayin sa kafin ya ɗauki wayan,yanayin yanda yayi salla kaɗai saida yasa Faisal tutsurewa da dariya yana cewa"me yasamu muryanka?

Saida ya shaƙa sannan  yafesar yana sake kame muryar sa dabata fitowa da kyau yace"idan dama ka kirane dan kamun wannan tambayar ne ka ajiye waya dan ina da abunyi,ya faɗa murya a shaƙe.

Ai Faisal besan sanda yafashe da wani irin dariya ba haryana riƙe cikin sa"ƙwafa Ahmad yayi yana kashe wayan yayi wani dogon tsaki mtssss yanajin haushin kansa daya kasa riƙe kansa kan ƙaramar yarinya karfa ta raina masa hankali gashi yanzu har takai Faisal yanason yimasa sharri.

Yana nan zaune wayan tasoma burarin neman agaji,kaman baze dauka ba ganin mai kiran nasa haka ya daure ya dauka dan yasan kiran dole tana da mahimmanci.

"Idan kasan rashin M zakamun pls Officer ka kashe wayan,abunda yace dashi kenan sanda ya ɗaga kiran"ok ok yace yana danne dariya dake zuwar masa dan yasan muddin yabari yakashe masa wayan karo na biyu ba lallene yakuma samun Ahmad ɗin  yauɗin ba.

Ka zauna cikin shiri karfe biyu dare Alhaji na Allah xe fita kayi kokarin dan gani kabisa a baya"ok kawai yace a takaice hira suka taɓa kaɗan nan yake sanar da Faisal ɗin maganan su Mami dama shi Alhaji na Allah dan ganin Aisha ta koma ɓangaren su ɗakin masu aikin gidan da zama.

Shiru Faisal yayi na minti biyu sai yace"ina ga kabarta ta riƙa zuwa tana tay masu aikin gida da wasu aikace aikace hakan kuma ze taimaka mana wajen samun wani evidence da zamu riƙa sannan kaima inason kayi kokari dan ganin an samu wani abun ta gunka kafin zaman kotu.

"In sha Allah Faisal akai nake ina cikin damuwa sosai wallahi dan nakasa samun nutsuwa cikin zuciya ta,tunda nabaro gida banida nutsuwa zuci data ruhi,yanda yayi maganan akarye saida ya karyama Faisal zuciya kwantar masa da hankali ya shiga yi yana bashi ƙwarin gwiwa saida ya tabbata ya dan rage damuwa sannan sukai sallama yana kashe wayan sa.

"Alhaji an samu matsala,miƙewa tsaye yayi yana kallon wanda yake tsaye a gaban sa yace"idon mikiya kasan bana shiri da kalmar matsala bana kuma son jin sunan ta meyasa kake kiramun ita anan,bayan kasan bani da alaqa ko jituwa da wannan sunan.

Yafaɗa a fusace cike da fushin da yasaka ɓoyeshi  hatta a muryar shi"Allah ya taimaki Oga tun safe yaranmu suna airport ɗin nan amma har yanzu nadake magana dakai sunce basuga koda mai kama da Gazali ba balle akaiga Zulai.

"Kai ina karyane haka sam baze faruba yafaɗa da karaji yanda yayi tsawa har saida idon mikiya yaɗan razara danjin yanda yayi maganan cike da ƙaraji.


ALLAH YASA MUDACE

继续阅读

You'll Also Like

1.7M 101K 40
"You all must have heard that a ray of light is definitely visible in the darkness which takes us towards light. But what if instead of light the dev...
1M 15.3K 38
Ivy Williams had always aspired to complete her university journey without any interruptions or complications. However, not even two months into her...
613K 32.7K 50
𝐒𝐜𝐞𝐧𝐭 𝐎𝐟 𝐋𝐨𝐯𝐞〢𝐁𝐲 𝐥𝐨𝐯𝐞 𝐭𝐡𝐞 𝐬𝐞𝐫𝐢𝐞𝐬 〈𝐛𝐨𝐨𝐤 1〉 𝑶𝒑𝒑𝒐𝒔𝒊𝒕𝒆𝒔 𝒂𝒓𝒆 𝒇𝒂𝒕𝒆𝒅 𝒕𝒐 𝒂𝒕𝒕𝒓𝒂𝒄𝒕 ☆|| 𝑺𝒕𝒆𝒍𝒍𝒂 𝑴�...
1.1M 28.3K 45
When young Diovanna is framed for something she didn't do and is sent off to a "boarding school" she feels abandoned and betrayed. But one thing was...