Fyaɗe aka yi miki. Shi ne abinda zuciyarta ke ƙara nanatawa. Ban san waye ba, ban kuma san dalilinsa na aikata haka a gareni ba, ni a sanina bani da wani abokin hamayya, bani da izgili kuma bana wulaƙanta kowa, to waye ya yi min fyaɗe? Kuma mene dalilinsa na lalata rayuwata a lokacin da zan fara more ƙuruciyata? Ko wace mace ya ce yana so sai ta mutu, dan haka zamu aura masa Sadiya domin daƙile wannan matsalar,ko da ta mutu a sanadin haka to daga nan matsalar ta kau.